NAJWA Complete ✔

MSIndabawa

59.4K 4.5K 9

Najib yaron littafin bai dda buri da aaddu'a sai ta Allah yaya bashi mace ta gari mai ilimi Sumaiyya Yarinya... Еще

1-5
11-15
16-20
21-25
26-30
31-35
36-40
41-45
46-50
51-55
61-65
66-70
71-75
76-80
81-85
86-90
91-95
96-100
101-105
106
107-110
111
113
114
115
116
117
118
119
120
121
122
123
124
126
127
128
129
130
131
132
133
135
136
137
138
139
140
141
142
143
144
145
146
147
148
149
150
151
152
153
154
155
156
157
158
159
160
161
162
163
164
165
166
167
168
168 End

125

591 59 0
MSIndabawa

*NAJWA*

🌐  *HAJOW*  🌐

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

By *MARYAM  S  INDABAWA*
*MANS*

DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*

*ALLAH YA SAKA MIKI DA GIDAN ALJANNA.*
*AMEEN*

PAGE *125*

Zaunar da Najwa tayi zatai mata kwalliya.
"A'ah Sis yimin simple ban son me yawa."

Wannan yasa tai mata jagira kawai sai dan man lebe da ta shafa mata."

Ya salam duk da batai kwalliya ba. Amman ba karamin kyau tayi ba.

Waya aka kira Zahra, dauka tayi, ta ce,
"Gasu ban."

Mayafan suka yafa, suka fita. tin daga nesa ya zubawa Zahra ido.

Najwa kuwa tsaki tayi, ta ce,
"Wallahi Mustapha ya fiya kallo."

Hararar ta Zahra tayi ta ce,
"Dadin ta kayan sa yake kalla."

"Au haka kika ce?"
"A'ah amman ai dadin ta ma bamu san yadda naki zai ba in ya ganki."

"Ba ruwan sa ai."
"Allah Sis irin wadan nan sun fi fitina."

"Ke gidan su. Yayan naki ne fitanan ne."
"A'ah yi hakuri Adda."

"Allah sarki har kin tunon da Basma ta. ina kewar ta wallahi."

Mustapha daya karaso wajen shi ya katse musu maganar da suke yi.

Durkusawa yayi yana cewa,
"Adda ina yini?"

Hararar sa tayi ta ce,
"Dan Allah ku daina mai dani tsohuwa."

"Anki din!"
Zahra ta fada. Duka ta kaima tana dariya.

Gaisawa sukayi, sannan suka matsa gefe suka zauna.

Mota ce, ta danno wajen da suke, kallo suka bi motar da yi banda  Najwa da ke danna wayar ta.

Najib ne ya fito daga motar sanye da  wandon jeans,  sai jar riga idon sa sanye da tabarau me garai garai.

Ba karamin kyau yayi ba, sai tashin kamshi yake.

Zahra ce ta rage murya tana fadawa Mustapha wani abu.

Da sauri Mustapha ya mike ya taro shi suna gaisawa.

Karasowa sukai suka gaisa da Zahra, Najwa ta nuna masa da hannun ta.

Kallon ta ya tsaya yi, da ido baki da hanci. duk ya rasa control din sa dan ya saka daina kallon ta.

Dariya Zahra tayi, ta ce, a ranta.
"Nagodewa Allah naga yadda zatayi da shi. Shima ga kallon nan."

Hannun sa Mustapha ya kama ya kai shi gefen ta.

Kamshin turaren da taji shi yasa ta dagowa da sauri.

Ido ta zaro ta mikewa a razane, kallon sa take da alamun kamar ta sanshi.

Shima hakan kokarin tino inda yasan ta yake.

Kai ya girgiza, tini ai ya dade da sanin ta ko na ganin ta da yake.

Itama kawar da tunanin tayi, a ranta ta ce,
"Kama ce."

Kasa tayi da kai, kallo ya bita dashi.

"Ina yini?"
ta gaisar dashi murya na rawa.

Kallon ta yayi, dan son tino inda ga taba jin muryar nan.

"Lafiya lou Najwa ya karatu."
"Lafiya Alhamdulilah."

Shiru tayi. Kallon ta ya tsaya yi kamar TV.

Kasa sakewa tayi kanta a kasa.
"Najwa Ina fatan kin aminta dani. Najwa ni me son kine, na jima da son ki a raina. Kece farin ciki na."

Duk rashin surutun Najib yau bakin sa yaki rufuwa.

Zuba yake mata bayanai yake a kan duk yadda yake son ta.

Ya kasa yin shiru, Najwa kuwa shiru tayi tana sauraron sa.

Duk yadda tayi tunanin sa yawuce nan.

Gaskiya ya mata, kuma daga maganar sa ma ta fuskanci, ko shi waye.

Da kyar ya barta dan kasa barin ta yayi.

Itama tin bayan rabuwar su, ta fada kogin tunanin sa.

Sun rabu da shi akan gobe zai zo yai musu sallama kafin ya tafi.

