NAJWA Complete ✔

By MSIndabawa

59.3K 4.5K 9

Najib yaron littafin bai dda buri da aaddu'a sai ta Allah yaya bashi mace ta gari mai ilimi Sumaiyya Yarinya... More

1-5
11-15
16-20
21-25
26-30
31-35
36-40
41-45
46-50
51-55
61-65
66-70
71-75
76-80
81-85
86-90
91-95
96-100
101-105
106
107-110
111
113
114
115
116
117
118
119
120
121
122
123
124
125
126
127
128
129
130
131
132
133
135
136
137
138
139
140
141
142
143
144
145
146
147
148
149
150
151
152
153
154
155
156
157
158
159
160
161
162
163
164
166
167
168
168 End

165

714 52 0
By MSIndabawa

*NAJWA*

BY *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Dedicated to *Rashida A Kardam*
*Anty Rash*

*Allah dafa miki. Allah karawa Mama lafiya da nisan kwana. Ameen*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya online writers*

*Allah kara mana hakuri da juriya.*
*Ameen*

*Gidan aminci da karamci. Allah kara basira Ameen*

Page
*165*




Magariba da tayi ne yasa ba a tafi kai Najwa ba.

An ajiye ta a dakin Mami, inda dakin yake a ciki da yan uwan Mamin ta, da yan uwan Dadyn ta.

Duk addu'a suke mata, Najwa na kwance cikin sitirar ta.

Kuka kuwa gidan duk a rikice yake. Mamin Najwa sam bata zo ba.

Ta ce,
"Da zuwana da ba zuwana duk daya ne, addu'a ce dai kuma bakina bazai taba daina yiwa Najwa addu'ar samun Rahama ba."

Mami dake gefen Najwa ta zuba mata ido taga kamar likafanin na motsi,

Bude fuskar Najwa tayi, ji tayi, tana cewa,
"Hamma! Hamma!"

da sauri Mami ta kalli jama'ar dakin tana cewa,
"Najwa bata mutu ba."

Da sauri jama'ar dakin suka yo kan ta, Kuje ku kira min driver.

Mami ta fada tana dauko wani katon hijab.

Najwa ta sakawa sannan ta kira Dady da kansa yazo ya dauke ta suka yi asibiti.

Suna zuwa aka amshe ta aka yi office din Najib inda ake duba ta.

Ruwa suka jona mata, Dr Farouk kuwa sai Hamdala yake ga Allah da yasa Najwa bata mutu ba.

Cikin ikon Allah wajen karfe Dayan dare sai ga Najwa ta bude ido, Mami ta gani zaune a gefen ta.

Mami ta kalla, ta ce,
"Mami, ina Hamma?"

"Sannu Najwa, sannu kin tashi?"
Ta danna bell da sauri Dr Farouk ya shigo, dudubata yayi, ya ce,
"Alhamdulilah! a samu a gasa mata jiki sai a bata ruwan zafi ta sha."

Mami da kanta ta hada mata ruwan wanka, wanda Najwa kasa tafiya ma tayi sai a kujera aka daurata aka kai ta ban daki.

Mami da kanta ta gasa mata jiki, suka fito ta canja mata kaya sannan Dady ya tayata daura ta akan gado.

Duk abinda Likita ya ce ai mata sukai masa.

Sai dai duk yadda ta motsa jikin ta sai ta ce,
"Wash!"

Mami sai sannu take mata, ai dole jiki yai ciwo ace kana kwance kwana da kwanaki.

Mami tausayin Najwa take dan har hawaye sai da ta zubar mata.

Najwa ta rame sosai, tayi haske idon ta duk sun zurma.

Allura aka karai min na koma bacci.

Da safe ina tashi Mami ta karai min wanka ta gasa min jiki, Dr Farouk ne ya bata wani magani ta shafa min a jiki na.

Ruwan Zafi kadai ake bani tin daren jiya.

Ganin har lokacin Hamma Najib be zo ba yasa Najwa mamakin ina yake, ko tsoron ta yake ji ne?

