03

1.3K 115 21
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*

*003

      *TUSHE...*

"Abdullahi Usman Direba Shine Babban d'a Namiji na Farko agidan Marigayi Alhaji Usman Zaria wanda asalinsa Haifaffan Garin Zaria ne,kuma Tashin Zaria a anguwar Babban Dodo Dake Cikin Birnin Zaria.

Alhaji Usman Direba kafin Rasuwarsa ya kasance Mutum ne mai Dabi"ar Aure Saki ya saki mata Sunfi Biyar Ciki harda mahaifiyar Abdullahi,Wato Hajara wacce ta kasance Haifaffiyar garin Zamfara ce Dake Babba birnin Jahar Gusau,A birnin Tarayyan Nageria,Wanda suka Hadu da ita wajen Wani bikin wani abokinsa Da yajema Biki nan garin Zamfara Shikenan Soyayyar ta Kullu Har takai su ga Aure,Hajara itace Matar Usman ta Farko,Auren Saurayi da Budurwa Sukayi.

Alhaji Usman Direba ne,wanda yake jan Babban Mota ta Kamfanin Dangote,Kuma Alhamdulillah ko acikin Direbobin Alhaji Usman na Dabam ne,Domin kowa Sana"ar ta karbeshi Cikin Lokaci kadan ya Tara Abun Duniya kuma yaje Ya Sauke Farali ne kafin yayi Auran Fari,kuma sai da ya Gina Babban Muhallinsa anan Babban Dodo Dake garin Zaria Lokacin Duka iyayansa Sun kare,Dama su Biyu Mahaifiyarsa ta Haifa Shida kanwarsa Habiba toh Tayi Aure a  Danja Dake Jahar katsina.

Ya samu Lakanin Alhaji Usman Direba ne saboda kwazonsa ga aikinsa kuma yafi Jin Dadi in ka Danganta Sunansa da Usman Direba Fiye da ka Kirasa Usman dinsa kai Tsaye Shiyasa Usman Direba yabisa Duk wanda ya sanshi da wannan lakanin nashi ya sanshi har yabar Gidan Duniya.

Ya auro Hajara Cikin Soyayya da kauna,Aka kuma kawomai Ita Zaria,agidan Daya gida Yan"uwan Hajara da Dangin Hajara Suka Tafi suna ta son barka Suna Fadin Hajara ta Dace,Hajara batayi Zurfi a karatun Bokonta ba iyakarta Jss3 ta Dakata da karatun sai dai Tana da Ilimin Addini Daidai Gwargwardo.

Zamansu ya Fara ne Cikin kwanciyar Hankali da kuma Soyayyah,Har na Tsawon wata Daya da wani abu Komai tace tana so Cikin Rawan jiki yake mata da Tattali sai dai Lamarin ya Sauya ne Lokacin da Hajara Ta Fara Laulayin Ciki kuma sukaje asibiti aka Tabbatar musu Da Tana da Shigar Ciki na Tsawon Sati Uku da wani abu wannan Dalilin Shine Sanadiyar Tabarbarewar zamansu wanda har yakaisu ga Rabuwa da Juna na Har Abada.

Hajara tayi mamakin Sanda Usman Direba ya nuna bayason Cikin Jikinta atakaice dai bai Shirya Haihuwa yanzu ba,ya Tada Bala"in sai an Zubar da Cikin nan ita kuma Hajara tace bai isa ba yayi Bala"in yayi barazanar Duk abanza Hajara tace bamai Zubar mata Cikinta,ganin haka sai ya Chanza Salo ya Daina sakarmata Fuska ba kalma mai Dadi,sai Harara da Habaice Habaice da Mganganu marasa Dadi,Daga karshe sai ya Fara mata Horon Yunwa Duk Hajara ta lalace ta Rame ga laulayin Ciki ga kuma Horo da yunwa Wajen miji kuma ba wani Saussauci Ballatana jin Dadin Dalilin Haka Rana tsaka Hajara ta Gudu ta koma Garinsu Wajen iyayenta ta kuma Fadamusu Duk Halin da akeciki Iyayenta kuma suka ce tayi zamanta agida kuma ciki Insha Allahu sai ta Haifeshi.

Wannan tafiyar ta Hajara itace Tafiyar ta Har Abada Daga Gidan Usman Direba Domin bata Dawo ba Sai dai Taga sakon Takardan Saki,Domin Tunda tatafi bai Bita ba kuma iyayenta suka ce bazata koma ba sai yazo har garin,shi kuma yaki Zuwa kanwarsa Habiba Taje har gidansu Hajara tana Rokon iyayenta da su barta ta Dawo ammh sukace Sai Usman yazo,Dole ta koma ba jin Dadi Domin Usman yamata Rantsuwa bazai je ba,Domin ma Ta gane Hajara bata gabanshi sai kawai ya Shiga neman Aure Wata Biyu da Tafiyar Hajara yayi Sabuwar Amarya mai Suna Sahura Ita yar zaria ce,Ranar kuma da aka Dauramai Aure ya Turama Hajara Sakinta Uku ta Cikin Akwatin Sirrin Wayarta Ranar tayi kuka kamar Ranta zai Fita ta kuma yi Nadamar wannan Auren na Usman wanda bai da wani Amfani iyayenta su suka Karfafamata Gwiwa suka kuma ce Tana Haihuwan Cikin Usman Bayan ta yayeshi Zasu maidashi Gidan Ubanshi Domin Itace Tasu bashi ba.

Kusan Abunda ya Faru da Hajara ne ya Faru da Sahura itama Auren ba Dadewa sai ga Ciki nan fa ya Tada Bala"i sai an Zubar tace bai isa ba Itama dai Bata Zauna ba ya Saketa ya Tura ta Gida da Ciki,Ba Dadewa kuma ya Sake Auran Wata Bazawara Karimatu sakin Wawa toh itace ma Tayi karfo Domin Daman Tunkafin ta Shigo Gidan ta samu Labarin Irin Halinsa sai ta Shigo da Shirinta na zama Dashi Domin bazata so ya saketa ba Tunda gaskiya Usman yana Kokarin kyautata iyalansa Shi matsalanshi Daya Rashin Son Haihuwa.

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now