039

1.5K 104 36
                                    

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!

_Wannan Shafin naki ne *MMAN SADIQ...* Ina jin Dadin yadda kike karanta wannan Labarin da Dukkan Zuciyarki...Nagode kwarai Allahu ya bar zumunci Ameen.._

*039*

"Barkat da kafarta ta taka Har bakin Titi,Bata samu Abun hawa ba sai da tazo Wajen makarantar Albani kana ta samu mashin din Daya Dauketa Zuwa Gida Har Ya sauketa Kofar Gidansu ta sauka ta Biyashi Kudinshi Kuka take,kuka mai Cin Rai da Tsanar Hafsah acikin Ranta Domin Tagama bama kanta yakinin itace Silan Faruwar komai.

Koda ta Zo Shiga Gidansu Kofar tana Kulle alama da har sun kwanta Bugawa tahau yi ammh ba Motsin kowa ganin karta tara Mutane yasa ta Fiddo Wayarta Cikin karamar Jakarta ta Kira Bahijjat,tunda ita Tana Gida Bahijjat ta Fara Barci Wayar Barkat ta tasheta Lokacin Da Taga Kiran Ta Tsorata sai da ta Duba agogo Wajen 10pm da wani Abu na Dare Cikin Tsoro ta Daga Kiran Tunkafin ma Tayi mgana Barkat din Cikin kuka Tace tazo ta Bude mata kofar gida Lokaci Daya tana katse Kiran

Hankalin Bahijjat ya Tashi Da Farko kamar ta Fara Shiga Dakin Hajiya ta Tadota sai Taga Ba amfani Tunda batama Jira Taga mai Barkat din tazo Dashi ba ammh acikin Jikinta Tana Ji ba lafiya Sai kawai ta Zari mayafi ta Bude Kofa ta Fice Zuwa Waje ta Zare Sakatan Kofar Tana Bin Barkat da kallo Wacce ta Shigo Dauke da akwatunta Cikin mamaki da Rudani Bahijjat ta Bita da kallo Bata samu Zarafin mgana ba Barkat ta Fada Cikin Falonsu ita kuma sai tayi Saurin maida Gidan ta Kulle ta Bi Barkat din da Gudu Zuwa Falo.

Tana Shiga,sai ta iske Barkat din Jikin Hajiyarsu Tana kuka ashe Hajiya Taji Fitanta zuwa Waje sai ta Fito Taji ko lafiya kafin ma Takai ga Fitowa sai ga Barkat din ta Shigo Da Akwati Tana ja kee tana kuka ganin Hajiya yasa Rauninta ya karu ta Fada Jikinta Tana kuka Hajiyar ta Riketa tana Lallashinta Da Tambayanta Ko lafiya ammh Taki Mgana Bahijjat ta kallo Wacce ta kariso Kusa dasu Tana Fadin"Bahijjat Tare da Megidanta Take ne ko yaya..?

Bahijjat ta saki Numfashi Tana Fadin"a"a Hajiya ita kadai ce.."Cikin Tashin Hankali Hajiya Amina taja ta kan Kujera suka Zauna Lokaci Daya Tana Fadin"Bani Ruwa tasha Sai ta samu Natsuwan yima Bayanin mai ya Faru.."Da gudu Bahijjat ta Runtuma Kitchen ta Dauko Ruwa mai Sanyi ta samu Wani karamin Kofi ta Tsiyaya ta kawo ma Hajiyar ita kuma ta kafa ma Barkat din Abaki Tana Fadin"Sha Ruwa Baraka zaki samu Natsuwa.."

Batayi musu ta karba tasha Da yawa kana ta mikama Hajiya Kofin Tana Sauke wasu Tagwayen Numfashi Lokaci kuma Natsuwarta na Dawowa Jikinta Cikin Sigar Lallashi da Rudani Hajiya Amina ta kalli Barkat tana Fadin"Baraka meya Faru Dake ne..?Ina megidanki Da kika Fito Daga Dakin Mijinki da wannan Daran..? Ina Fatan Allah yasa lafiya..?

Tafada tana kallonta Jin Haka yasa Barkat ta Barke da kuka Tana Fadin"Hajiya ta shiga Tsakanina da Abdullahi..Tun Zuwana Gidan bata barni na Huta ba komai nayi ma Mijina bana Burgeshi Aduk kalamansa Sunanta ne, akomai nashi Itace kan Gaba Hajiya Shin Nima ba matarsa bace kamar yadda take matarsa ba..? Cewa fa yake Tafini iya komai tafini Biyayyah da Ladabi Hajiya ta Rabamu.."Ta karishe Fada Tana Fadawa jikin Hajiyan Tana sakin Wani Marayan kuka Daga Hajiya Amina Har Bahijjat Dake Tsaye Abun ya Dakesu Cikin Tashin Hankali Hajiya ta Dago ta Tana Fadin"Kinga Bar wannan kukan yi min bayani..? Abdullahin Sakin ki yayi..?

Tafada Cikin Zullumi Girgiza mata kai Tayi kafin ta Dora da Basu Labarin Abunda ya Faru Ta kara Harda karya da gaskiya Ta karishe da Fadin"Wlh Hajiya ita ta Hadamu..Duk Abunda ya Faru itace sila.."Shuru Hajiya Amina Tayi tana wani Nazari Bahijjat kuwa wata Ashar ta lailayoma Hafsah Tana Fadin"Lalle ma Matar nan Shegiya ce..Ahaka kamar ta Allah ashe bata da mutumci bansani ba..! Wlh ban so ki Fito Daga Gidan nan baki Nuna mata ke Haifaffiyar Tudun wada bace ita awa..? Banza a banza da ita.."

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now