NAJWA Complete ✔

By MSIndabawa

59.6K 4.5K 9

Najib yaron littafin bai dda buri da aaddu'a sai ta Allah yaya bashi mace ta gari mai ilimi Sumaiyya Yarinya... More

1-5
11-15
16-20
21-25
26-30
31-35
36-40
41-45
46-50
51-55
61-65
66-70
71-75
76-80
81-85
86-90
91-95
96-100
101-105
106
107-110
111
113
114
115
116
117
118
119
120
121
122
123
124
125
126
127
128
129
130
131
132
133
135
136
137
138
139
140
141
142
143
144
145
146
147
148
149
150
151
152
153
154
155
156
157
158
159
160
161
162
164
165
166
167
168
168 End

163

742 53 0
By MSIndabawa

*NAJWA*

BY *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Dedicated to *Rashida A Kardam*
*Anty Rash*

*Allah dafa miki. Allah karawa Mama lafiya da nisan kwana. Ameen*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya online writers*

*Allah kara mana hakuri da juriya.*
*Ameen*

*Gidan aminci da karamci. Allah kara basira Ameen*

Page
*163*



*INDABAWA Hausa Novel group tnc for love nd supporting.*
Allah barmu tare Ameen.



Kallon sa take a ranta tana fadin sai ta san yadda ta raba Najwa da shi.

"Ya kika tashi?"
ya tambaye ta yana zama a kan kujerar gaban madubi.

"Lafiya lou! Ya Najwan?"
Ta tambaya

Kallonta Najib yayi, kafin yace,
"Tana lafiya, kinsan masu ciki sai da  lalashi."

Zabura tayi jin ya ambaci ciki.
Kallon ta yayi ya ce,
"Lafiya?"

"A'ah ba komai."
Ta fada cikin rashin gaskiya.

Kafada ya dage ya ce,
"To ni zan fita sai na dawo."

Bama taji me yace ba saboda ta tafi tunanin Najwa na da ciki.

"Tab ai bata isa ba, ciki tazo ta haihu, ta gaje dukiyar sa."
Ta fada a fili.

Dakin ta fara zagayewa tana tunanin abinda zatayi.

Ta jima kafin tayi  tsalle na tuna abin yi.

Sai da ta tabbatar Najib ya bar gidan sannan tayi wanka ta shirya.

Najwa kuwa tana can ta raka mijin ta tana masa addu'a.

Falo ta koma tana zaune tana waya da Hamma Salim.

Suna gamawa ta mike dan zagawa bayan gidan.

Sanye take da dogon hijab har kasa fuskar ta tayi kyau tana tafiya tana kallon wajen dan duk kallon da take masa ta taga ne bata taba zuwa gun ba.

Kamar ance ta kalli gefe taga Sumaiyya wata faduwar gaba tayi da sauri ta fara karanta addu'a a cikin ran ta.
*Allahumma inna naj'aluka finuhurihim wana uzubika min shururihim*

Gaba tayi, ta zauna a gun da aka tanadar dan zama a huta.

Ta jima a gun dan sallah azahar ita ta tashe ta.

Bangaren ta ta koma, tayo alwala ta tada sallah.

Tana idar wa ta shiga kitchen, tayi miyar ta tin jiya dan haka ta daura farar shikafa da taliya sai kwai da ta dafa.

Tayi hadin Kabej da dankalin turawa da bama da waken gwangwani.

A firij ta saka sai lemon Mangoro da tayi.

Falo ta koma zama tayi da bismillah tana shafa cikin ta. Addu'a ta tofa a cikin nata. Waya ta dauka, ta kira zahra. Mikewa tayi ta dauko Maltina a cikin firij ta dawo ta zauna.

Suna gama waya tayi waya da Mami, Mami na kara jan hankalin ta akan ta dage da addu'a da karanta alkur'ani ko dan cikin jikin ta.

Godiya Najwa tayi Mami na saka mata albarka.

Tana gamawa ta kira Mamin Najib ta gaishe ta, tambaya ta hau yi mata me take so?

Ba abinda take bukata dan haka Mami ta barta.

Sumaiyya kuwa tana can tana leken Najwa har ta bar wajen sai da ta dauki awa wajen biyu sannan ta shiga daki ta dauko maganin da aka bata da Maganin zubar da ciki tayi bangaren Najwa.

Tana cikin bude Maltinar zata sha kenan sai ga Sumaiyya ta shigo.

"Innalillah wainna illahir rajiun!!"
Ta fada a cikin ranta.

Karasowa tayi ta  kalli Najwa ta kalli dakin, ta ce,
"Yauwah daman Abinci nake son in kinyi ki zubo min yunwa nake ji."

