MASIFAFFAN NAMIJI..!

By JamilaUmar315

54.1K 4.3K 635

A mu"amalansa da kowa Sai son Barka....Kowa kuma zai iya Fadin kyakyawan Hallayarsa..Ammh ga Matarsa Hafsah b... More

01
002
008
009
012
010
011
013
015
016
017
018
027
03
019
020
021
022
023
033
024
036
025
026
04
034
028
029
005
030
031
032
037
038
06
035
040
039
FINALE
007

014

1.1K 116 6
By JamilaUmar315

*MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*DEDICATED TO:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!

_Shafin yau Gabadayansa Sadaukarwa ne zuwa Gareki *MY BEST❤️HALIMA..* ALHERIN ALLAH YA KAI MIKI ADUK INDA KIKE AMEEN..._

*014*


"Falon babu Kowa sai karan Talabijin Daya ketayi Shi kadai...Kwata kwata Babu motsin kowa Cikin mamaki Dukkansu suke Bin Falon da kallo ganinsa kaca kaca da alama dai matar Gidan bata Dubashi ba.

Saman Center Table din Dake Tsakiyar Falon Ga Filet nan da kofuna da kuma Goran ruwa da lemo Wanda da alamu Harda wanda akayi amfani Dashi Jiya da Daddare dana yau da Safe, kila da megidan zai Fita ne,ya Taimaki kanshi.

Suna Ta Raba ido Cikin Falon,Subai Ta kalli Hafsah tana Fadin"Ke wai matar gidan kuwa tana nan..? Hafsah tace"Tana nan mana..Da bata nan da batace tana nan ba kinsan tace batajin Dadi kila Tana ciki ne.."Mariya ce Ta kara bude baki ta kwarara Sallama sai ga Sakina ta Bude wata Kofa dake yammah haka ta Fito Dagani Daga barci tatashi Domin Rigar barci ce ajikinta mai igiyoyi,Sai wata Hula Dake saman kanta Fuskarta Duk ta yamutse Alamun dai Tun barcin Jiya bata iya Tashi ba sai yanzu.

Da Mirmishi ta Tarbesu Lokaci Daya tana karisowa kusa dasu Cikin Fara"a tace"Sannun ku da zuwa..ku zauna Ashe Kun kariso...?Hafsah tace"Eh wlh..Muna Ta sallama muka ji Shuru..? Ta fada tana zama kan Daya Daga Cikin kujerun da sukayi ma Falon kwanya,Suma su Subai"atu da mariya da Jidda Hade da Inna Talatu suka nemi waje suka Zauna,Lokaci Daya suna gaisheta ta amsa Tana kallon Inna Talatu ganinta Babba yaasa ta gaisheta ita kuma ta amsa Tana Tambayanta gida da yara.

Mirmishi Sakina tayi batayi mgana ba Hafsah ce tace"Wasu yaran Inna..? Wadanan yan Boko ne yara ba yanzu ba.."Inna Talatu tace"Ikon Allah daman Haihuwan Tsarata ake sai sonda Mutum yaga dama..? Kai yaran zamani.."Tafada tana kyabe baki Dariya suka sakamata Harda Sakinan Subai ce tace"Inna baki gane ba..Ba yanzu suke Bukatar ya'yan ba sai zuwa Gaba.."Inna Talatu ta tabe baki Tana Fadin"Aikin Banza ai Duk wannan Shirme ne da Biyema ka"idan Yahudawa Annabi da kansa yace kuyi Aure ku Haiyayyafa sai nayi alfahari Daku Ranar lahira ammh ku kuma kuna ma Tsara Lokacin da zaku samu ya"yan ne Allah ya kyauta To.."suka kara sakamata Dariya saboda sanin Halin Inna Talatu na barkwanci da kuma Ban Dariya.

