part 44

5.4K 182 4
                                    

*💖SAHRA💖*
   *Hot Love💋*

44.....

*Haske Writer's Asso.💡*

_bansan ta'ina zanfara baku hakuri ba,,,kuyi hkr don Allah... Wllh uzurirrikan sunada yawa, banyi tunanin zandau lokaci haka ban kare book dnn ba,,amma yanda katsara bahaka Allah ya tsara maka ba...kumin afuwa don Allah. Ina sonku fans dina❤._
_Masu min mssg suga banyi reply ba suyi hakuri nakwana biyu bana online ne._

     Suna fita daga dakin Aliyu ya kama shoulders dinta duka biyu yajuyo da i'ta gabanshi kamar zai shigar da i'ta cikinsa, dan rankwafowa yayi duba da kereta da yayi sosea  a tsayi ya kura mata i'do yana ganin yanda duk jikinta yayi sanyi da alamu tausayin samha ne ya rufeta, saukar da kanta kasa tayi don bazata i'ya jurar ganin kwayar idonsa ba tafara juya zoben azurfar dake hanun ta, kamo hanun yayi cikin wani irin yanayin so da kauna yashiga murzawa a hankali  yana lumshe idon sa yace"akwai wani abune!?." Yafada yana bude idonsa yasauke kan kyakykyawar fuskarta, girgiza kanta tayi murya can kasa tace"babu!."   Kugunta ya kama da hanunshi daya, ya makaleta a bari dayan jikinsa suka fara takawa parking lot. Wani irin dad'ine ya kama sahra takara manne mishi tanaji kamar su tabbata a haka kada ya saketa, sai shakar daddadan turaren jikinsa take, a haka  driver yafito  yabude musu kofa suka shiga , yama motar wuta suka fice daga asibitin. Dunkule hanu mom tayi ta daki jikin bango ta furzar da wani iska mai zafi sai huci take , sake curtain din tayi tabar jikin window tadawo cikin dakin ta zauna sai kad'a kafa takeyi, juyowa samha tayi ta kalli mom a ranta , tayi tsaki ta lumshe idonta tana kollon yanda  aliyu suka jera da sahra bakaramin haduwa sukayi ba, take taji wani mugun bakin ciki ya rufeta  tana tuno asarar abubuwa datayi a rayuwarta saboda aliyu ...jitayi wani zuciyan na tunzirata karta hakura dashi tunda akansa tarasa abubuwa masu matukar muhimmanci , "meye kuma yayi saura yanzu, banida komai narasa komai...bazan taba yarda ba saina sameka yadda nakeso kuma saina wulakanta ka! Nasa maka bakin ciki fiye da wanda nake ciki a yanzu." Wani kara tasaki tana dafe da kirjinta , nan da nan ta burkice ciwo ya tashi  kamar zata mutu, a hargitse mom tafita tana kuka takira doc yay mata alluran baccci. Bayan sati uku,,, ba'a binda yasanza game da ciwon samha , kullum ba sauki don bata kwantar da hankalinta ba ko kadan saima wasu sabbin mugayen kudurirrika datake sawa a ranta, kullum ciwo gaba yakeyi tarame, tabushe tayi baki, ga matsanan cin ciwon kai da zazzabin cikin dare tareda yawan jiri datake fama dashi. Yau misalin karfe takwas likita yazo dubata ya tadda ta, tana kwarara amai kamar zata amo duka kayan cikinta , ga mom na kanta  duk ta gama rudewa tafara zargin ko ciki ne da i'ta,  kura mata ido likitan yayi yana kallon yanayinta, kawar da kansa yayi daga gareta yakira wasu nurses biyu suka gyarata,,  bayan an gyara gurin ya dubata snn ya daibi jininta ya fita. Karfe goma  Aliyu yafito daga wanka daure da towel, hada ido sukayi da sahra dake zaune bakin gado tana sanye da atampa riga da skart sunyi matukar yimata kyau tai saurin sauke kanta kasa, ganin yanufo inda take yasa tatashi tafita daga dakin baki daya yay murmushi ya'i'sa gaban mirror yafara dressing. Kananan kaya yasaka, riga polo da bakin trouser bakaramin kyau yayiba, yay cuming gashin kansa . a falo ya taddata tana zaune , tana ganin fitowansa tatashi tai gaba abunta don dama breakfast zasuje suyi, murmushi yayi shima yabi bayanta. Tunkafin sukarasa cikin falon suke jiyowa muryan