BA KYAU BA ✔️

נכתב על ידי sakieyy

95K 9.6K 234

*** Dariya ya saki a wurin, dariya yake yi had'e da goge kumatun shi kamar tab'abbe, wai shine yau yake kuka... עוד

Chapater one
Chapter two
Chapter Three
Chapter four
Chapter five
Chapter six
Chapter seven
Chapter eight
Chapter nine
Chapter ten
Chapter eleven
Chapter twelve
Chapter thirteen
Chapter fourteen
Chapter fifteen
Chapter sixteen
Chapter seventeen
Chapter eighteen
Chapter nineteen
Chapter twenty
Chapter twenty-one
Chapter twenty-two
Chapter twenty-three
Chapter twenty-four
Chapter twenty-five
Chapter twenty-six
Chapter twenty-seven
Chapter twenty-eight
Chapter twenty-nine
Chapter thirty
Chapter thirty-one
Chapter thirty-two
Chapter thirty-three
Chapter thirty-four
Chapter thirty-five
Chapter thirty-six
Chapter thirty-seven
Chapter thirty-eight
Chapter thirty-nine
Chapter forty
Chapter forty-one
Chapter forty-two
Chapter forty-three
Chapter forty-four
Chapter forty-five
Chapter forty-six
Chapter forty-seven
Chapter forty-eight
Chapter forty-nine
Chapter fifty
Chapter fifty-two
Chapter fifty-three
Final chapter

Chapter fifty-one

1.6K 209 9
נכתב על ידי sakieyy

Kangon ya cika mak'il da hayak'in shaye shaye, y'an daban suna can a zaune sun saka kayan maye a gaba suna ta d'urawa a cikin, gaba d'ayan su basa cikin hankalin su,,

Samira kuwa har ta gaji da kuka, tayi shiru a wurin, ba abunda take in ba addu'a ba da yin hadda qur'anin ta, jira kawai take suzo suyi mata abunda suke ga dama, ta rugada ta rugumi k'addararta, abu d'aya kawai take dana sani a rayuwarta, rashin gaya wa Abdulshakur tana sanshi, dama zata iya k'ara ganin shi a duniya, in har ta samu ta k'ub'uce daga hannun mugayen mutanen nan dukda tasan abu ne me wuya, tayi al-k'awarin baza tab'a bari ya s'ub'uce daga hannunta ba, zata ruk'e shi ta kama shi gam gam yadda ba wani abunda zai sake raba su ko ya shiga tsakanin su, hawaye ne suka dawo zuba a fuskarta,

"Oga oga"

Muryar wannan d'ayan taji wanda ya mik'owa ma ogan nasu (me suna blade) waya lokacin da za tayi magana da nabila, nabila bama tasan yin tunanin ta, Girgiza kanta tayi ta k'ara d'aga ido ta ganshi ya ruk'o wuyan rigar wani yaro k'arami wanda baifi shekaru sha takwas ba, ko wane hali ne ya saka shi shiga cikin irin wannan rayuwar, gani tayi ya cilla shi gaban ogan nasu wanda ya kame akan kujera yana busar sigari,

"wayar da kace ya cillar ta waccar matar ashe baiyi ba, kashe ta kawai yayi ya b'oye ta a cikin jikinshi, sai yanzu na kama shi a cikin kangon kusa ya kunna ta yana ta danne danne"

Cikin maganar shaye shaye yayi maganar samira ma da kyar ta iya gane me yake cewa, da taji an ambaci wayarta ji tayi kamar ta tashi ta wurta daga wurin su ta kira neman taimako, amma ba hali har yanzu tana k'ulle, ko salla sunk'i barinta tayi, ga yanzu tasan dare yayi sosai duk da bata san k'arfe nawa ba, kawai inda taji dad'i da har yanzu basu tab'a lafiyar jikinta ba, tasan in har suka tab'ata mutuwar wulaqancin da nabila ta fad'a zatayi zata tabbata, zaburar da ogan yayi ya mik'e ce ta bawa samira tsoro, ji tayi ya wan ke shi da wani wawan mari, ta tabbata in har ita ya mara da wannan jibgegan hannun nashi sai ta sume,

"Kai baka da hankali ne, kasan hatsarin abunda kayi, yanzu in har sukayi tracking wayar fa kashin mu ya bushe"

Tsabar yadda yake tsawa tare da maganar ya saka samira had'e jikinta wurin d'aya tare ta langwab'ewa a jikin bango, dan k'atuwar muryarshi abun tsoro ce, in har ka ganta a wurin da koma abun tausayi, ba d'ankwali akanta balle takalmi, rigar ta tayi bud'u bud'u da k'ura, d'ayan ne ya k'ara cewa,

"Banji wayar ta dad'e a kunan harda zai saka su su gano inda muke"

Blade ne ya kalle shi tare da zuk'ar sigari, sai da ya cika bakinshi da hancin shi da hayak'inta sannan ya busar had'e da cewa,

"Ka tabbata?"

