019

1.1K 86 8
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!

_Ina Kike Y'a guda Tamkar da Dubu....Diyar kwarai irin albarka Wato *RAHMA UMMU FAREESA..* Ladingota,Taho wannan Shafin na yau gabadaya mallakin kine Dota..Ke Ta Dambance awajen Janafty Ina Rokon Allah Ya Cigaba da Dafa miki acikin Rayuwarki Har Abada..Son kauna wanda baya karewa D'iyata..._

*019*

'"Cigaba da Charting sukayi Abdullahi na gayamata yadda yayi kewarta,Ita kuma tana Biye mai Tana mai Tabara da sangarta Ganin ta kunnoshi Da yawa yasa ta kashe Datan kawai ta sauka tana Sauke Numfashi.

Subai"atu Dake gefenta ta waigo Tana Kallonta Bayan itama Tagama Waya da Mahmud dinta Dayake suna katifa Daya ne a kasa matar gidan ta Shimfida musu,Makotan su Goggo Habiba ne,Ita kuma Zannira tana Bisa gado Ita da yarinyarta sai Jamila Diyar goggo Habiba da wasu baki Suna Dakin Uwargidan Dayake gidan Uwargida da Amarya ne,sakamakon Chan gidan Goggon Baki sunyi yawa Ba wajen kwana yasa Goggo tace Jamilarta Ta kaisu gidan Alhaji Isa din su kwana makotansu ne ana zaman Mutumci da karrama Juna.

Ganin Kallon Datake mata ne yasa Hafsah tace"Kallon fa..? Nanawa ne..? Subai tace"Ke zan Tambaya naga kingama Chart da Yayanmu kina ta Sauke Numfashi kodai kodai..?Cikin Sauri Hafsah tace"Kodai me..? Subai na Dariya tace"Kodai ana Bukatar Yayan Namu ne..? Wani Duka Hafsah ta Dakama Subai tana Fadin"Kefa yar iska ce. ? Mugun saka idonki yayi yawa kina waya da naki mijin ammh hankalin na wajena ko..? Sai na Fada masa Allah."

Subai na Dariya Tana Fadin"Yo yau naga ikon Allah Ina Laifina gani nayi kuna gama Mgana kin Hau Nurfafashi Dole na maganta.."Tafada tana kashema Hafsah ido Daya,Kafin Hafsah ta Bude Baki tayi mgana Wayarta ta Shiga kara Da Sauri Subai ta Saka Hannu ta Dauki Wayar ganin An Saka *HUBBY*❤️ yasa Tagane Abdullahi ne,Mirmishi ya kwace mata da Dariya tace Tana Kallon Hafsah.."Lalle Su ya Abdullahi manja...Ahe Hubby ne kuma.."Tsaki Hafsah tayi ta Fizge wayar Tana Fadin"Bai kai a kirasa da Hubbyn bane.? Ko me kika maidashi Yar rainin Hankali.."Ta karishe fada Tana Hararanta Dariya ta kama Subai tanayi Har tana kara kwanciya kan Katifar ita kuma Hafsah sai ta Juya mata baya ta Daga Kiran Kafin tayi mgana Taji Abdullahinta ya Saki kakkarfan Ajiyan zuciya Cikin Rudewa tace"Abban Amira me ya Faru..?

Shagwabemata yayi yana Fadin"Umh.Uhm bake bace..! Itama Cikin Tabaran tace mai"Ni kuma.?me nayi..? Ta fada tana wani karya wuya Kamar wata karamar yarinya,Baki kawai Subai ta saki Tana kallonta,Dagachan Bangaran Abdullahi yace"Ina ta Kiranki baki Daga ba...Zuciyata har ta Fara Zafi Hafsatuna.."Karya wuya Hafsah ta sake yi kafin tace"Afuwan Megidana..na dan Fita ne Shiyasa.."Cikin Kaguwa Abdullahi yace"Ina kika je kuma da wannan Daran..? Da sauri Tace"Ba fita nayi ba..Tsakar gida na Fita naje nayo Fitsari Kafin mu kwanta.."Ajiyar Zuciya ya Sauke yana Fadin"Kina ina ne..? Gidan goggo..?

Hafsah tace"A"a muna makotansu inda muka kwana Jiya..Chan ba wajen kwana Don ma yau an ragu wasu sun Bi amarya.."Abdullahi yace"Eh yanzu Muka gama waya da Umma take Fadamin ita da Inna Abu sun raka Amarya Malumfashi.."Hafsah tace"ai kam mu sai gobe zamu je mu ga Daki in Allah ya kaimu.."Yace Allah ya kaimu Plz Hafsatuna ki Dawo Goben Allah gidan yayi min Girma Ina jin kewarki Sosai.."

Hafsah tace"Insha Allahu ko bamu Dawo gobe ba Jibi Tun Safe muna Tafe.."Ba haka yaso ba Dayake Goggo Habiba ne sai yace"Ok Allah ya kaimu ina Yaran nan ne..? Subai da Zannira..?

Hafsah tace"Ga Subai nan Zannira kuma Tana Ciki mu muna Falo ne.."Baki ya Tabe yana Fadin"Sai da safe...Ki kularmin da kanki kinji ko..? Hafsah tace"Insha Allah..kaima haka.."Dagahaka suka yanke Kiran Sai ji kawai Hafsah tayi Subai ta Fado mata tana Fadin"Ke daman Haka ya Abdullahi ya iya Rage murya yana Shagwaba..? Ashe dai ba Masifa kadai ya iya ba.."

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now