Mikewa Najwa tayi tana ajiye Maltinar akan table din dake gefen ta.

"Lah Anty ba komai. Bari na kawo miki."
Tayi cikin kitchen din.

Da sauri Sumaiyya ta matsa tana saka mata magungun nan a cikin maltinar.

Tana gama zubawa kenan sai ga Najwa. mika mata tayi.

Amsa tayi. Ta ce,
"Sannu."

"Yauwah!"
Daukar matlinar tayi zata sha, dakatar da ita Sumaiyya tayi dan ta tabbata kwayar bata narke ba.

Ta ce,
"Najwa sai naga kamar maltinar da sanyi ko?"

"Eh!"
"Ai kuwa ba ason masu ciki suna shan kayan sanyi ki bari ta dan wuce ko."

"Toh!"
Najwa ta ce, ta ajiye.

Tana nan a tsaye dan so take ta narke taga ta sha ta tafi.

Najib ne ya kira, dagawa tayi tana masa ya aiki ya ce mata ai yana hanya.
Addu'ar dawo gida lafiya tai masa sannan ta kashe wayar.

Sumaiyya na tsaye tana kallon ta. Sai da tabbatar da kwayar ta narke sannan ta ce,
"Ki sha ai ta rage sanyi. Bari naje naci abinci.'

Dauka Najwa tayi tana kurba, juyawa tayi tafi cikin murna da jin dadi.

Ko falo bata rufe ba taji shigowar Najib da sauri ta shige ta rufe kofar ta.

Bangaren Sumaiyya ya yi, yana shiga ya ga alamun rashin gaskiya a tattare da ita

"Allah ya shirya ki."
kawai ya iya fada ya fito daga bangaren nata.

Najwa kuwa tana can tana shan malt din ta har Najib ya shigo.

Da sauri ta taro shi tana masa sannu da zuwa.

"Yauwah Baby na. Sannu da kokari."
Suka koma cikin falo.

Abincin sa ta gabatar masa ta zuba masa sannan ta dauki ragowar malt din ta karashe.

Kallon ta yayi ya ce,
"Ke dai kinfi ganewa kwadayi ko?"

"Love to ba Babyn ka bane."
"Ai shi yasa nace sai na Zane  shi ya fito."

Dariya tayi, ta kwana akan kujera. Mintin ta uku da kwanciyya taji cikin ta na hautsinawa.

Da sauri ta mike tana fada.
"Innalillahi wainna illahir rajiun."

Kallon ta Najib yayi, ya ce,
"Menene?"

Kasa magana tayi sai cikin ta da take nuna masa.

Kwanciyya tayi tana juyi da sauri Najib yayo gun ta. Yama rasa abinda zai yi.

Cikin minti biyu sai ga fara kumfa na fitowa daga bakin ta.

Da gudu ya dauke ta yai ma Dariver magana ya fito da mota.

Asibiti suka nufa da gudun gaske. Yana zuwa yayi office dinshi da ita.

Da gudu sauran ma'aikatan asibitin suka karaso office din.

Shi kasai mata komai yayi sai hawaye dake zubowa daga idon sa.

Hannun sa kuwa duk ya baci da jini abinda ya kara daga masa hankali kenan.

Addu'a yake aran sa yana Cewa Allah yasa cikin be fita ba.

Mutum mutumi ya zama ya kasa koda motsawa daga inda yake.

Da kyar ya iya ciro waya ya kira Mami ya shaida mata abinda kefaruwa.

Mami cikin tashin hankali ta taho asibiti.

Najib na ganin ta ya fada jikin ta yana kuka sai kace karamin yaro.

Lallashin da take yi tana kwantar masa da hankali.

Likitoci sun fi biyar ne suka rufa akan Najwa.

Har magariba suna kan ta da kyar Mami ta lallaba Najib ya tafi massalacu Dan yayi sallah.

A can ma addu'a ya dinga wa Najwa. daga massalaci ya Koma cikin.

Ba kowa a dakin sai Mami dake zaune a gefen ta. Ta zuba tagumi, Kallon sa Mami tai masa nuni da hannu alamar yazo.

Kamar karamin yaro haka ya je wajen ta. Najwa ya kalla ya ce,
"Mami me sukace yana damun ta.?

"Kaga Najib ka kwantar da hankalin ka, ba wani abu bane kaje Dr Farouk yai maka bayani. Kasan dai kowa da kaddarar sa dan haka ayi hakuri a rumgumi kaddarar da Allah ya saukar mana kaji."

Kai ya gyada dan sam bajin abinda Mami take fada yake ba. Najwa kadai yake kalla yana can tunanin me ya same ta da halin da yanzu take ciki.

Fita yayi daga office din shi ya nufi office din Dr Farouk.