D'aga mishi kai yayi, blade ce mishi yayi a yaje ya hukunta yaron dan yayi babban laifi, haka ya k'ara jan yaran wanda yake ta faman kuka yana bada hak'uri a lokacin wani ya sake k'arasowa wurin ya rad'awa ogan nasu wani abu, juyowa yayi ya kalli samira tare da sakin dariya,

"Inajin wanda muke jira ya k'araso"

Gaban samira ne yayi mummunar fad'uwa wa, hantar cikinta ce ta kad'a tsoro ya sake kamata, gani tayi kowa na d'akin ya juya ya fita harta ogan nasu blade, haba jikin Samira ya fara rawa, gaba d'aya ta rikice addu'a ta ci gaba da yi a ranta tare da sunkuyar da kanta k'asa dan bata san ganin wane zai shigo,

"Well, well, look who we have here"

Ismail, abunda tace a ranta kenan saurin d'aga kanta tayi dan ta tabbatar ko shine, tana d'aga kanta kuwa ta ganshi a ga banta yana sakar mata murmushi, zuciyar ta ce ta sake mahaukacin bugawa, shikenan tata ta k'are, wannan la'anan nan ne daman, dad'in da take ji zata mutu cikin mutuncin ta gaba d'aya ya rushe tasan tsinan nan bazai tab'a kyeleta ba, hawaye ne suke sake zubawo daga idanunta, gani tayi ya d'auko kujerar da take kwali d'aya a wajan ya saka a gabanta ya zauna tare da hard'a k'afa, samira k'ara matsawa tayi a jikin bango ta k'ara shigewa ga tsoro da ya cika idanunta da fuskar ta,

"At last, yau ga ki ga ni"

Yayi maganar cikin kwanciyar hankali, da nishad'i, samira shashek'ar kuka ta fara,

"No no daina kuka, dan yau sweetheart dink'i abdulshakur baya nan balle ya rarrashe ki"

Yadda yayi maganar kasan abun nayi mishi mutuk'ar dad'i, samira kallan shi tayi da dalla mishi muguwar harara, k'azamin bakin shi ya daina kiran sunan shakur d'inta, ji tayi kamar ta tashi ta shak'e shi, wani tsnar shi take ji ta mamaye mata zuciya, k'arshen irin su ismail bazai tab'a yin kyau ba, shi da nabila sai Allah ya nuna musu tun kan subar duniya,

"Nasan kinsan yarda saurayin ki ya saka ni a gaba gaba d'aya ya b'ata mun kasuwanci na"

Wani irin kallo yake mata kuma a lokacin da yake mata maganar, kallan tsana, itama ta tabbata irin kallon take mishi,

"Ni da nake abokin shi shekara da shekaru ya zubar a shara saboda mace irin ki"

Ya nuna samira, ita kuwa ta kafa mishi ido wanda ke d'auke da tsan tsan tsana dan bata san mai zata ce mishi ba saboda gaba d'ayan ta a tsorace take,

"Da nabila ta gaya mun me zata miki naga shine babbar ramuwar da zan iya yi akan shi, a ganin ki, in har yaji labari anyi amfani dake kuma ba mutun d'aya ba ba biyu ba uku ba kafun a saka wuk'a a farke kayan cikin ki ya zaije"

Wani amai ne ya taho wa Samira, har ta fara yin shirin zubar da duk abunda ke cikinta a k'asan wurin, bayan zubar da hawayen da idanuwanta ke yi, tana ji ismail na sakin dariya, amma gaskiya ko a cikin marasa Imanin shi na k'arshe ne, bata tab'a had'uwa da mugun mutum irin shi ba a rayuwarta, gaba d'aya abokan abdulshakur nada mutunci da kamala shi kad'ai ne ya fita daban,

Ganin shi da tayi ya tashi ya fara yowa kanta ne ya saka ta fara motsi tana jan igiyar dake d'aure a bayan hanunta, so take kawai ta kwace, in har babu wanda zaizo cecanta Allah ya kawo mata mutuwar ta yanzu yanzun nan akan dai taga cin mutuncin da yake shirin yi mata, hawaye basu bar zuba a fuskar ta ba kuma bata daina jan igiyar ba, hannunta har ya fara yin jaa dukda bak'ar fatarta, ta jima kanta ciwo saboda igiyar akwai kwari, da taga ya doso dab da ita kawai ta kulle idanunta tana jiran taji k'azamin hannunshi a jikinta,

Amma sai jin jiniyar y'an sanda sukayi, sauri samira tayi ta bud'e idanunta, k'ara jin jiniyar tayi a kusa kusa kuma kamar da yawa, tana ganin ismail ya fara rikicewa yana waige waige, jin k'arar harbin bindiga sukayi, samira ta k'ara lumshe idanunta, ba kalar masifar da bata gani ba yau dai, tsabar bata cikin hayyacinta gaba ki d'aya bata yi tunani zuwa cecanta akai ba, ji tayi kamar ba kowa a wurin, tana bud'e idanunta ai kuwa ta nemi ismail ta rasa, yayi ta kanshi kenan,

