FINALE

1.7K 103 16
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!

~Alhamdulillah...Dukkan Godiyata Ta Tabbata ga ALLAH shugaban Halittun Duniya...Salati Tare da Rahma Gafara Aminci Su Tabbata ga Annabin Rahma Annabi Muhammad Sallalahu alaihi wasallam Shida Iyalansa da Sahabansa gabadaya..~

*041*

Tunda Barkat ta Dawo Gidan bata kara yarda Tayi zaman Dakin data saba abaya ba,Tun Safe Zata Fito Bayan ta Gyara Dakunanta,Tafito tace Tana so Ta karbi Wani aikin ta Taya Hafsah ita kuma Hafsah sai taki Bata Daman Tun Dawowarta Tace mata Sai ta Haihu ta gama Jegonta kana zata bata Girki ammh Kwanan Miji yana nan ayadda yake in ya kwana Biyu Dakin Hafsah,Sai ya koma Dakin Barkat din ya kwana Biyu,Bai saka musu baki ba sai da Hafsah Ta nemi Daya koma kwana Dakin Barkat da kwana Gabadaya Saboda Tsohon Cikinta gashi kuma Haihuwan Fari kada wani Abu ya taso ba kowa a kusa Da ita.

Lokacin da Hafsah ke Fadamai Haka yana Zaune a kasan Cafet Dinta ne ya Tankwashe kafa yana Cin Tuwon Semo miyar kubewa Bushashiya wacce Hafsah Ta Dafamai Da Daddare,Ita kuma Tana Gefensa Zaune Rike da Noor tana bata Nono Amir da Amira kuma Suna Dakin Barkat tun Dazu Chan ma Sukayi Sallar mangariba Yanzu Chan suke zama Tunda Taja yaran ajiki Sosai.

Yana kai Lomar Tuwo bakinsa yana kallon Hafsah a karkace Gefe Daya na Cikin Zuciyarta Najin Haushin Shisshigin Hafsah na Wani Lokacin..Ina Ruwanta..? Waya aiketa Shiga Hurumin da ba nata ba bai gama mamaki ba ta katseshi da Fadin"Har ma Dazu nake ma Barkat din Zencen tadai Nuna min ba komai ammh ai nima Mace ne nasan Yanayin,kaga kuma Haihuwar Fari ce Gwara asamu wani kusa da ita Tunda bamu san Wani Yanayi Haihuwan zata zo Dashi ba Gashi kuma kai ba barinta Zakayi ta koma Gidan Gaban Hajiyarsu ta Haihu ba ko Zaka barta ne..?

Ta fada Tana kallonsa Mamaki ya kara kamashi bai samu Zarafin mgana ba sai da ya Koshi da Tuwon kana ya Ture Kololin gabansa yaja Roban Wanke Hannun Dake gabansa ya Wanke Tas ya saka Tissue ya Goge Bakinsa Tsaf kana yayi Gyatsa Lokaci Daya da Hamdala yana Fadin"Alhamdulillah..."

Yafada Lokaci Daya yana Mike kafa,Kansa ya jinginar kan Hannun Kujera Lokaci Daya yana Balle Botorin Rigan Shaddan Dake Jikinsa Dama Yana Shigowa da yunwa ya Dawo Abincin ya Fara ci kafin Wanka, Hafsah Ta Karkace kai Tana Fadin"Baka ce komai ba Abban Amira..Ina ta mgana..?

Waigowa yayi yana kallonta kafin yace"Na"am kika ce me..? Ban ji bane..! Ya fada yana Zabga Hamma Galala Hafsah Tayi Tana kallonsa Kafin tace"Kai Abban Amira yanzu Duk mganganun da nagama yi baka Jini ba..? Kai ya gyada mata yana Fadin"Ban ji ba sake maimaitawa.."Baki Hafsah kawai Ta Gimtse Ta Cigaba da Noor Nono ammh ta bata Ranta Sai Abun ya bamaa Abdullahi Dariya,Ganin yadda Hafsah Tasha kunu sai ya Matso Kusa da ita yana Fadin"Meye kuma na Fushi Hafsatun Abdullahi..? Uhmm gayamin yanzu ina Sauraranki kisan Dazu Ina cin Abinci Kuma kinga ba kyau ma kana Cin Abinci kana mgana..! Yafada yana Sosa Sajensa Cikin Dariyan Dayake ta Dannewa

Jin Haka yasa ta waigo ta kalleshi Tana Koramai Jawabin Da tayi mai Tun Farko,sai da takai aya kana ya Dage mata Gira yana Fadin"Duk wannan aikin waya saka ki ko waya aike ki..? Hafsah tace"Bangane waya aike ni ba Abban Amira gani nayi Hakan ne ya Dace kada ace mun kyaleta ita kadai.."Karamin Tsaki Yaja yana Fadin"Ace mana..Waya Damu..? wanda yaga an kyaleta yazo ya Taimaketa mana..ke banda ma Tsabar Saka ma kai Wahala da kuma aikata abu ba"a saka ka ba Ni kin yi mgana Dani nace Miki Eh na yarda..? Bafa ki min mgana ba ammh Har kinje kin ma  Barkat mgana,ai Tunda kinyi gaban Kanki kin kyauta ammh Nidai bada yawuna ba ban kuma amince ba..Raban kwana ne da kukayi zan Dinga kwana Bibbiyu dakin kowaccenku kamar yadda kuka Tsara Mganar kuma Wani Abu ya Faru Allah ke Tsarewa kuma ga waya Cikinmu Duk wanda ta Kira zai kai mata agaji,Bana son Mganar da bazata yuyu ba..!

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now