002

2K 201 6
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated to: My Habibaty💞Aisha Idris Abdullahi*

*002*

   "Tana cikin karatun azkar din ne Wayarta Dake gefenta ta Dauki Tsuwa ta Dakata ta Dauki Wayar sunan wanda Taga yana Kiranta ne yasa ta Saki Mirmishi Cikin Jin Dadi da wani Farinciki Ta Daga tana Fadin"Qawata.."

Dagachan Bangaren Subai"a tace"Ba wani kawarki Allah Hafsah Daga ke har yaya Abdullahi baku da kirki ace Har yau kwana na goma da Haihuwa ammh Daga ke harshi ba wanda ya Leko..? Haka ake Rayuwa..?Har Anty Zannira Dake kaduna tazo Ita da Mijinta ammh ke ban ganki ba,Ballatana Shi yaya Abdullahin..?

Hafsat ta Saki Mirmishi kafin Tace"Toh uwar korafi kin gama.
? Domin bana so na katse miki Hanzari ne Tunda kika Dauko Wannan Dogon Korafin naki sai kin idashi zakiji Dadi.."Subai"atu tace"Ba wani Sarkin korafi ko Gaskiya.."Hafsah tace"Ai bance ba gaskiya bane ammh sai ki Tsaya ki Saurari nawa uzurin ko.? Kinsan dai Haka kurum Tunda Kika Haihu Banaki Leko ki ba ko...?

Subai"atu Tace"Umh...Ina Sauraranki.."Hafsah tace"Wlh Tunda Kika Haihu nace ma Abban Amira zani Barka ammh baicemin komai ba Har suna yazo,Ranar suna kuma Wlh naso zuwa sai na Tashi bana jin Dadi,ga Amir nata Zazzabi Da Amai Shiyasa kika ga Baki ganni ba Ammh Insha Allahu Cikin Satinan ina Tafe karki Damu kawata.."

Subai"atu tace"Haka dai kikace Don ki Kare kanki da Mijinki bakomai..Sai na ganki.."Hafsah tace"Lah..Baki yarda ba...? Share zencen Subai"atu Tayi kafin tace"Jiya Ammi tazomin Barka Harda Abun arziki ki Tayani Godiya Qawata Allah ya saka da Alheri ya kara Tsawon Rai.."

Hafsah tace"Kajiki da wata mgana..?Don Uwa tama yarta wani abu sai ya zama Abun Godiya.."Subai"atu tace"Hakane kuma..ammh ai Godiya Abu ne mai kyau ko..? Ni ba wannan ba Ina Jiranki Allah kuwa Har Danki yayi Fushi Dake ya kwana Goma Aduniya baki zo kin ganshi ba ballatana Shi Yaya Abdullahin...." Hafsah tace"Kiyi Hakuri Insha Allahu Zamu zo.."

Subai"atu Tace"Toh Allah yasa."Daganan sukayi Sallama kowa ya Ijiye wayarsa Hafsah ta Gyara zama tana Sauke Numfashi Abun yazomata Cikin Ranta na Rashin kyautawarta ga Kawartata Subai"atu wanda kuma Ba Laifin Kowa bane sai na Abdullahi Domin Tunda akayi Haihuwar take mai nacin Tambayar ya barta Taje tama Subai"atu Barka ammh ya ki Kula Mganarta Har Suna yazo,Ranar sunan kuma Har yace ta Shirya ya kaita Ita da yara sai kuma yan Masifarsa suka Tashi Daga kawai Ta bata Lokaci wajen Shiryawa Shikenan yace ya Fasa kaita kuma Bai lamunta ta Fita ba Takaichi kamar ya kasheta,Tana ji Tana gani ya kwashi su Amira Zuwa Gidan Mama suka barta agida saboda Takachi Sai da tasha kuka,Ranta ya baci yasaa bata karamai mganar Zuwa Gidan Subai"an ba ta barshi ai Shima kanwarsa ne In Ya barta Taje Domin kanshi in ya Hanata Shima kanshi yayi mawa Ita miye nata aciki.

Gashi Abunda ke bata mamaki da Abdullahi yana da kyakyawan Mu"amala da kowa banda ita Shiyasa ko zata Shekara Fadin Aibun Abdullahi babu mai yarda,Ko Wajen iyayenta bata Isa ta Kushe Abdullahi ba,baya kwana Biyu baije Tudun wada ya Gaishesu ba,weekend kuwa Shi da yara a Cikin Zaria suke yinshi da Tudun Wada,Shiyasa komai zai mata Take Shanyewa sanin ko Zata Shekara Fada bamai yarda da Ita Saboda in ka Ganshi Bazaka Taba Zaton yana iya Doguwar Mgana ba ballatana Har ya iya wannan Hayagaggar,Abunda ke Daurema Hafsah game da Abdullahi Shine,Komai tayi mai Bata Burgeshi kuma komai tayi ba Daidai bane Duk ko iya Kokarinta na ganin ta zama mai Daidai acikin Idanuwansa ammh Abu ya Gagara Shekara Biyar da Auransu ammh ba wani Abunda ya Chanza Suna nan Jiya yau.

Ajiyar Zuciya ta Sauke jin Sallaman almajirinta yunusa,mikewa tayi ta Fito suka Gaisa,Rijiya ya Nufa ya Fara Zuba mata Ruwa Cikin Babban Roban Dake wajen,Ganin haka yasa ta Bude Kitchen ta Shiga ta Dauko kayan Miya ta Fara gyarawa Ta Tagama sai ta Saka Cikin Wata Robarta mai murfi tana cema Yunusa in ya Gama Zuba Ruwan ya mata Wanke wanke ya Dauki Nikan nan ya mika mata Gidan Nene mai nika yace mata Toh Daganan Ta koma Daki,Tana nan kwance Bayan Fitan Yunusa Zuwa Nika sai ga Nepa sun kawo Wuta ta Mike tana Fadin"Kash Nepa baku kyauta ba sai da yunusa ya tafi kai min nika kana kuka maido Wuta..?

MASIFAFFAN NAMIJI..!On viuen les histories. Descobreix ara