NAJWA Complete ✔

Oleh MSIndabawa

59.5K 4.5K 9

Najib yaron littafin bai dda buri da aaddu'a sai ta Allah yaya bashi mace ta gari mai ilimi Sumaiyya Yarinya... Lebih Banyak

1-5
11-15
16-20
21-25
26-30
31-35
36-40
41-45
46-50
51-55
61-65
66-70
71-75
76-80
81-85
86-90
91-95
96-100
101-105
106
107-110
111
113
114
115
116
117
118
119
120
121
123
124
125
126
127
128
129
130
131
132
133
135
136
137
138
139
140
141
142
143
144
145
146
147
148
149
150
151
152
153
154
155
156
157
158
159
160
161
162
163
164
165
166
167
168
168 End

122

556 57 0
Oleh MSIndabawa

*NAJWA*

🌐  *HAJOW*  🌐

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

By *MARYAM  S  INDABAWA*
*MANS*

DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH
*ALLAH YA SAKA MIKI DA GIDAN ALJANNA.*
*AMEEN*

PAGE *122*


*Kuyi hakuri kwana biyu page daya nake turowa. Wamnan yasamu ne saboda bana samun lokaci ssai.*

*Anayin maneji*

*Masoya littafin  nan. Naga sako nagode. Allaah barmu tare*

Ranar sai dare suka bar gidan.

Mami kuwa sai nan nan take da ita.

Ko da yaje Kano damuwar rashin ganin ta bata bar shi ya sake ba.

Dan duk a matse ya ke. yaje gidan Khaleel inda kulawar da yaga Khadija na bashi ba karamin burge shi tayi ba.

Duk da tana da ciki bata da kasala da kwiya. dan gidan tsab dashi abin sha'awa sai tashin kamshi yake.

Yana zuwa aka tare shi da abinci me rai da lafiya ga hadin lemo.

Sosai yaci abincin dan Najib baya wasa da cikin sa.

Ba yadda Khaleel beyi dashi ya kwana a gidan ba yaki.

Zuwan sa Kano yayi ziyara yan uwan da kakanin sa. Inda suke ta masa tsiya be kawo amaryar sa ba.

Wanda ya dade be ganshi bama wannan karan yaje ya yi musu abin arziki.

Ana jibi zai dawo ya fadawa Mami, Mami ganin yar aikin da zata kaiwa Sumaiyya bata zo ba. Tasa su Najwa suka tattara suka tafi gidan Summy dan su taya ta tarbar me gida.

Tunda suka je take cika tana batsewa su kuwa ko ta kanta basu bi ba.

Inda sai hirar su suke, su dafa abinda suke so, su sha abinda suke so.

Duk da abin na mata zafi amman tasan baza ta iya hanasu ba.

Ranar da zai dawo ba ta tashi a bacci ba ma sai karfe Ukun rana.

Lokacin sun gyare gidan tsab sun turare shi.

Najwa da Zahra ne suka gyara bangaren Najib.

Inda suka ce Najwa ita zata Masa girki. Fried rice tayi da hadin salad sai waina masa da yake su Bara'atu su  fada mata yana son ta.

Sai farfesun kayan ciki da tayi masa da hadin lemoka da kunun aya.

Kafin magariba sun gama komai gida sai tashin amshi yake.

Sun shirya zasu tafi Najwa tayi bangaren sa ta hada masa ruwan wanka dan tasan i yanzu dai yana hanya.

Tana dawowa suka shige mota. Jeep ce wannan yasa Najwa ta shige can baya, su kuma suka zauna a tsakiya.

Har an bude musu gate zasu fita ya danno hancin motar sa cikin gidan.

Tsayawa Drivern su yayi har sai da ya fito suka gaisa.

Karasowa yayi wajen motar yana leka kansa ta taga.

Bara'atu ce ta ce,
"Sannu da zuwa Yaya. Ya hanya?"

"Lafiya ya amsa mata da. Gaisar dashi sukai gaba dayan su.

Sai da suka gama sannan Najwa ta ce,
"Ina yini Hamma Najib?"

Tsigar jikin sa ce ta mike, jin muryar ta me dadi da sanyi ta doke shi.

Amsawa yayi yana son ganin fuskar ta. Duk da yaso yasan muryar tata.

Ganin zasu fita ne yasa ya barsu kaf ya tsaida su.

Bangaren sa ya nufa dan watsa ruwa. Yana shiga da gajiya ya tadda an hada masa ruwa.

Murmushi yayi a ransa dan yasan ba Summy ce da wannan aikin ba.

Dan tin daga harabar gidan yaga canji kuma yasan Mami ita ta aiko su dan su dan yi masa gyara.

Wankan yayi cikin farin ciki dan ruwan sai kamshi yake masa.

Sai da ya shirya ya nufi bangaren ta.

Tana zaune tana sana'ar tata ta kallo, tin wankan safe vata karayi ba.

Fuskarta sai maiko take yi. A gefen ta ya zauna.

Kallon ta yayi, itama haka dan tayi kewar sa.

Mamakin ta yake, bako sannu da zuwa bare ai masa ya hanya.

"Ya gidan?"
Shiya tambaye ta.

"Lafiya? Ya kake?"
Mikewa yayi be bata amsa ba.