Sakina dai batayi mgana ba, sai Mirmishi sai chan ne,Hafsah ta kalleta tace"Kanwar Mama ce muna ce mata Inna Talatu.."Yake tayi Tana Fadin Allah sarki Kafin Hafsah ta Nuna Subai tana Fadin"Nasan baki santa ba Ita ke bima Zannira sunanta Subai"atu azaria take aure..su Mariya kuma nasan kila kin ganesu..? Sakina ta kallesu Daya bayan Daya kafin tace"Allah Sarki..Sannunku da zuwa.."Suka amsa da yauwa Subai"atu dai nata yan kalle kalle Tana Tabe baki Sakinar na Lura da ita,sai itama ta Dauke kanta ta Mike tana Fadin"Bari na kawo muku Ruwa...kunzo ban lahiya banyi komai Cikin Gidan ba.."

Hafsah tace"Ayyah bakomai da kin barsa ma munsha Ruwa saman Hanya muke.."Bata saurareta ba tawuce zuwa Kitchen suka Bita da kallo ganin yadda take wani taku ta kowani Kira na Jikinta yana amsawa Baki Subai ta Rike tana Fadin"Ji wai macen Aure..? Ji gidanta..?gaskiya Ya Nazifi kyan jiki kawai yabi da Dukiyar mahaifinta ammh banda haka wlh banga Abun so anan ba.."Hafsah ta Take mata kafa tana kyafta mata ido Mariya nata Dariya Inna Talatu dai bata saka musu baki ba Domin Itama Sakinar bata bata Sha"awa ba sam..

Ruwa da Lemo ta kawomusu da Kofuna kana ta koma ta Cikin Bedroom dinta ta Dauko wayarta tazo ta zauna ta Dora kafa daya Kan Daya tana latsawa Subai kuwa sai Binta da kallo take awulakance,ganin basu sha Ruwan ba yasa Sakinar ta kallesu Tana Fadin"Kun ki shan Ruwa..? Hafsah tace"Zamu sha..Dayake kinga Daga gidan zannira muke bamu tare da kishi.."Itace tasha Ruwan sai Inna Talatu Subai da Mariya da Jidda ba wanda yasha,Sunanan zaune sau Daya Sakinar ta Dago tana Tambayan Hafsah yasu Amira..? Tace suna Lafiya suna Gidan Ammi.

Sunyi zaman mintuna Talatin kana Subai ta kalli Hafsah tana Fadin"Muyi Harama ko..?12 ta wuce kada muyi Dare Bisa Hanya.."Tafada tana mikewa Lokaci Daya tana Gyara zaman Saleem Dake Hannunta,suma Duk sai suka mike suna Fadin"Ai kuwa Toh sakina mu zamu wuce.."Cewar Hafsah sai Lokacin Sakina ta ijiye wayarta tana Fadin"Tun yanzu..?

Hafsah tace"Muna Bisa Hanya ne..Zaria zamu koma.."Sakina tace'Ai nagode..Ku gaida gida Allah kiyaye Hanya mungode.."Subai ce tace"Toh in yaya Nazifin ya dawo sai agayamai mun zo..Allah kara lafiya.."Sakinar ta karba da Ameen Fuskarta ba Fara"a Sosai iyakarta Rakiyarsu bakin kofar Falonta ta koma Subai bata Samu Bakin mgana ba sai da suka Dauki Hanya kana ta kalli Hafsah Tana Fadin"Gaskiya matar nan ta Ya Nazifi bata da Kirki..Duk Fadin Rashin kirkinta dasu Zakiyyah ke Fadi ban yarda ba sai yau Dana ganta.."

Hafsah tayi Dariya tana Fadin"Wai ina Ruwanki da Rashin Kirkinta..? Matar nan kin Cika gulma.."Subai tace'"Allah ba Zencen gulma ba sai gaskiya Shiyasa ba"a son Dogon Buri,kinga da Lokacin da zai yi Aure yabi yadda Sunna ta koyar mai addini da Tarbiya Shi kuma sai yabi Mai kyan Diri da kuma Tarin Dukiya Shiysa Tunda yayi Aure yake ta kwarewa kamar kudin Guzuri.."Dariya ta kama Mariya da Hafsah suka kyakyalce da Dariya Jidda dai Tabe kawai Tayi Dayake ita ke gidan Gaba.