Kallon sa Dr Farouk yayi ya ce,
"Dr Najib Kaje kaga Najwan ne?"

"Eh naje me yake damun ta ne?"
"Zauna muyi magana man."

Kai ya girgiza alamar bazai iya ba.
"Fada min abinda ya samu Najwa kawai dan shi kadai ne zai kwantar min da hankali."

Dafa shi Farouk yayi, ya ce,
"Haba Friend cool ur mind Najwa tana lafiya, sai dai An sawa Najwa guba a abinda ta ci ko ta sha, haka nan tasha maganin zubar da ciki."

Kai ya hau girgizawa yana fadin,
"Najwa bazata taba aikata haka ba, Najwa bazata taba gigin zubar da ciki ba. Tabbas akwai wanda yai mata haka. Ai kuwa duk wanda na gane da hannun sa a cikin wannan al amarin bazai ji da dadi ba."

Kallon sa ya mayar kan Farouk ya ce,
"A wane hali take ciki yanzu?"

"Eh to tana da rai sai dai abinda ke cikin ta ya zube ayi hakuri haka Allah ya kaddara ina maka jaje Allah yasa haka ne mafi alheri."

Ido Najib ya damke, yana jin wani zafi a zuciyar sa da idanun Sa.

Ido ya bude, Wanda sukai Jajir dasu sai kace jini.
"Nagode!"

Ya fada cikin raunin murya ya juya ya fita. Office din shi ya shiga.

Akan gadon da Najwa take kwance ya kifa kansa.

Mami ce ta matso ta dago shi, ta ce,
"Haba Son ka zama jarumi me karbar kaddara me kyau da mara kyau. Allah ya jarabbe ka yaga yadda zakayi ka daure kaci wannan jarrabawar. Insha Allahu zakaga abu me kyau nan gaba."

Kai ya gyada mata kawai yana goge hawayen idon ta.
"Taso kaci abinci."

Kai ya girgiza mata. Ya ce,
"Wallahi bazan iya ba. Mami bari naje massalaci ga kiran Sallah isha'i."

"Allah bada sa'a sai ka dawo."
ya fita.

Sumaiyya kuwa tinda taga fitar Najib da Najwa a hannu kuma hankalin ta ya tashi sai yanzu take na damar abinda taso aikatawa.

Kirjin ta na dukan uku uku take da haka ta kira Anty ta.

Antyn ta sai karin gwiwa da ta dada mata ta nuna kar ta damu ai ba asan ita bace.

Da haka ta samu ta dan kwantar da hankalin ta.

Najib ya jima a massalaci yana addu'a Allah ya tayar mata da Najwa.

Sai wajen goman dare sannan ya dawo cikin asibitin duk ma'akatan asibiti tausayin Najib suke dan yanzu suma kara tabbatarwa da irin son da yakewa Najwa.

Cikin kan kannin lokaci ya rame yayi zuru zuru.

Yana shiga gun Najwa ya je ya kalle ta, ya tofa mata addu'a sannan yayi wajen Mami.

"Mami kinji me ke damun Najwa?"
"Naji Najib amman ban san wanda zai mata haka ba."

"Insha Allahu koma waye asirin sa zai tonu."
"Ya kamata ka tafi gida ko?"

"Gida Mami. Wallahi Mami ba zan iya barin Najwa ba. Dan Allah Mami ki barni agun ta dan Allah Mami hankalina bazai kwanta ba in nayi nesa da ita."

Kai kadai Mami ya kada ta ce,
"Zauna kasha ko ruwan zafi ne."

Da kyar yasha dan cewa yayi Najwa bata ci komai ba shima bazai iya ci ba.

Dadyn sa baya gari dan haka besan me yake faruwa ba.

Ranar tare suka kwana da Mami da Najib.

Najib ko runtsawa be ba. Daga yayi sallah yayi sallah yai addu'a zai zo ya kalli Najwa.

Cikin kan kanin lokaci tayi rama sosai, ta kara fari.

Fuskar ta dauke da murmushi. Sai ya sumbace ta sannan yake komawa ya kara tada sallah.

Haka yai tayi har akai sallah asuba ya tafi massalaci. Sai bakwai ya dawo cikin office dinshi.



*INDABAW

Continue Reading

You'll Also Like

45.2K 702 16
DELULU & GUILT PLEASURE
1.5K 160 52
Rayuwar auren su abar kwatance ce. Soyayyar da sukewa junan su, mai girma ce. Tarbiyyar da sukayi wa yaransu mai kyau ce. Komai na Mukhtar da Hafsah...
47.2K 4.3K 77
The life of a Soldier
278K 38.5K 20
လက်တွေ့ဘဝနှင့် နီးစပ်ချင်ယောင်ဆောင်ခြင်း