011

1.1K 112 7
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Janafty*❤️

*Dedicated To:My Habibaty💞Aisha Idris Abdullahi..*

_*Na Sadaukar da wannan Shafin kachokan zuwa gareki FAUZIYA S MADAKI..❤️,Janafty na Matukar Godiya da karamcinki gareni..Nagode kwarai Allah ya bar zumunci*_

*011*

 

"Washegari ma Haka ya tashi Ba Fara"a sosai Tunda Hafsah Taga haka sai ta kama kanta sanin in ya tashi da irin wannan yanayin Ita yake saukemawa aikuwa Duk Kafa kafanta sai da ta samu nata Rabon.

Jakar yaran na makaranta ya Duba yaga an basu Homework kuma ba"ayi musu ba nan fa ya fara ma Hafsah Fadan Tana da Careless kan ya"yanta Tunda har za"a basu aikin gida Tun Ranar jumma"a ammh tana gayamai bata san am basu yi ba Shuru kawai tayi mai saboda tasan ko tayi mgana bazai saurareta ba ammh laifin na Amira ne domin ita tace an basu Homework Ranar jumma"a Da suka Dawo Daga makaranta sai tace taja Amir ta koya mai suyi Homework Din tare,Tunda Gobe zasu tafi gidan Mama ba Lokaci ashe Amira bata Kama ma Amir din sunyi ba,gashi yanzu Fada ya koma kanta.

Haka ya fice Ranshi bace ko Cikakken kari bai yi ba,Kuma ranar bai Dawo Gidan da Wuri ba sai Dare Nan ne ma yake Fadamata Daga Tudun wada yake Ammi da Daddy na gaisheta sai Lokacin Taga sakin Fuskarsa.

Ranar sati ta zagayo Ranar asabar da kanshi ya kaisu Amira Chan Makarantarsu Ta hadda Daganan kuma ya Biya Gidan mama bai Dawo ba sai pass 12 bai jima da Shigowa ba sai ga Nazifi yazo Daukansa,Dama ko da yazo yana wanka ne,Yana Fitowa ya Shirya a gurguje,ya saka Kaya yace Hafsah ta bashi wasu Takardu Daya bata ajiya ta Dauko ta bashi suka Fice bashi ya Dawo Gidan ba sai wajen karfe Goman Dare agajiye ya Dawo wanka kawai yayi yaci abinci Hafsah tamai Tausa barci ya kwasheshi bai mata bayani ba sai da Safe Lokacin suna karyawa.

Ashe Fitar da sukayi Jiya Filinsa na Gaskiya ya saida wanda suka Siya Tare da Nazifi Kusa da kusa sai shi ya saida nashi Ya cika da kudin Hannunshi ya Siya wani Babban Fili a GRA,shine basu Dawo ba sai Dare sai da akayi Cike ciken Takardu da kuma sallaman Dilallai.

Hafsah ta kallesa tana Fadin"Meyaasa ka saida wanda kuka siya da abokinka Abban Amira..? Yana kurban Tea din Dake Hannunsa yace"Saboda na Gra din yafi Girma Sosai zai isheni na gina 3Flat harda Wadatar Filin Ijiye mota ina so in Allah ya yarda bayan na gama Ginin Gidan mun koma sai na Siya mota ko..? Wanchan kuma bai da Girma Sosai da kadan yafi wanda muke Cikin nan fa.."Kai Hafsah ta gyada kafin tace"Da wannan dan wannan kuma..Allah ya sa albarka Allah kuma yabada ikon Ginawa.."Ya amsa mata da Ameen nan suka cigaba da karyawan Jefi jefi suna Taba Hira.

Bayan yayi wanka Taga bai da Shirin Fita ta kallesa yana Zaune gefen gado yana latsa wayarsa tace"Yau Nazifin ba zai biyo maka ku fitan bane..? Bai Dago ba yace"Ai tun jiya ya koma Kaduna...Sakina ta je mai weekend.."Yar Dariya Hafsah tayi kafin tace"a"a lalle Dole kuwa bazaka ganshi ba kila sai Wani Weekend din."Tabe baki Abdullahi yayi kafin yace"Allah sa tayi mai zuwan ko na marmarina ne,Jiya muna Wajen Siyan Filin nan na Gra ta Kirashi tace ta tadawo bata ganshi ba,Shine bama mu gama Dashi ba nace ya tafi kawai ma karisa awaya kawai.."Hafsah tace"Ka kyauta.."Daga haka ta Dinke bakinta Shima gogan bai ce mata komai ba sanin Halinsa yasa ta Tura Kofar Tailet ta Shige Tana so ta wankeshi kafin ta Fara aikin waje.

Ranar litina kuma Yana office Mijin Zanniratu ya kirashi yana Shaidamai Haihuwan zannira ammh aiki aka mata Tana asibiti an ciro mata yarta mace,Barka Abdulllahi yayi da kuma Sakon sannu ga ita Zannira suna gama waya ya Kira Mama yana Fadamata tace itama yanzu Suka gama waya da mijin Zannira din nan Mama tace yakamata ko Mariya atura taje ta zauna da ita kafin adawo da ita gida Tunda Jidda na makaranta,tana Shekarar Karshe a sakandiri ita kuma Mariya Karatu suke basu da Test shiyasa.

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now