NAJWA Complete ✔

By MSIndabawa

59.5K 4.5K 9

Najib yaron littafin bai dda buri da aaddu'a sai ta Allah yaya bashi mace ta gari mai ilimi Sumaiyya Yarinya... More

1-5
11-15
16-20
21-25
26-30
31-35
36-40
41-45
46-50
51-55
61-65
66-70
71-75
76-80
81-85
86-90
91-95
96-100
101-105
106
107-110
111
113
114
115
116
117
118
119
120
121
122
123
124
125
126
127
128
129
130
131
132
133
135
136
137
138
139
140
141
142
143
144
145
146
148
149
150
151
152
153
154
155
156
157
158
159
160
161
162
163
164
165
166
167
168
168 End

147

643 44 0
By MSIndabawa

*NAJWA*

BY *Maryam S Indabawa*
*Mans*

Dedicated to *Rashida A Kardam*
*Anty Rash*

*Allah dafa miki. Allah karawa Mama lafiya da nisan kwana. Ameen*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya online writers*

*Allah kara mana hakuri da juriya.*
*Ameen*

*Gidan aminci da karamci. Allah kara basira Ameen*

Page *147*

Na gaida ke, *Princess Amrah* Ina yinki. Allah kara basira da zakin hannu. Allah saka miki da alheri.
*Ameen*



Summy kuwa bata tashi dawowa ba sai karfe dayan dare, lokacin Najib har yayi bacci.

Ganin fitilar barandar sa a kunne wannan ya tsorata ta. Amman ta dake tayi cikin dakin ta.

Kwanciyya tayi tana sake sake a ranta taje ko kar taje  daga baya zuciyar ta, ta yanke mata hukunci akan tayi kwanciyyar ta. Ai kuwa haka akayi.

Washe gari da safe ta tashi da wuri ta shiga kitchen ta saka masu aiki su shirya mata break dan akwai abinda boka ya bata ta saka masa a abinci.

Dankali tasa aka soya masa sai ruwan tea da farfesun kayan ciki.

Bangaren sa ta kai masa wanda shi ko tashi beyi bama.

Dakin ta, ta koma ta zauna tana jiran fitowar sa.

Sai karfe sha biyu ya tashi yana tashi yayi wanka ya shirya cikin wani farin yadi.

Wayar sa ya dauka ba abinda ya gani sai sakon Najwa.

Murmushi yayi ya kira ta.
"Barka da safiya ranka ya dade."

"Barka kadai  baby na. Kin tashi lpy."
"Lafiya lou Alhamdulilah. Ya ka tashi?"

"Na tashi lafiya Amarya ta. Yasu Mami."
"Lafiya suke."

"Masha Allah daman zan fita nace zan kira, zanje wajen Mami, daga nan zan leka asibiti."

"To Yallabai! Allah ya dawo dakai lafiya Allah tsare min kai. Ka kular mana da kan ka."
"Kedawa?"

"Antyna man."
"To sai anjima."

Sukai sallama shi sai a lokacin ma ya tina da Sumaiyya.

Fita yayi, har zai fice daga gidan ya dawo dan duba ta.

Tana zaune a falo ba laifi tayi kyau da ita.

Tana ganin shi ta mike, kallon ta yayi ya dan yi murmushi.

Zama yayi, ya ce,
"Ina kika je jiya."

Kame kame ta fara yi. Kallon ta yayi yaga ba alamun gaskiya a tare da ita.

"Kiji tsoron Allah dai ki sani duk abinda kike Allah na ganin ki. Kuma Allah zai tambaye ki. hakanan duk abinda kike kina tsoron Allah kuma ki sani in ni da wanda kika je gareshi baya ganin ki Allah na ganin Kuma zai nuna aranar Alkiyama ranar da babu yafiya komai yazo karshe. Kiji tsoron Allah ki sani raba 'da da mahaifi ba abune me wahala ba. Amman in har Allah ya baki nasara to ki sani Allah ya jarabbce ki da babban laifi kina addu'a Allah ya yafe miki. Ni dai mijin kine kuma bazan so wani abu maea kyau ya same ki ba. Ki sani abinda kikai min na yafe miki."

Mikewa yayi ya nufi hanyar fita. Baki ta tabe ta bi bayan sa.

"Kayi hakuri."
ta fada dai dai lokacin da zai shiga mota.

"Naji."
"Kaci abinci to?"

"No i am fasting."
"Sai ka dawo "

Ta fada tana shigewa ciki.

Kallon ta ya tsaya yi, ya girgiza kai, ya tada motar ya fice.

Gidan Su Ya nufa kai tsaye bangaren Dady ya nufa suka gaisa, Dady na zolayar sa  Ango Ango.

Shidai sai washe baki yake. Dady ya ce,
"Maman ka ta ce min wai da sumaiyya zaku tafi ko?"

"Eh!"
Ya bashi amsa.

"To Allah yasa albarka."
"Ameen Dady."

Momy ce ta shigo ta ce,
"A'ah Najib ne ya shigo."

"Eh Mami. Ina kwana?"
"Lafiya lou son ya sumaiyyan?"

"Tana lafiya tana gaishe ki"
"To muna amsawa."