Mariya ce tace"Haka ake ta Gulma a anguwa ana Fadin Auran kudi yayi Gashi kuma ya Auro ma kansa wacce tafi karfinsa kwanaki Mama naji suna mganar da Ya Abdullahi Da suka samu matsala ya Taba marinta ta koma Gida Babanta ya Kira Baba wada yace wlh sai yamaka ya Nazifi a kotu Baba wada yace Abun bai kai nan ba,Ya Kira ya Abdullahi yace maza ya Raka Shi Ya Nazifin  suje suyi ban Hakuri wanda ya jawo Ruwa ya Dakesa Shi kadai da Mutumcinsa bazai bari Nazifi ya maidashi Mutumin banza ba.."

Salati Subai ta saka ta na mamaki kafin tayi mgana Hafsah tace"kwarai kuwa Kwanaki sunje kano..Shida Abban Amira ammh kusan Halin yayanku Wlh ko Tadin bai taba yi Dani ba.."Mariya tace"Tabdijam Wake jin Zence abakin Ya Abdullahi in banda Mama..? Ko nima Ranar bai san ina Ciki bane Ina ma Mama gyaran Daki Dana Fito muka Hada ido kinga Ruwan Harara..?Dariya suka sakamata Lokaci Daya Subai tace"Da farko Haushinsa nakeji ina mai Allah kara ammh yanzu ya koma Bani Tsausayi Wlh inda ina da Diya Budurwa sai na wanketa na bashu Naga yarda Shegiya zata kare sai taje ta Rungumi aikinta Ubanta kuma sai ya maye mata Gurbin Nazifin..'

Hafsah ta Rike baki Tana Fadin"Lalle lamarin Babba ne..Ai bata baci ba ga Muhsina sai ya Jirata in ta kara Girma muyi Tuwona maina.."Duka Subai ta Daka mata abaya Tana Dariya Mariya na Tayasu Jidda kuma daman bata Cika saka musu baki ba in suna mgana Inna Talatu kuma taji sanyin A.C mota Tuni Barci ya saceta,Mariya ce ke Tayasu Da Dariya Dayake ita akwai manyance,Bus stop suka ijiye Mariya ta Hau adaidaita ta koma Bayan sunyi Sallama nan suka Barta tana neman Abun hawa.

Suna Tafe suna Hira gwanin Sha"awa Suna gabda Shigowa Zaria Subai tace"Jidda wai yaushe ne,Bikin autar Goggo Habiba ne..? Jidda tace"Wlh na manta ammh fa an kusa kamar naji Mama suna mgana da ita datazo mata Barkan Anty Zannira Tace watan Gobe ne.."Hafsah tace"Kai Abun har yazo..kamar fa Shekara aka saka ko..?

Subai tace"Eh mana nima nayi mamaki..Komai aka sakama Lokaci sai yazo lalle kice Danja zatayi Diban baki.."Hafsah tace"Aifa..Allah dai ya kaimu.."Jiddaa tace"Kafin na Madina din wannan Asabar din Diyar mijinta na Aure fa Shiyasa ma Tace ma Mama bazata samu zuwa Kaduna ba Tadai Kira Anty Zanniran ta mata barka.."Hafsah tace"Allah sarki..yakamata kuma ama Goggo kara kowani Sha"ani Da ita da ya"yanta akeyi.."

Subai tace"Sai Ya Abdullahi ya wakilataki kije Qawata.."Hafsah tace"Wa..? Rufamin Asiri ina Lallaba yan kayana yanzu ma Baku san Abunda zan Tarar ba na Tsiya.."Ta fada tana Dariya Dayake ta basu labarin yadda ya Barta ta Taho Tunda Ranar da sukazo da Daddare Umman Sadiq ta Kirata tana Tambayanta ko ya Kirata yace tatafi sai tace gatama akaduna.

Basu iso Zaria ba sai Wajen Biyu na Rana Dayake basu yi Gudu ba Gidan Mama Tawagar Sunan ta yada Zango suka bama Mama sakonta ita kuma tayi ta Hamdalan Sun dawo lafiya daya suka baro masu wanka sukace Lafiyarsu kalau suna gaisheta Dama koda suka iso Mama tayi Danwakenta da yajinta da manja nan suka baje sukaci suka Koshi suka Dora da Ruwa kana aka Zauna zaman Hira Bayan sunyi Sallar azahar.

