chapter 39

232 37 5
                                    

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)
🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤
👩🏻KAMA DA WANE......
BATA WANE👩🏻‍🦱
💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

*Na*
*UMMU NAJMA*
marubuciyar *HAR ABADA*

*DEDICATED TO*
*AMMYN KHAIRAT(golden girl)*
*AND RUKAYYA IKRA(ummu sultan)*

Special gift to *Fenarh matar Soja*
*And Muhammad Karim* Allah ya baka lafiya yasa kaffara ce🙏🏼

39👯
" meyasa zakayi surrendering Bayan na fada maka Zan Nemo wata hanya da zamu warware matsalolin mu me yasa kake dada maida abubuwa masu wahala a gareni? bani so in Gaza brother"

Murmushin takaici Idris yayi Yana dada riqe qarfen cell din yace "Dole nabi umarnin mahaifiya ta, bani son sake maimaita wani kuskuren Tasha wahala a baya bazan so sake saka Mata wani ciwon saboda baqin ciki na ba"

" Babu wani abin da zai faru da Kai ko da ita zansan Yanda zanyi na fitar da Kai daga wurin Nan, for now ka rufe bakin ma duk Yanda za'ayi da Kai kada ka kuskura kace komai zanje KD zuwa yamma insha Allah Zan dawo mu fitar dakai daga Nan gurin"

Girgiza Kai Idris yayi kanshi a qasa kunyar Sa'ood sosai ya Kama shi, shi yayi sharri ma twin brothern shi ya cutar dashi Amman yau da ya Shiga irin wannan halin gashi ya tsaya Masa Yana son fitar dashi,

"Brother ka koma gida ka kula da mama da Haleesa kawai iyalina nasan ba zasu wulaqanta ba inhar Sa'eed Yana raye, ka barni na amshi hukuncin laifi na ko zuciyar mahaifiyata zaiyi sanyi ta daina fushi dani"

Rai a bace Sa'ood ya daka mishi tsawa "shut up!! Ba Kai zaka fada min abinda zanyi ba, Kai Mai laifi ne kuma dan nabi Bayan ka bawai hakan na nufin baka qona min zuciya bane, you broke my trust Idris I will save you for the sake of mamanmu, Nabila and our whole family don't try anything stupid na sake jaddada maka ka rufe bakin ka har naje na dawo"

**********
2:02pm

Hannunta ta saka ta share hawayen dake gangaro mata tana sheshsheqar kuka tace, "Yaya Sa'ood kana ganin zamu samu mafita ta hakan kuwa? Wallahi a tsorace nake"

" Ki kwantar da hankalin ki insha Allah mijinki zai fito cikin aminci nayi magana da Sa'eed shima ya amince zai taimaka Mana kuyi ta addu'a kawai yanzu haha mun kusa Isa wurin da zamuje a qarasa komai na Miki alqawarin Idris ba zai kwana a cell ba so cool down your mind please"

Kukan da take ta faman dannewa ne ya kubce Mata ta fara rerashi cikin qunar zuciya, " bansan me zance Muku ba Amman Ina roqon ku Dan Allah kuyi haquri domin Bayan hakan ya faru ya sanar dani, saidai ban sanar Muku bane saboda Ina tsoron abinda zai Sami miji na a tunani na shi kadai ne gata na but you proved me wrong Yaya Sa'ood, komai soyayyar ka da kusancin ka da mutum idan yayi ba dai_dai ba ka nuna mishi Kuma kada ka goyi Bayan shi, na gode ya Sa'ood ubangiji Allah ya biya maka buqatun ka na duniya da lahira ya saka maka da mafificin alkhairi Allah ya tsare maka rayuwar ka da dukiyar ka ya Sanya ka kasance cikin farinciki na HAR ABADA"

Da "ameen" ya amsa Mata Yana Mai Jin dadin addu'ar ta, sukayi sallama sannan ta katse Kiran ta koma parlo tana qoqarin dai_daita nutsuwar ta, da Sarwa da sauran matan gidan har da iyaye an taru anyi jingum_jingum,

Tana fitowa Haleesa ta qaraso da sauri ta rungume ta saboda ita shigowar ta Kenan Bata San me ake ciki ba, don tunda ta Gama zuba rashin kunyar ta da safe ta Shiga daki ta rufe kanta sai yanzu ta fito,

KAMA DA WANE....(Completed)Where stories live. Discover now