Washe gari karfe tara suka shiga jarabawa, inda sha daya har sun fito.

Suna fitowa suka hange sa daga jikin motar sa.

Kasa tayi da kanta, suka karasa gun sa.

Dan durkusawa tayi ta Gaida shi. Amsa wa yayi idon sa kyar akan ta.

Zahra ce, ta ce,
"Har ka fito kenan."

"Eh wallahi, nazo naga Baby na na wuce."
Fuska Najwa ta rufe da tafin hannun ta dan kunya.

"To shikenan ni bari naje, sai munyi waya Allah kiyaye hanya."
"Ameen Zahra Nagode fa "

"Ba komai."
ta fada tana yin gaba

Kallon sa ya komar dashi kan Najwa.
"Baby nah!"

Shiru tayi,
"Toh! ni zan tafi, sai munyi waya."

Muryar ta yajiyo me dadi da sanyi tana masa addu'a.
"To Allah kiyaye hanya Allah kai ka ya dawo da kai  lafiya. Allah tsare."

Kallon ta ya tsaya yi, yana ta amsawa daa
"Ameen Ameen!"

Shiga yayi ta rufe masa kofa tana daga masa hannu.

Sai da taga tafiyar sa, sannan ta nufi hanyar hostel.

Zahra na ganin ta fara yin dariya ta ce,
"Baby ya soyayya."

Duka takai mata, ta ce,
"Bana so."

Kayan su suka hada, suka debo aka saka a motar gidan su.

Lokacin suka tafi gidan Mami har ta hada musu kayan abinci kala kala.

Wanka sukai sannan suka zauna, cin abinci.

Kwanciyya Najwa tayi dan yin bacci. Tinawa tayi da Najib wannan yasa ta dauki wayar ta, ta tura masa sako me dadi.

Yana sauka yaji karar wayar sa, dauka yayi, sakon Najwa ya gani.

Wani murmushi ne ya sauka akan fuskar sa wanda besan lokacin da ya fita ba.

Gidan Mami ya fara sauka dan ya samu abinda zai ci ya huta kuma.

Yana shiga yai wanka sannan ya ci abinci.

Bangaren sa na da ya shiga, ya kwanta bashi ya tashi ba sai yamma.

Lokacin ya kuma ganin wani text din nata.

Mamaki ne ya lullube shi, ganin Sumaiyya da take matar sa ma bata damu dashi haka ba.

In ya tafi in har be kirata ba, to baza ta taba kiran sa ba.

Sumaiyya duk abinda take so, Najib na mata shi. Kudi kuwa kamar me kullun zai dire mata.

Abunda yake hada shi da Sumaiyya shine rashin son yin aiki. Bazata taba gyara waje ba.

Haka nan bata son kitso, jikin ta dai zatai wanka sau da a rana, tai kwalliya amman kanta ba ya samun gyara sai ta gadama zataje saloon a tsefe a wanke a sake wani.

Sai rashin girki sam bazata masa girki ba. Duk yadda yake da son abinci amman baya samu dan in ya dawo sai dai ya samu abu me sauki ya dafa ya ci.

Bangaren sa kuwa zai iya cewa bata shiga sau biyar ba. Bare taga ya baci ta gyara masa ma.

Ga rashin kula, wai taga yayi dare ko yai tafiya ta kira sam babu wannan.

Sai dai in tana neman wani abu ne. Abin na damun sa.

Gashi wai safiyya tayi ta gaishe shi ya dawo daga aiki a tarbe shi ko ai masa sannu da zuwa duk bazai samu ba.

Be taba ganin ta da Alkur'ani ba bare yaji tana karatawa.

Shi da yake son mace me addini sai gashi Allah ya hada shi da Sumaiyya.

To ya godewa Allah kuma a koda yaushe yana mata addu'ar shiriya.

Har a isilamiyya ya saka ta amman bazai ce ta taba zuwa ba.

Ga rashin Sallah akan lokaci. Gashi bata son zuwa gaida su Mami. In yace yazo suje sai ta kawo wani abun.

*INDABAWA*

Продолжить чтение

Вам также понравится

Unforgettable Days(A Hausa Story) Hussainaa

Любовные романы

9.3K 104 1
Khairiyya was lost and couldn't think of a perfect solution to what happened. At last she decided to keep it a secret forever without telling anyone...
MADINAH MSHAKURworld

Любовные романы

53.4K 1.9K 12
Just walk in and read, I promise u are going to be mesmerize with the emotional love story embedded in this novel.
CAPTAIN MUZAMMIL Asma'u Usman

Художественная проза

47.1K 4.3K 77
The life of a Soldier
Bintun Batuul Ta masu gari

Художественная проза

2.7K 238 15
Saboda yadda mahaifin mu ya din ga saka Mana suna Fatima, har se da nayi tunanin ko Muna da alaka da shi'a ne, saboda Naga yawancin sune mutanen da k...