020

970 91 4
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!

*020*

"A Ranar su Hajiya Sa"a basu samu Tafiya ba sakamakon Tana Cikin bacin Ran Rashin gayamata Abunda ke Faruwa da lariya batayi ba Shiyasa ko Waya Datace Zata Turo kudi a siyama Jiddan lariyan ta Hana,ta kawo mata Excuse din cewa Ta bari sai ta Dawo har yanzu Jidda Yarinya ce ko waya sau Biyu suka Taba Mgana da ita Lokacin da tazo Tariyan Sabon Gidan Ita Lariyan Abunda yasa bata maida Hankali ba Saboda Tana chan tana kokarin Tattara Dukiyarta waje Daya ta Dawo gida Shiyasa bata maida kai akan Lamarin ba ballatana Har ta Fahimci akwai mtsala.

Sai washegari Ranar Talata Tun wajen karfe 11am na Safe Hajiya Sa"a Ta Biya ta gidan Lariya ta Dauketa acikin bakar Jeep dinta Saboda bazata iya gane gidan ba gaskiya Rabonta da cikin gari Tun Ranar da Usman Direba ya saketa Rabonta da kafarta ta Taka Babban Dodo to tana Yaye Jidda Bayan an maidota ta Bi kawarta suka Tafi Saudiya.

Da suka Shigo anguwar Hajiya Sa"a Taga Chanje Chanje dadama Na Gidajen zamani da kuma Cigaban Rayuwa Tace ma Lariya in ita kadai ce bata iya gane ko"ina,Bata gama mamaki ba sai da Lariya ta nuna mata gidan Tabishi da kallo acikin Ranta tana Fadin am samu Chanji Domin Abdullahi ya gyara gidansu Sosai bama samfarin Ginin Baya bane wannan na zamani ne.

Siririn Gilashin Fuskarta ta zare Tana Bin gidan da kallo Ta Madubin Motarta Cikin mamaki Tace"Lariya gida nan ya Sauyamin Sosai in ni kadai nazo ban iya ganewa.."

Hajiya Lariya tace"Eh gaskiya kam Yaya ai Shekarun fa da yawa ba gidan ba Duka anguwanma an samu Sauyin Yanayi Ballatana ma Gidan gaskiya ko bayan Rasuwar megidan bai Lalace ba Yayannasu ya tsaya akan gidan Sosai.."Kai kawai Sa"a ta kada kafin ta Daidaita parking a kofar Gidansu Abdullahi.

Firfitowa sukayi Lokaci Daya Hajiya sa"a na gyara zaman mayafin kanta Tana sanye ne da wani leshi mai ubansu kyau da Tsada ta Saka mayafi har kanta sai wani takalmi mai Tudu Hannayenta suna sanye da zabban Zinare harda Wuyanta da Awarwaro,Fuskarta kuma tana Sanye da wani medicated Glass dan karami na karin karfin gani ko na gayu ne bansani ba,Sai karamar jakarta mai kama da pos dake rike hannunta wanda wayarta ke Ciki sai key din Motarta makale a Yatsanta na Hagu.

Area din take bi da kallo,ba yalwar Mutane saboda Safe ne ma"aikata Duk sun Tafi aiki Yara na makaranta magidanta kuma sun Fita neman Abun bama iyalai Hajiya sa"a Ba fara bace ammh Tana da kyau daidai misali yar kimanin Shekara 46 aduniya ce kallo Daya zaka mata ka Fahimci ta goge a Duniyanci da kuma Bariki idanuwanta suna Bude ne sosai Daga ganinta tayi Shige Shige Sosai Domin Hancinta yana Dauke da Huji ne,sai bakinta dake Jere da Hakoran Makka Har guda Biyu,ita kanta Hajiya Lariyan Shigar alfarma tayi Sosai in ka gansu zaka Fahinci Yaya da kanwa ne saboda suna Tsantsan kama da juna.

*****

Mama na Cikin Daki Tun da tagama Sallar Walha ta Zauna tana addu'o'inta bata Tashi ba,gidan ba kowa Daga ita sai Jidda sai Auwal dake dakinsa yana Barcin asara Mama tayi Tashin Duniyan nan ya tashi ya Tafi Shago Tunda yau bazashi Makaranta ba ammh yaki Fitowa ko Karyawa bai yi ba Sai kawai ta Fita batunshi Mariya kuma Ta tafi asibiti Tun safe in aka Turata.

Jidda na Tsakar gida tana Wanke wanke yan kwanukan da suka Bata ne da kayan karin safe,Taji sallama kamar Daga saama Da Farko bataji ba sai da Hajiya Lariya ta Daga murya ta kara Maimaita Sallaman,kana Jidda taji ta Dago da kanta Daga saman yar Kujeran Tsakar gidan Data ke kai sai kawai taga taci karo da Lariya Baki ta Bude harda Hanci Tana Bin ta da kallo Cikin kayattacen Mirmishi Hajiya Lariya tace"Jidda..."

Da Sauri Jidda ta mike Tana Fadin"La.! Anty Lariya kice...? Tafada Cikin murna tana Rufe bakinta kafin ta Zura da gudu ta Fada Jikinta Tana murnan ganinta Hajiya Sa"a Dake bayan Lariya Hawaye suka Cika kwarmim Idanuwanta,na ganin Tilon yarta wacce Rabon ta da ita Tun Tana da Shekara Biyu da wani Abu aduniya,Jidda Dake Rumgume da Lariya idanuwanta suka kai kan Hajiya Sa"a Dake baya Tana Binsu da kallon Sha'awa,Da Sauri Jidda ta Saki Hajiya Lariya Ta matsa Gaba Tana kallon Hajiya Sa"a Cikin Bugawar Zuciya,Idanuwanta kamar zasu Fado kasa,Kamar Mommy ta take gani,wacce bata taba ganinta ba sai dai a hoto Lariya ce Taga yadda suke kallon Juna Dukkansu yasa Ta Rike ma Jidda Hannu ta Jata har gaban Hajiya Sa"a Ta Dauki Hannuwansu ta Hada waje Daya Tana Fadin"Jidda kin gane ta..?

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now