NAJWA Complete ✔

By MSIndabawa

59.6K 4.5K 9

Najib yaron littafin bai dda buri da aaddu'a sai ta Allah yaya bashi mace ta gari mai ilimi Sumaiyya Yarinya... More

1-5
11-15
16-20
21-25
26-30
31-35
36-40
41-45
46-50
51-55
61-65
66-70
71-75
76-80
81-85
86-90
91-95
96-100
101-105
106
107-110
111
113
114
115
117
118
119
120
121
122
123
124
125
126
127
128
129
130
131
132
133
135
136
137
138
139
140
141
142
143
144
145
146
147
148
149
150
151
152
153
154
155
156
157
158
159
160
161
162
163
164
165
166
167
168
168 End

116

546 52 0
By MSIndabawa

*NAJWA*

🌐  *HAJOW*  🌐

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITER'S*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

By *MARYAM  S  INDABAWA*
*MANS*

DEDICATED TO *RASHIDA A KARDAM*
*AUNTY RASH*

*ALLAH YA SAKA MIKI DA GIDAN ALJANNA.*
*AMEEN*

PAGE *116*

Momy har tayi fadan amman Sam Najwa bata iya tsayawa da kowa.

Mutum daya ne ya na ce mata shine dan gidan kawar Momy duk rashin kulawar da take masa amman sam shi ya kasa hakura da ita.

Tin da ta bashi hakuri tare da hada shi da Allah akan ya tabu da ita yaki. Yasa ko ya zo bata zuwa bare ya ganta.


Ba laifi yana dan kiran ta su gaisa ya tambayi su Mama daga haka ba abinda yake daduwa.

Haka nan duk wata yana aikiwa Khaleel da kudi tayi amfani dasu.

Mama ceta, ta kurawa Sumaiyya kan ta fito da miji wannan yasa ta fadawa Khaleel dan ita yana jin nauyin Najib.

Khaleel ya kira Najib ya fada masa komai. Ba komai ya ce masa akan zai fadawa Dadyn sa ayi komai da an dawo ayi bikin.

Ba karamin dadi Khaleel yaji ba inda suka shirya zasu bikin su gaba daya.

Dady Najib ya fara ya fada masa, komai Dady yayi ji dadi da farin ciki bama Mami da ta fara hada lefe tin lokacin da ta samu labari.

Kafin ya dawo aka saka rana wata biyar. inda da ya dawo za'a sha shagalin biki.

Aiki aka dauke shi a can na shekara abinda ya hanashi dawowa kenan.

Najib yana can duk abinda ya gani na mata sai ya siyo ba Sumaiyya yake siyowa ba. Illa Yarinyar da ta zame masa jinin jikin sa. Yarinyar da be san ta ba. Sai gani sau biyu da yayi mata.

Cikin ikon Allah har ya kammala abinda ya kai ya fara shirye shiryen dawowa.

Mami ba karamin murnar dawowar sa tayi ba  dan ya kara kyau da girma ya zama cikaken namiji me kamala

Ranar da ya dawo ranar aka kai lefen sa gida Su summy. Summy kuwa murna kamar tayi me.

Khaleel yazo suka shirya abubuwan da za'a yi dan sati biyu aka saka za'ayi bikin sa.

Kati suke kaiwa wanna yasa ba zama tinda ya dawo dan ma abokan nasu daya ne

Wannan yasa suka raba wanan yayi can wancan yayi can.

Katsina ya tafi dan kaiwa abokin mahaifinsa, kati wato mahaifin Zahra.

Yaje lafiya inda Momy ta tarbe shi hannu bibiyu, ya ci ya sha. Duk yadda suka so ya kwana ki yayi. Dan ya ce akwai inada zai je a ranar ma.

Sallama yayi musu ya fita, gidan wani abokinsa ya nufa dan kai masa kati tare da yi wa matar sa barka ta haihu.

Har ya nufi hayar gidan ya tuna be siyo musu komai ha. Wanna yasa ya juyar da motar sa ya nufi. Green House dan siyawa Baby kaya.

Yau Dady ya basu kudi wannan yasa tin safe da suka fita har yamma basu dawo ba dan daga kasuwa suka tafi Can green house dan siyar wasu kaya da zasuyi.

Sun gama siyayar su sun fito, suna cikin mota za'a tayar kenan ya karaso gun a motar  sa.

Ajiye motar sa yayi ya fito ya nufi cikin wajen kiran sa akayi yana juyawa yaga wani abokin sa da sukayi karatu tare komawa yayi suna gaisawa kamar ance ya kalli gefen sa ya hango ta a cikin mota kallon ta ya tsaya yi dan ya tabbatar  da ko ita ce.

ido ya mutsuke ya kara kallon su lokacin da suka hau kan titi. Kafin yayi wani yunkuri har sun bacewa ganin sa.