Cikin Hiran ne Subai ke Fadin"Mama Ashe haka Matar Ya Nazifin nan take mara Mutumci..?Mama tace"Ho ke Subai"atu ina kika ganta kuma..? Nan mariya ke gayama Mama Yadda akayi Mama tayi Dariya Tana Fadin"Hoho..Subai kina nan da Halinki..Ina Ruwanki da Rashin Kirkinta Tunda Mijinta yaji kuma yagani.."Subai tace"Mama bawan Allah ya koma Abun Tsausayi.."Hafsah tace"Don Allah mu ki kyalemu da wannan mganar in baza ki iya gani ki kyale ba ki barshi.."Hararanta Subai tayi Daganan bata kara Mgana ba ammh haka Kurum take jin Haushin Sakina acikin Ranta.

Sai Da sukayi La"asar kana Kowa tayi Shirin komawa Gida kafin su Tafi sai Da Mama ta saka Suka Shiga Gidan Inna Abu ita da Subai suka kaimata Sakon Naman Sunanta da Turmin zanin Sakon Zannira ta karba tana ta Godiya ta sakamusu albarka suna gidan ma sai ga Baba ya Shigo nan Inna Abu ke gwadamai  Shima yayi ta Godiya yana saka musu albarka kana suka musu Sallama suka Fito Direban Mijin Subai Shi ya Fara kai Hafsah Gida kana ya wuce da ita Dama ta karbi key hannun Mama Tunda nan Abdullahi ke Barin key din Guda Daya Dayan kuma Dama yana Hannunshi ne.

Tana Komawa Gida ta Zage ta Fara Gyaran Gidan ganin Duk yayi Kura ta Share Tsakar Gida da Kitchen ta Share ganin yadda Abdullahi ya Birkita mata shi kawai Wajen Dafa Ruwan lipton,Ruwan zafi ma cikin Kittle yake sakawa,Dakin barcinsu kuwa Taga Abu kaya duk ya watsar Sai da ta gyara haka Tailet Ya watsar da Soso nan Sabulu chan komai dai ya Batashi Bayan ta Share ko"ina ta gyara sai ta koma Zaman gyara kayan Abdullahi na Cikin Wardrope wadanda kila wajen Daukan kayan da zai sakane Duk ya Birkita goggun Ciki ga kuma Kayanta da nashi wanda aka Dawo Dasu Daga wanki da Guga nan ya Turasu waje Daya Tana Gyarawa Tana mita acikin Ranta sai Gabda da mangariba ta gama gyaran kayan kana ta Fito Zuwa Kitchen ta Duba Fridge dinta taga Tana da Sauran Nama da Nikakken kayan Miya kawai sai ta Dora Musu Jallop din Shinkafa,Acikin ranta kuma tana Addu'an Allah yasa wannan karon Abdullahi ya siya mata gas Tuni Take nacin ya siya mata yaki wai saboda yara bata da Hankali wata Rana Sanda zasu je kusa ma bata sani ba Tunda Taji haka ta Hakura damai magiya.

Ta idar da Sallar mangariba kenan ta Kira Ammi ta Shaidamata Ta dawo Ammi tace"An dawo lafiya..Su Amira dai Kila sai Friday zasu dawo..Taji Dadin kiwon Tsohon Mijina ta nace taki Tafiya.."Hafsah na Dariya tace"Kai Ammi kodai ke kikaga Sabon Miji kika makalemai kina ma Daddy jan Aji Shi kuma ya kama Sabuwar amaryansa..?