Fita yayi, ya nufi bangaren Baba. Acan ya tadda su Talle zama sukai suna tsare tsaren yadda zasu bikin.

Ranar litinin za'a kawo Najwa, dan haka da yamma za ai dinner daga nan za a kai ta gidan ta.

"To amman kusan me?"
suka amsa da
"A'ah!"

"A daren ranar zamu tafi nida Sumaiyya."
"Ayyah Yaya ko kwana baza kai ba."

"Ba hali dan a friday suke son sauka ta gashi har na dada kwana biyu, kinga dole na tafi a ranar."

"Allah sarki, Allah ya kaimu toh."
"Ameen!"

Ya jima a gidan dan su yasa suyi masa kayan sha ruwa.

Inda in dare yayi, zai zo ya sha ruwa. Karfe shiga ya shigo gidan ana shan ruwa ya sha ruwa sannan ya tafi massalaci.

Sai bayan isha'i ya dawo ya ci abinda suka shirya masa.

Yam ball sukai masa, da kunun gyada sai kunu aya da sukai masa.

Da zai tafi suka bashi masa da lafiyayar miya da taji nama sosai

Sai karfe tara ya koma gida. Sumaiyya na zaune a falo tana jiran dawowar sa dan ta sa an shirya masa abinci me magun guna nan.

Sai dai tin magariba take zuba ido bashi ba alamun sa. Ko da ya dawo, kuma ya ce ya koshi.

Haushi kamar me dan sauran na kwana biyu in be ci ba ya kare. Washe gari ma tin safe da ya fita sai dare bayan ya je gida yaci abincin sa ya koshi. Tinda yasan Ba yi ma abincin take ba.

Shima da ya dawo haka ta kara tarar da abinci. Amman beci ba. Ranar karshe da kanta ta shirya masa da sassafe ta kai masa daki.

Dataga zai fita bashi ta saka masa a mota.

Ranar murna Najib zai ci abinci me magani dan boka yace inda yaci bazai kara tunanin wata Najwa ba.

To yana shiga office, ya tada mami tayi masa ta aiko masa da ita wannan yasa ya bada abincin dan sai da zai tafi ma aka bashi fulas din.

Kullun suna makale da Najwa a waya kusan yini suke tare dan duk inda zasu je kai invitation card tare suke yini waya ta ce sunje can ta ce suna can. Da Khaleel shi ya dinga zurga zurga da ita.

Tin daga ranar da Sumaiyya taga Najib yaci abinci, ya bata kara yunkurin masa girki ba.

Ranan tana zaune ya sa a dauke ta akai ta ai mata visa, murna gun Sumaiyya kamar me.

Kuma ita bata ga yana wani shirin biki ba. Wannan yasa ta kwantar da hankalin ta.

Su Mamin Najib kuwa ana can ana ta shirye shiryen biki haka su Talle tin ana sauran kwana biyu suka daga suka tafi kano.

    ***********
Alhamdulilah komai yana tafiya dai dai a bangaren su Najwa inda yau ranar labara har an mata gyaran jiki lalle da kunshi.

Tafito amaryar dai sosai, fadar irin kyau da cikar da ta kara ma vata lokaci ne.

Kyau iyakar kyau Najwa tayi shi, tana daki, ita da su Zahra da Khadija matar Khaleel. Sai talle da bara'atu da wasu daga cikin class mate din dinsu da suka zo.

Duk sun yi ankon wani material fari ne adon  ja. Ba karamin kyau sukai ba.

Gidan ya cika da jama'a dan Najwa tace kamun gida take so.

Tana daki me kwalliya na mata, wani dark pink colour material ta saka me stone ajiki, akai mata nadin head da wani dark pink colour abu.

Silver jaka da takalmu ta saka, gaskiya Najwa ba kowa ne ya gane ta ba.

Kowa ka gani fuskar sa kunshe da murmushi da farin ciki.

Karfe Biyar aka kama amarya a dakin Mamin ta. Inda daga nan aka fito da Amaraya harabar gidan ana kida da rawa.

An mata liki sosai taga yan uwa dan duk anzo.

Ganin jama'a kamar kasa yasa Najwa fashe wa da kuka.

Yan uwa kuwa kowa da gudun mawar sa. Mami ta samu kudi Najwa ma an bata gift daga kawayen ta.

Su Basma kuwa ana tsakiyar fili ana ta rawa.

Hamma Salim kuwa sai liki ake ana bikin Kanwa.

Kowa yaci ya sha ya koshi anyi taron ranar lafiya an tashi lafiya cikin farin ciki da annushuwa.

Anyi hotuna da vedios
Washe gari akai budar kai.

*INDABAWA*

Continue Reading

You'll Also Like

251K 20.4K 61
"Tun ina yarinya kike zagin mahaifiyata, tun bansan menene maanar kalmomin wulakanci da muzgunawa ba nakejin kina fadarsu ga mahaifiyata, ina cikin w...
907K 30.9K 110
When Grace returns home from college, it doesn't go like she thought it would. With her past still haunting her everyday choices, she discovers a sid...
44.9K 701 16
DELULU & GUILT PLEASURE
274K 38.5K 20
လက်တွေ့ဘဝနှင့် နီးစပ်ချင်ယောင်ဆောင်ခြင်း