Dan ba wannan abin ya kamata ya fito daga bakin ta ba.

Daining ya nufa, Fulas din dake daining din su kansu abin kalla ne.

Be taba ganin su a gidan ba, to ita da ba girkin take ba tayaya zai gansu.

Fulas Fulas din ya bude wani kamshi je ya doki hancin sa.

Masa ce an mata miyar nama miyar kanta abar a ce banda wani kamshi da take fitar wa.

Yawu ya hadiya. Zubawa yayi ya fara ci. Ji yayi kunnen sa kamar zai cire dan dadi.

Abincin yake ci cikin kwanciyar hankali a ransa ya a cewa wannan ba girkin su Bara'atu bane.

Summy kuwa kamshin girkin shi ya taso ta daga kallo  da take, dan ita ma sai taji yunwa.

Fried Rice din ta zuba ta fara ci kai ta fara gyadawa dan dadin girkin.

Yana gamawa da masar ya dauka ya saka a friji haka ma fried rice din.

Falo ya koma ya zauna biyo shi tayi ta zauna akan cinyar sa.

Kirjin ta, ta manna da nashi, tini hankalin sa ya tashi.
Romancing junan su suka fara daga nan ya dauke ta cak yayi dakin baccin sa da ita.

Su Najwa na komawa gida suka fara hada kayan su dan monday zasu fara lecturer.

Mami duk ba dadi taji, amman ya zatayi, goma ta arziki ta hada musu inda tasa a nema musu jirgi dan gobe suke son dira a kano jibi su wucce Katsina.

Gata kuma sai makaranta. Dady ma sai da ya basu kudi me yawa har airport suka raka su. Sai da suka ga tashin sanan suka juyo.

A kano ma suna dira har an zo daukar su. Mamin Najwa da murna ta tare su.

Inda da yamma ta kaisu shopping da kanta daga nan zooroad suka wuce ta karbo kusu dinkunan su.

Da dare kuma sukaje yiwa kakannin su sallama.

Kowa sukaje sai dai ya sanya musu albarka tare da addu'a.

Washe gari suka mika Katsina. Inda acan ma sai kewar su ake yi.

*Bayan Wata Biyu*

Karatu yayi nisa dan har sun kusa fara jarabawa first semester level three.

Komai lafiya yake tafiyar musu, inda har lokacin Najwa bata kula wani bare har ta tsaya da su.

Mami tini ta aika wa su Najib da yar aiki. Duk rashin son yar aiki da bayayi.

To yaya zaiyi sai yanzu ya gane daman can Sumaiyya kazama ce bata damu da ganin datti ta gyara wajen ba.

Haka nan girki ba iyawa tayi ba. Wannan yasa sai ya dawo da dare yake girka abinda zai ci.

Dan shi bazai iya cin abincin waje da na masu aiki ba.

Ita kuwa wani sabon san jiki ne ya same ta dan wanka ma da kyar take iya yi kullum yini take kallo sai chatting da kawaye.

Katsina ya kara shiryawa zuwa, wannan zuwan ba karamin addu'ar yayi na Allah ya hada shi da ita ba.

Tin da ya dira ya fara jin kwarin gwiwa wannan yasa yai wanka ya shirta ya fita.

Su Najwa kuwa sun koma hostel saboda jarabawar da suka fara.

Bikin wata mate din su za'a yi wannan yasa suka shirya zuwa Green house dan siya  mayafan da zasu amfani da shi.

Kamar hadin baki shima ya shirya ya tafi store din dan siyan abubuwan da zai danyi amfani dasu.

Shigar su kenan shima ya iso wajen, ciki shima ya shiga ya fara daukar abinda yake so.

Sai da ya gama tsab sannan ya nufi wajen biyan kudin.

Kamar daga sama ya hango ta tsaye a gun tana biyan kudin.

Kallon ta ya tsaya yi sosai, ganin zai kara rasa damar sa yasa ya ajiye kayan ya bi bayan su.

Motar da suka shiga yabi baya, a hankali a hankali har suka  karasa bakin gate din makarantar su.

Bin su ya cigaba dayi har suka karasa bakin hostel din su. Sai da suka shiga sannan ya samu wasu yan mata ya ce,
"Dan Allah yan matan can neke son ku kira min."

Kai yarinyar ta jinjina kai ta ce,
"Allah yasa su zo, dan basa kula samari."

Ta fada tana yin cikin dakin nasu.


*INDABAWA*

Lanjutkan Membaca

Kamu Akan Menyukai Ini

255K 10.1K 32
""SIT THERE AND TAKE IT LIKE A GOOD GIRL"" YOU,DIRTY,DIRTY GIRL ,I WAS TALKING ABOUT THE BOOK🌝🌚
44.6K 701 16
DELULU & GUILT PLEASURE
251K 20.3K 61
"Tun ina yarinya kike zagin mahaifiyata, tun bansan menene maanar kalmomin wulakanci da muzgunawa ba nakejin kina fadarsu ga mahaifiyata, ina cikin w...
109K 7.8K 38
Tace "ke ni kin isheni, kin saka ni a duhu, me kike nufi da waďannan zantukan? Nace "kin sha faďa mini yadda mace ke gane tana ďauke da ciki da ya...