Ammi tace"Wa..? Wannan ai ba megida bane Tunda baya Cefene.."Hafsah ta saka Dariya Ammi na Tayata tana jin Hayaniyarsu Amira Hafsah tace"Ammi kina ganin ba Matsala..? Kada fa Hayaniyarsu Amira ta Saka jinin Daddy ya kara Hawa..?Ammi tace"Ko daya karki damu ai shi Hayaniyar yaran yake so Tunda yanzu duk baku kusa dashi..Baki ga yadda yake sakewa dasu ba suma Sunfi son zama Dakinsa indai yana Gidan.."Hafsah tace"Shikenan Ammi..Ki gaida Daddyn zan kirasa.."Ammi tace"Shikenan.."Daga haka suka yanke Kiran Juna Hafsah na Mirmishi Sanin Diramar Ammi da Daddy kan Son Yaran da suka Haifa ita da Anty Hadiza,Koda Ammi tace sai Ranar Friday su Amira zasu dawo bata damu ba sanin Direba ke kaisu makaranta kuma Suna da kayansu chan Gidan Ammi kamar yadda suke dashi Agidan Mama Tunda suna yawan zuwa wasu kayan adawo dasu wasu kuma abarsu chan.

Koda Abdullahi ya Dawo ya Iske Hafsah ta gama Komai Har wanka Tayi ta Saka kaya Cikin Wasu Ubansu Riga da wando yan kanti wadanda suka kamata Sosai suka Fitar mata da Surar Jiki gefe daya kuma Tama kanta Barin Turare Duk inda ta gifta sai Tashin kamshi kawai take,kanta kuma wani Karamin Vail din gyale ta Daura,koda ya Shigo Gidan yaga Hafsah ta Dawo bai yi Mamaki ba Tunda ya Biya Gidan Mama ya ga Sakon Zanniran kuma Maman ta gayamai Sun Dawo Tun dazu Subain ma da Hafsah tare suka Fita.

Koda ya Shigo Hafsah Tana Sallar Isha"i Saboda haka kawai sai ya wuce Cikin Bedroom Karamar Jakarsa ya ijiye da key din Mashin Dinsa,kana ya Shiga Toilet ya iske ta sakamai Ruwan zafi a kittlle kawai sai ya juye yayi wanka Dashi ya Fito Kenan Daga wanka yana Sanye da Bakin Wando sai karamin Towel yana Goge Jikinsa Dashi sai ga Hafsah ta Shigo kallo Daya yayi mata ya kauda kansa kawai ya karisa gaban madubi ya Dauki mai ya Fara Shafawa.

Da kallo Hafsah ta Bisa sanin Hali yasa kawai ta karisa garesa ta Rumgumesa ta Baya Lokaci Daya ta Zuro Hannuwanta saman Cikinsa wanda Dukkansu sai da Jikinsu ya amsa Cikin kissa ta kwantar da kanta saman Bayansa Sanin tayi Laifi sai ta ke kokarin amfani da Hanyar da tasan Zata sauko da Fushinsa Da wuri.

Yana Jinta ya mata Banza sai ma Kokarin Rabata da Jikinsa yake yi Jin Haka yasa ta kara makaleshi Lokaci Daya ta Shagwabe Murya tana Fadin"Abdullahina Kana ganina na Dawo Shi ko mgana ko..? Tafada Lokaci Daya tana amfani da Hannunta Duka Biyu Tana Shafa kwantattacen gashin Daya kwanta saman Kirjinsa,Wanda sanadiyar haka Tsikar Jikan Abdullahi ta Fara tashi Ganin tana neman Birkitamai lissafi yasa yayi Sauri  Juyowa Lokaci Daya yana saka Hannu ya Raba Hafsah da Jikinsa Kallonsa take Cikin manyan Idanuwanta Shima sai ya sakarmata ido kawai yana kallonta ammh Fuskarsa ba Fara"a ko kadan

Ganin Haka yasa Jikin Hafsah sai yayi sanyi Duk Confident din Datazo dashi sai ta nemeshi ta Rasa,Sai kawai ta sadda kanta kasa tana wasa da Zoben Hannunta Cikin sanyin Murya tace"Sannu da zuwa ka Shigo ina Sallah.."

Yana kokarin Rabata ya wuce yake Fadin"Uhm...Na Shigo kina Sallah.."Daga haka bai kara komai ba ya Bude wardrope yana neman Jallabiyan da zai saka bata Dandara ba ta kara Binsa ta saka Hannun kenan zata Rikosa yayi saurin kaucewa yana kallonta Lokaci Daya yana Fadin.."Ina Kika ijiyemin Jallabiyoyina..? Yafada yana kallon Gefe Saboda Shigar datayi Domin wanke Laifinta ya kusa yin Tasiri a tare da shi.