Ji tayi an shigo wurin a guje, bata ga fuskar wane ba saboda akwai d'an duhu gashi kuma daga nesa, amma tunanin ta wani daga cikin y'an daban ne ya shigo, k'ara mak'alewa tayi jikin bango ta fara yin addu'a, tare  da sunkuyar da kanta da k'ara kulle idanunta, bata san taga ko wane bala'i dake shirin faruwa da ita, jin da tayi kamar an zube a k'asa kusa da ita ne ya saka ta fara bud'e idanunta a hankali,

Abdulshakur ta gani a gaban ta, abunda ya fara zuwa kanta shine ta fara gane gane ne, dan ko da wasa bata yi zatan shi bane, gaba d'aya ya canza ya koma kamar bashi ba, k'ara ji tayi an shigo wurin da sauri ta d'aga idanunta tayi shima bata ga fuskar shi ba sai da ya matso kusa, fuskar ya mu'azzam ce, sai a lokacin abun ya fara shigar mata kai, wani kuka ta saki da ta gane da gaske sune suka zo cecanta, kuka take yi sosai har mu'azzam yazo ya cire mata igiyar hannunta bata sani ba, yana cirewa ta tsinci kanta a cikin k'irjin abdulshakur, ya k'ank'ameta da mugun k'arfi yama manta da mu'azzam a wurin, tana ji bayan rigarta ya fara jek'ewa alamar kuka yake, wani irin dad'i ne ya kamata Allah yayi tana da sauran rai zata k'ara ganawa da masoyanta,

Godiya ta fara yima Allah da ya amshi addu'ar ta, kuka sosai ita da abudulshakur suke a wurin shi kuwa mu'azzam ya tsaya yana ta kallon su, amma kika k'ura mishi ido shima zaki ga hawaye na zuba a fuskar shi, sai da sukayi kuka mai isar su sannan suka saki juna, gaba d'aya abdulshakur ya fita daga hayyacin shi, har wani duhu yayi a yini d'aya, samira da take kallanshi taji sanshi ya k'ara shiga zuciyar ta tausayin shi ne ya sake kamata, Allah ne k'adai yasan halin da ya shiga da yaji an neme ta an rasa, kallon shi cikin kwayar idanun shi tayi da suka zama jaa, a hankali da bud'e bakinta ta furta abunda tafi komi san gaya mishi a yanzu,

"I'm sorry"

Tana gama fad'a taga kwallar hawaye ta zubo daga idanunshi, tausayin shi ne ya sake kamata, ta gode Allah da yasa ta sake ganin shi da idanunta, muryar da suka ji ce ta saka ta d'agowa daga kallan abdulshakur d'in da take, wanda shi kuwa a lokacin ya saka hannun ya share hawayen fuskarshi,

"Ina ji mun kama su gaba d'aya"

Kalan abdulshakur ahmad yayi, sannan yace mishi,

"Ya kamata kazo ka ga harda wa muka kama a cikin su"

Samira tasan sarai me haka yake nufi, ismail zaije ya gani, tasan in abdulshakur ya ganshi a wurin sai abun ya dake shi sosai, tana jin idanun shi a kanta, itama juyowa tayi ta kalle shi tare da yi mishi murmushi, dan tasan shine k'ad'ai abunda zai ta dashi daga wurin ta, a hankali ya mik'e ya bar wurin kana gani ba dan yaso ba, suna fita mu'azzam ya k'arasa ya kwance mata igiyar k'afar ta, tare da ruk'eta ya tayar da ita tsaye, kallan shi tayi shima tace mishi su mama fa, bai ce mata komi ba, bai bata amsa ba haka ya kamata har suka fita daga cikin kangon.


(Finally she is safe, and how do you like abudulshakur and samira's reunion 😂😍😍,

Please vote and share ❤️❤️

המשך קריאה

You'll Also Like

37K 1.3K 32
Karki kashe! Tsura ma screen din wayar tayi tana kallo, ta rasa me Rayhan yake nufi da ita sam a rayuwarta. Send me you pic I wanna see that beautifu...
1.4M 59.2K 70
ငါလား.... စိတ်ချ...... နိဗ္ဗာန်ရောက်ရင်လည်း မင်းကိုပဲ ချစ်နေအုံးမှာ.......... သုနေတင်ထွဋ် ကမ္ဘာပျက်သလို လေပြင်းမိုးသံတွေထ...
8.5K 909 69
Love, Romantic, sadness, happiness komai ya haɗa ku shiga ku sha karatu.
438K 23K 51
အခြေအနေတစ်ခုကြောင့် လက်ထပ်ဖြစ်ခဲ့ကြတယ် အန်တီက ရိုးရဲ့ ဇနီးမယားပါပဲ... အေျခအေနတစ္ခုေၾကာင့္ လက္ထပ္ျဖစ္ခဲ့ၾကတယ္ အန္တီက ရိုးရဲ႕ ဇနီးမယားပါပဲ...