Dafa shi abokin nasa yayi ya ce
"Tafiya?"

Kai ya gyada ya ce,
"Wallahi wata yarinya da nake nema ce ta kuma har sun tafi."

"Ko dai da ita za ayi ne."
Murmushi yayi ya bude motar sa ya dauko masa kati ga katin bikina nan.

Sukai sallama ya shiga yayi siyayyar da zai yi ya fito.

Ya dade yana mamaki dan yana tunanin ko idon sa ne amman me zai kawo yarinyar nan garin.

Da wannan ne ya samu hankalin sa ya dan kwanta.

Dan sai ya dinga tunanin ko gizo idon sa ke masa.

Amman yagi alkawarin zai zi ya neme ta.

A ranar ya wuce kano be koma abuja ba har aka daura aure.
Mami taso Najwa  tazo amman lokacin sun fara jarabawar second semester wannan yasa duk yan uwa sai tambayar ta suke. Duk da daman bata saba shiga cikin su ba.

Basuyi wani event ba sai a Abuja da suka hada dinner.

Summy ko kukan barin gida ha tayi ba.

Tin karfe biyu suka tafi kai amarya, inda da magariba aka tafi yin dinner.

Zan iya cewa tin da ya dawo sau daya suka hadu sai ranar dinner Khaleel.

Amman Summy bata kawo komai a ranta ba. Shi kuwa duk abin nan hankalin sa ya tafi kan Yarinyar da yake yawan gani.

Gidan Najib katon guda ne wanda masu ginin ma daga waje aka dauko su.

Gida ne wanda ya tsari dashi abin sha'awa.

An zuba wa summy kayan alfarma da kyau a bangaren ta.

Bangaren sa kuwa shi ya zuba duk abinda yake bukata sai dayan site din da yake a rufe.

Dakin bacci uku ne sai falo guda biyu da kitchen da ban daki a bangaren summy.

An shirya mata wajen nata sosai. Inda daga gun dinner aka kai ta dakin ta.

Tare da yan uwan ta suka kwana dan sai gobe zasu tafi.

Wasje gari da safe Mami ta aika musu da abincin da tayo musu ba abinda ba a aiko musu ba.

Haka nan duk wanda yazo sai da aka bashi kudi da turnin atamfa  banda kayan rabo na biki da aka hada musu.

Suna gamawa suka fara shirin tafiya. Inda Mamin Najwa da ta kwana a gida mami tazo ta yiwa Summy fada kan ta kula da mijin ta.

Yan uwan ta duk suka tafi, Mami ce ta aika mata da Bara'atu da Talle dan su tayata zama kafin anjima Najib ya tafi.

Tunda mutanen da suka kawo ta suka tafi ba abinda tayi ko dan karkade karkaden nan batayi ba.

Sai kwanciyya ma da tayi, ko da su Talle su kaje gidan duk sallamar da  suke bata amsa musu ba saboda baccin da take yi.

Gidan suka kara share mata tare da goge shi tas suka turareshi sai tashin kamshi yake.

Abincun ranar da Mami ta basu su kawo suka jere mata a dining sannab suka zauna suna kallo.

Sam bazaka taba kallon su kace masu aiki bane dan kyawawa ne ga tsafta ga ado. dan Mami duk wata sai ta kaisu siyayya tare da kaisu gyaran kai.

Wannan ya kara dada fito musu da kyan su. In ka kalle su sai ka  zaci ya'yan wani attajiri ne.

Ga makaranta da suke yanzu haka suna SS2 makarantar da suke ita kanta sai ya'yan wane da wane.

Najib shi ya sa su dan yanajin yaran kamar kannen sa dan yana son kakarsu ya dauke ta kamar kakarsa.

Ya horar da yara da tsafta kamar yadda Mami ta horar dashi.

Haka nan ya koya musu jan aji da nutsuwa dan ya tsani mutumin da be da nutsuwa.

Duk abinda ya daura su akai sun dauke wannan yasa suke burge su

Samari dayawa na kawo musu hari,  amman sam basa kula su. Dan ko a abokan Najib din ma akwai masu son su da yawa.

Sai da yace su bari su gama secondary tukunna.

*INDABAWA*

Continue Reading

You'll Also Like

16.2K 859 71
'Ammi ya zan yi da rayuwata? Ya kuke so in yi da zuciyata? Ban taba ba...daidai da rana daya ban taba mafarkin yin rayuwar aure ba tare da Ameer ba...
37.8K 738 10
A girl that was raised by a single Mum, she's a Baker, a henna designer meet the love of her life, but In between their love lies another love, what...
10.2K 591 13
Hamida was an ordinary girl trying to fit in, into the world entirely. after the death of her father, she and her mother moved in to stay with her Un...
47.2K 4.3K 77
The life of a Soldier