Batare Da tayi mgana ba ta matsa gefensa ganin haka yasa Shima ya matsa hade da Juyamata Baya,Mamaki ya kara kama Hafsah aranta tace Abun Babba ne,Jallabiyansa ta Daukomai mai Ruwan toka tana Fadin"Gata ko na chanzo maka wata ne..?

Bai mata mgana ba illah ido Daya Zubamata lokaci Daya yana mika mata Hannunsa tagane Abunda yake Nufi ta mikamai Jallabiyan ta koma gefe tana kallonsa Bai sakata ba ya maidata ya Dauko Baka ganin haka yasa ta Girgiza kai ta Fice kawai Zuwa Kitchen ta Hado ma Abdullahi Dinner dinsa Zuwa Tsakiyar Cafet din Dake Cikin Falon.

Ta kawo mai Ruwa kenan sai gashi ya Fito yana waya Jin datayi yana ambaton Mutumina yasa ta gane da Nazifi yake mgana Yana zama kan Daya Daga Cikin kujerun Falon taji yana Fadin zataji Daga Haka sukayi sallama,Abincin ta Zubamai Cikin Filet tana Fadin"Na saka maka Coslow din ne..? Bai mata mgana ba sai ya Sauko kasa ya Tankwashe kafa Sai ta mikamai Filet din Hannunta zuwa gabansa ta Turamai Dan Vowl din Data saka Coslow din Shi kuma ya saka Cokali ya Diba ya zuba kana ya Fara Cin Abinci gefe ta koma tana kallonsa Sakamakon Ita ta Riga taci nata Tun Dazu.

Hankalinta ta maida kan Talabijin tana kallon Tashar Arewa24,Chan taji yana Fadin"Ashe kun Biya gidan Nazifi yau..? Hafsah ta waigo tana Fadin"Eh wlh..na kira sakinar tace tana gida bata koma ba batajin Dadi.."Kada kai yayi kafin yace"Yan suna..? Gashi kin Dawo na zata chan zaki zauna sai Zannira ta yaye kana sai ki Dawo.."Kai Hafsah ta Sunkuyar Lokaci Daya tana Fadin"Allah baka Hukuri.."Bata Rufe baki Ba Abdullahi ya katseta da Fadin"Shoutup...!!! Gabanta ya Fadi sai ta kara Sunkuyar dakai tana Wasa da adon kwalliyar Rigarta.

Cikin Bacin Rai Abdullahi ke Fadin"Banda kin Rainani Hafsah har ni na ce bazaki je waje ba ki kira Ummata ki kaimata karata ko..? Saboda Umma ke Auranki ko..? Ko kuma Ita Zanniran tafini Muhimmanci ne Tunda kika zabi ki Farantamata ni kuma ki Sabamin ko..? Hafsah ta Dago Tana kallonsa Cikim marairaicewa tace"Allah Abban Amira ba Haka ba..!Ba haka bane To yane Hafsah..?

Ya fada yana Tsareta da mayen Kallonsa mai kama da Tuhuma Cikin Fargaba ta maida kasa tana ajiyar Zuciya,Kada kai Abdullahi yayi yana Fadin"Kinsan meyasa na Hanaki zuwa sunan nan..? Bai bata zarafin mgana ba yacigaba da Fadin"Saboda ki gane ni keda iko dake..Kuma kina karkashina ne..Ina da ikon da zan Hanaki zuwa Sunan komawaye ba Kanwata Zannira ba koda kanwarki ce ko yayarki Ni Abdullahi ina da ikon da zan ce bazaki ba kuma ta zauna ammh saboda ki nuna min iyakata ki ka kira Umma ta Tilastani yin Abunda ban Shirya ba kin kyauta ai gashi kin je kinyi ma Zannira Suna kin Dawo kin barta Chan ita da Mijinta suna zamansu lafiya ke kuma kin Dawo kin Tarar da mijinki wanda kika Nuna ma bai isa Dake ba yayi kyau...".

