Yafada yana Daure Fuska Kwabe Fuska Hafsah Tayi Tana Fadin"Haba Abban Amira...b..."Bana son Wani mgana Don Allah ina Ruwanki wai da ita..? Malama kiji da kanki kawai Mganar kuma ko zata koma Gida ne,ta Haihu ki Tambayeta indai tana son komawa Fine ni bani da Matsala...'Yafada yana Mikewa Cikin Mika Hafsah ta Bishi da kallo Ta kasa mgana kafin ta kada kai tace"Shikenan Tunda Haka kace...Ammh Ban ji Dadin yadda kamin Wannan Fahimtar ba.."

Shima kai Tsaye yace"Nima ban jin Dadin yadda kike yanke min Hukuncin batare da Sanina ba..Ki Tsaya iya matsayinki kawai malama mganar kuma Taya kwana nidai ga Abunda nace in kinga Zaki iya Taimakawa malama Hafsah sai Duk Ranar girkin ki ki Rika Tafiya Dakin Barkat kina Tayata kwana Fakat.."Da mamaki Hafsah Tace"Kai kuma fa..?

Yana Mirmishin Mugunta yace"Ina Inda ya Dace mana...Domin ba inda zani ki Tafi Dakin Wata Taya kishiya kwana Ki kwana Cikin Tsinuwan mala'iku Domin nidai bada yawuna aka Tafi ba Atoh.."Daga haka ya Shige Cikin Bedroom din yana ta Fada da kallo Hafsah ta Bishi kafin ta kadai kai ta Mike Tana Rike da Noor wacce tayi Barci Ciki ta Shiga Itama ta Shimfidar da Noor Daidai Lokacin da Abdullahi ya Leko Daga Ban Daki yana Fadin"Ina Ruwan zafin... ?ko baki saka bane naga Kittle din bakomai..!

Ko kallonsa Hafsah batayi ba Cikin Kufuluwa tace"Zan saka kenan suka Dauke Wuta...Sai dai in na Dafa maka a Gas.."Tafada tana kokarin Ficewa Daga Dakin,baki ya Rike yana Fadin"me yayi zafi..? Barshi zan yi da Ruwan sanyi ni ba bakon zafi bane..Ammh fa Dole akamin ba Daidai ba Zan Fada.."Yafada yana Komawa Cikin Toilet Din Lokaci Daya da Rufo Kofa Hafsah najinsa ta Fice tamai Banza Sanin Halinsa Tunda ya kuma Turtse Shikenan kuma.

Dakin Barkat ta Shiga ta iske Amir yayi Barci Amira ce Kadai Batayi ba Suna ta Hira da Barkat wacce Take zaune ga Katon Cikinta wanda yayi kasa alamun Haihuwa ko yau ko gobe,Sannu Hafsah Tayi mata kana ta kama Amir takai shi yayi Fitsari takai Daki ta kwanta kana ta Dawo tace Amira taje ta kwanta sai da Amiran ta Fita kana Hafsah tayi ma Barkat Zencen yadda sukayi da Abdullahi Mirmishi kawai Tayi kafin tace"Dama fa naji ki ne kawai Anty Hafsah..Bakomai kamar yadda yace ga waya In naji wani Abu zan Kira Insha Allahu.."

Hafsah dai Duk Taji kunya Ta Dade Dakin Barkat din Har wajen karfe goma kana ta mata sai da safe ta Fice zuwa Dakinta,Sai da ta kulle kofarta ta kashe Duka Wutan Dakunan ta leka Dakin Su Amira ta gyara musu kwanciya tayi musu addu"a kana ta Shiga Bedroom dinsu ta iske Abdullahi har yayi Barcinsa bai Jira ta ba Bata damu ba Tunda Itama Taji Haushin yadda ya Nuna mata iyakarta Ta Fada Tiolet tana Jin Takaichin Abun Har Cikin Ranta.

Shi kuwa Bangaran Abdullahi ya Yi ma Hafsah Hakane Domin ta Kiyayeshi,In yana kyaleta gaba Sai Ta Rika bashi ma Umarni yana Bi,wani Lokacin Wajen Tsausayinta Cutar dashi Take bata sani ba,Shiyasa ya Taka mata Burki Tun yanzu kafin abun yayi gaba kuma ya kasa Controlling din Abun.

Washegari Haka Hafsah tatashi Tana wannan Fushin Abdullahi kuwa bai bi ma ta kanta ba ya nuna mata ma bai san Tanayi ba Dole ta Tattara Fushinta ta watsar ta saki ammh Duk da Haka bata Dandara ba Ranar da Daddare bayan ya Daawo ta kara Zuwar mai da mganar Yayi ma Hajiyarsu Barkat mgana Ko Kanwarta Data Dawo Gida Aina Aba Barkat din ta zauna mata kafin ta Haihu Tunda ta Dawo Gida Ta gama Candy,Abun sai ya koma Bashi Dariya da Tsausayi da wani kaunar Hafsah Acikin Ranshi Yana Tunanin samun Mata masu irin Zuciyanta ba, sai an Tona bai mata gardama ba,Yace zuwa gobe zai je gidan yayi mgana da Hajiyan Amina Hafsah Taji Dadi Sosai Tayi tamai Godiya Shi kuma ya Fanshe da cewa Sai ta Bashi Tukwaici,hakanan ta Saki Jiki ta bashi Abunda yafi so aduk Duniya ya kwana yana Moran Abunsa.

Washegari bayan ya tashi Daga Wajen aiki ya Nufi Gidansu Barkat ya samu Hajiya Amina ya Roketa alfarman da basu aron Aina Saboda ta Rika Taimaka ma Barkat din,Hajiya Batayi Gardama ba ta amince Daman Barkat din na Ranta Bai baro Gidan ba sai da Aina ta Hada kayanta ya Daukota suka Taho Tare sai dai Barkat ta gansu kwatsam Tayi ta Murna tana ma Abdullahi Godiya yace ta Godema Hafsah Domin ita ta kawo Shawaran ya Dauko mata Aina Din Lokacin Daya Fada mata Haka taji wani iri Ammh sai ta Danne Bata nuna ba tabi Hafsah Har Daki Tayi mata Godiya ita kuma Sai ta nuna bata ji Dadin yadda Abdullahi ya Fadama Barkat din komai ba,Har sai da ta gayamai Cikin Gatse yace"Toh karya zan yi..? Ke fa kika Kawo Shawaran kuma nayi aiki da ita Banga wani Abun mgana ba Mata dai bakwa Raina Abun Tsegumi..! Jin yace Haka yasa ta kama bakinta ammh ta sani Har ga Allah ba macen da zata ji Dadin Irin Abunda Abdullahi yayi ace Mijinka bai da Tunanin Dauko wacce zata taimaka maka sai Kishiya ta Bada Shawara hakan bai Dace ba ammh Dayake Abdullahi Audu ne Dole ta kama Bakinta ita kanta Barkat bata isa ba Domin Yanzu lallabashi Take bata Fatan Abunda ya Faru da ita ya kara Faruwa akan wata ma bama ita ba.

MASIFAFFAN NAMIJI..!Where stories live. Discover now