Kasa daurewa Nayi na kalli agogon office din, karfe Takwas da rabi, amman har yanzu ba Hamma wanda duk jama'ar da suka zo ta'aziyya ta kowa yazo yai min sannu.

Har su Mami nah duk sun kira suna min sannu, Basma kuwa ai sai murna Addu'ar ta bata mutu ba.

Ina kwance ina tunanin Hamma, abin na damuna na rashin ganin sa.

Ni dai kasa Daurewa nayi, nace,
"Mami ina Hamma ne, ko baya nan ne?"

"A'ah yana nan, shima yana cikin asibitin nan be da lafiya, amman yanzu Dady ya ce, min ya farka, ki kwantar da hankalin ki da sauki."

Hankalina ji nayi ya kara tashi da a kwance nake da sauri na mike zaune, zaman kasa yi min yayi na mike da sauri.

Ai kuwa nayi gaba zan fadi saboda rashin kwarin jiki na.

Da sauri Mami ta riko ni, ta ce,
"Ina zaki?"

"Mami gun Hamma zani."
Zaunar da ni Mami tayi, ta ce,
"Kiyi hakuri, anjima kaje kinji."

Dan dole na hakura, kwanciyya nayi amman duk hankalina baya jikina.

Karfe uku ina kwance naji an budo kofar dakin Juyowa nayi.

Hamma na gani da sauri ya shigo. Mikewa nayi zaune da sauri.

Sai da yazo gaban gadon ya durkusa, hannun sa ya kai, kan wuya na, ya taba fuskata, ya juyar da ita gefe, ya kuma juyar da ita gefe.

Wani murmushi ya saka, rumgumeni yayi a jikin sa, ya dago ni ya kuma mayar dani.

Sai da yai haka sau uku sannan ya kamo hannuna, ya kai dan yatsana bakin sa.

Cizar hannun yayi, wata kara na saki da sauri ya zare hannun yana dariya. Nima dariyar nayi.

Kan gadon ya hau ya zauna, ya janyo ni jikin sa ya rumgume ni.

Saukar danshi naji a bayana wannan yasa na dago da sauri.

Haawaye na gani a idon Hamma Najib,
"Haba Hamma mene abin kuka?"

"Najwa hankalina ya tashi sosai, kwakwalwata ta samu rudani da kin mutu da bansan ya zanyi da rai na ba. Da bansan ina zan shiga ba. Da bansan ya...."

"Haba Hamma, kamar ba musulmi ba, zaka dinga ringa wannan maganar, baka san Allah na jarabar bawa yaga ya zai yi ba.
Ka kuma san Allah me rahama da jinkai da ya baka ni, da ya dauke ni, haka Allah zai mayar maka da wacce tafi ni, hamma kana mika komai ga Allah dan zai iya jarabar ka yaga yadda zakayi."

Yatsan sa ya saka ya rufe min baki, ya ce,
"Najwa nasan da wannan kuma ina kokari, amman ki tayani da murna da godewa Allah da ya bar min ke."

Ya fada hawaye na zubowa daga idon sa.

Magana ya cigaba dayi,
"Bazan iya kwatan ta miki halin da na shiga ba da baki da lafiya, haka nan bazan iya kwatan ta miki halin da na shiga ba da aka ce min kin mutu. Cikin kan kannin lokaci na koma wani iri...."

Mami ce ta shigo dakin da sallama. Da sauri Najwa ta janye jikin ta daga na Najib.

Basket ne a hannun ta, mikawa Najib tayi, ta ce,
"Ka bata abincin ta ci."

Kai ya gyada mata, fita tayi. Kallon sa ya maida kan Najwa wacce take shafa cikin ta.

Tinda ta farka bata ji motsin da ya sabai mata ba. Ko lafiya?

Tausaya mata yayi, ya ce,
"Baby na. Komai ya samu ga bawa mukadari ne, kuma haka Allah ya kaddarar ta mana."

"Haka ne Honey. Me ya faru?"
Hawayen idon sa ya goge ya ce,
"Baby mun rasa Babyn mu."

"Innalillahi wainna illahir rajiun!"
Ta fada a cikin zuciyar ta.