Maganganunsa sun kashe Hafsah Jiki sai ta kada kai Tana Fadin"Nidai nasan ban Kira Umma na gayamata komai ba ita ta Kirani Tana Tambayanta meyasa banje suna ba sai nace mata kai ka Hanani batama Jira cewata ba ta yanke kiran kuma Harga Allah bansan cewa kai Zata Kira ba da ban barta ba ammh na amsa Laifina Don Allah kayi hakuri.."Yana jinta har tagama mganarta bai Tankamata ba,Ganin yayi mata Shuru yasa ta marairaice tana Fadin"Kaji..? Bazan kara ba Insha Allahu.."

Tafada tana sakarmai Idanuwanta kamar bazai Tanka ba sai kuma ya Dago yana kallonta ajiyar Zuciya ya saki Lokaci Daya yana Fadin"Ya wuce..Ammh kuma karki Fasa biyema mara Hankalin yarinyar nan Subai"atu ni ba irin sakaran Mijinta bane mara wayau ko"ina sai ki ganta tana saka kafa in kikace ita zaki dinga bi Wuyana zaki Sha Allah.."Dariya ta kusa kama Hafsah sai ta kanne Tayi Saurin Fadin"Insha Allahu.."

Ture Filet din gabansa yayi ya mike yana Fadin"Kwashe kayanan ya isheni..Nazifi na muku ban gajiya ya koma sakina ke Fadamai kun zo.."Ta mike tana Fadin"Eh muna amsawa..Sakon Naman sunanka nawajena Zannira tace azo maka Dashi.."Tabe baki yayi yana Shiga Bedroom dinsu yace"Ita kuma gulmanta yayi yawa ina Abunda ya Shafi Abdullahi da Naman suna ko ce mata kikayi mijinki baya Siyan miki nama Shine yasa ta aikomin dashi..?

Yafada yana Tsare Hafsah da ido,Da sauri tace"A"a wlh cewa tayi dai adiban maka kaida Auwal..Ni ba ruwana.."Mirmishi yayi kafin yace"Haka Chan naje Mama na turamin gabana nace wannan ai Shirmen mata ne Naman suna ta Hada suci agida,..."

Hafsah  batayi mgana ba ta kama Bakinta Shima bai kara mgana ba ya Shige Ciki ya barta tana kwashe Kayan da yayi amfani Dashi..





*Shakira.."*

Continue Reading

You'll Also Like

158K 12.2K 54
แž”แž„แžŸแŸ’แžšแž›แžถแž‰แŸ‹แžขแžผแž“แž˜แžทแž“แžแžถแžขแžผแž“แž‡แžถแžขแŸ’แž“แž€แžŽแžถ แž˜แž€แž–แžธแžŽแžถแž€แŸแž”แž„แž“แŸ…แžแŸ‚แžŸแŸ’แžšแž›แžถแž‰แŸ‹แžขแžผแž“แžŠแŸ‚แž› แžขแžผแž“แž‡แžถแž€แž˜แŸ’แž˜แžŸแžทแž‘แŸ’แž’แžทแž”แž„ Kim Taehyung Date: 24/02/21 - 02/02/22 Author: แž…แž“ แžšแŸ‰แžถแž แŸ’แžœแžถ
397K 29.8K 35
Kim - แ€แ€ปแ€…แ€บ~~แ€แ€ปแ€…แ€บแ€แ€šแ€บ~~~แ€™แ€ฑแ€ฌแ€„แ€บ Jeon - แ€™แ€ฑแ€ฌแ€„แ€บแ€žแ€ญแ€แ€šแ€บ Cv_ Pinterest
384K 25.7K 30
"แ€™แ€ฑแ€ฌแ€„แ€บแ€Ÿแ€ฌ แ€™แ€ญแ€”แ€บแ€ธแ€™แ€แ€ปแ€„แ€บแ€ธแ€แ€ฑแ€ฌแ€„แ€บ แ€žแ€ญแ€•แ€บแ€”แ€ญแ€ฏแ€„แ€บแ€…แ€ฌแ€ธแ€œแ€ฝแ€”แ€บแ€ธแ€แ€šแ€บ"