Shiru tayi, kallon ta yayi ya jawo ta jikin sa, yana lallashin ta dan yasan kukan zuci take duk dan kar ta tayar masa da hankali.

Najwa bata taba kara sanin tana son Cikin jikin ba sai yanzu da ta rasa shi.

Tabbas kamar ya sani kukan zuci take dan sai ajiyar zuciya take saukewa.

Sun jima a haka kafin ta daina.

Zaunar da ita yayi ya zubo mata abincin da Mami tayo mata.

Dankali ne da hanta ta dafo mata, sai farfesun kayan ciki.

Kadan ta iya ci dan cikin ta a cunkushe yake.

Suna gamawa cikin ta ya hau ciwo nan da nan Najib ya rikice.

Dr Farouk ya kira, dubata yayi ya ce tasha magani ba wani abu bane, rashin cin abincin da batayi ne kwana biyu shiyasa. Amman a hankali zata daina ciwon in ta ci abinci.

Shifa Najib yana mantawa dashi likita ne, dan indai abu ya samu Najwa rikicewa yake ya manta da komai da komai.

Sai da ta Sha maganin sannan cikin ya lafa mata.

Bacci ne ya sauke ta. Kwanan su Uku suka Koma gida.

Gidan Mami suka koma dan Mami sam taki ta bar mishi Najwa dan har yanzu bata gama warwarewa ba.

Haka ya hakura, kayan da Mami tasa ya dauko a gida shi ya tuna masa da Sumaiyya ma.

Yana shiga gidan yaga shigar ta part din ta ita da wasu kawayen ta.

Bangaren Najwa yayi ya debo mata kayan sawar ta.

Har zai wuce ya ce, bari ya leka gun Sumaiyya.

Zai shiga kenan yaji shewar su, suna cewa,
"Ashe kin rabu da Alakakai."

Suka kara kwashewa da dariya. Be san da wa suke ba kawai ya juya ya bar wajen.

Gidan Mami ya koma, dakin Mami ya shiga dai dai fitowar Najwa daga wanka kenan.

Karasawa yayi ya kamo ta, ya zaunar da ita a gefen gado.

Shi ya shirya ta, sannan ya saka mata kaya.

Kwanciyya tayi dan bacci take ji. Shima gadon ya hau zai kwanta.

Da sauri ta Najwa ta mike, kallon ta yayi ya ce,
"Menene cikin ne?"

Kai ta girgiza ta ce,
"Allah ka tashi ka fita salam Mami tazo ta ganmu tare."

Kallon ta ya tsaya ya ce,
"To shine me?"

"Haba Hamma kai fa baka da kunya ko?"
Baki ya bude yana kallon ta.

Ya ce,
"Nine banda kunya ko?"

Kai ta girgiza,
"A'ah zan nuna miki bani da kunya ne a gaban Mami."

"A'ah Hamma ayi hakuri."
"Naki."

"Shikenan."
Ta fada tana mikewa.

Janyo ta yayi ta fada jikin sa,
"Yi hakuri man."

Shiru tayi tana kokarin tashi daga jikin sa.

Tausa ya farai mata, tausar da rabin ta tsokana ce.

Tini jikin ta yai sanyi tai shiru tana amsar sako da yake aika mata.

Jin shirin yai yawa yasa ya leka fuskar ta.

Idon ta a lumshe, sai murmushi take.

Cakul kuli yai mata ai kuwa da sauri ta mike tana dariya.

"Haba Honey Bacci fa nake yi."
"Na sani amman akwai abinda nake so muyi magana akai."

Mikewa tayi zaune, ta ce,
"Ina ji."


*MS Indabawa*

Continue Reading

You'll Also Like

10.1K 591 13
Hamida was an ordinary girl trying to fit in, into the world entirely. after the death of her father, she and her mother moved in to stay with her Un...
9.3K 104 1
Khairiyya was lost and couldn't think of a perfect solution to what happened. At last she decided to keep it a secret forever without telling anyone...
40.9K 624 16
DELULU & GUILT PLEASURE
43.7K 1.2K 25
A girl that do drugs and a Soja that fight drugs, kakakara kaka.