hajja sai ruwan bala'in take saukewa, rabewa gefe sahra tayi ta sauke kanta kasa ganin yanda hajja keta fada a abba, bata fuska aliyu yayi ya karaso gurin yace "hajjja!." Juyawa tayi takallesa taja dogon tsaki tajuya taci gaba da balbale abba tana fadin"wllh dole ka kori wnn shigeya maiyar yarinyar, don bazai yiyu su talautarmin dakai ba, kullum shegiya tana faman kwanciya a asibiti wai ba lpy wayasani ma ko karyane...to wllh dole uwarta ta maida i'ta dangin ubanta don daga yanzu bazaka kara biya mata kudin magani,,,kawuce muje asibitin yanzu kashaidawa uwarta cewa karta yadda tadawo maka da 'yarta cikin gidannan kuma bazaka kara kashemusu ko sisi ba can sukai dangin ubanta. Hakuri abba yarinka bata yana cewa "kiyi hakuri don Allah hajja...zanyi duk yanda kikeso...Allah ya huci zuciyarki."  Juyowa tayi ta bankama Aliyu harara tace "daina  kallona dalla malam, saiwani muzurai kake da mola2 ido."idonta ne ya sauka akan sahra dake tsaye har lokacin kanta kasa ta washe baki tace" kai yarinya yar albarka ashe kina gurin nan?, kinga kainane yadau zafi banma kula dake." Karasowa gurin sahra tayi ta dafa kafadunta tana cewa"ki kwantar da hankalinki don kuwa yanzun nan zamu yada kwallon mangoro muhuta da kud'a..wnn shegiyar bazata kara dawowa cikin gidannan ba, dole ta hakura tabarki keda mijinki kusakata Ku wala bamai takura miki wllh...kuma kikara kwantar da hankalin kwana kwanan nan zaku tashi daga nan kukoma sabon gidan mijinki kuyi abinda ranku yakeso." Takarashe maganar tana kara washe baki, i'tadai sahra batace komai ba kanta kasa har hajja tayi ta gama Surutunta.  Kallon Abba hajja tayi taimishi alama dasu tafi, bamusu  yanufi hanyar kofa i'tama tabi bayansa, har sunje bakin kofa  tajuya taga su mami sunanan gun tsaye masuda alamar tafowa tace"to mahammadu saika fada musu dakanka sutaho muje don naga basuda niyyar fitowa,,,tunda ga marainiyar wayonsu wacca basu dauketa bakin komai ba tayi magana."  Bawanda ya tanka mata a cikinsu suka fito mota biyu suka yi asibiti. Sai Sha daya   suka i'sa,  kai tsaye dakin da'aka kwantar da i'ta duka suka nufa,  hajjace a gaba i'ta tafara shiga  tana watsawa mom harara ...kirjin mom ne ya buga datayi tozali da hajjja don tasan ganinta ba alkhairi bane a gareta ba. Da kyar mom ta tattaro kala manta tace"sannu da zuwa hajja!. Ya mutsa fuska tayi tace "kyaji da gulmarki ni ba'abinda ya kawoni kenn ." Daya bayan daya mom tarinka bin mutanen dake cikin dakin da kallo Kirjinta na bugawa don yanayin bba kadai ya tabbatar mata da cewa ba lpy.  Gyara tsayiwa hajja tayi tana fadin"hawwa kina jina ko?, ba komai ya kawomu ba illa mahammadu zai shaida miki cewa ...ki tattari yarki ki maidata dangin ubanta indai har kinaso kici gaba da zama dashi , don bazai yuwu ace yarki ko yaushe tana cikin rashin lpy yana kashe mata dukiya ba, ga fitintunu da suke tashi ta dalilinta don haka gara kiyi gaggawar maidata don bazata kara shiga gidanba kuma ko sisinsa bazai kara kashewa a kanta ba." Hashin hankali baasa masa rana, iyaka tashin hankali hankali mom yatashi ,don bata taba tunanin faruwar haka ba, wnn wani irin sabon wulakanci ne hajja zata bijiro dashi?, daura hanunta tayi biyu bisa kanta ta fasa uban i'hu wanda yay sana diyar farkar da samha daga bacci. Da kyar ta'iya bude idonta wanda sukayi mata balain nauyi ga azababben ciwon da kanta ke mata tatashi da kyar tana karewa mutanen dake cikin dakin da kallo, idonta ne ya fada kan hajja dake faman aika mata da harara .Gabanta ne ya fadi sosea taja dogon tsaki a ranta tana fadin"mayyar tsohuwa!."  Ji sukayi mom takara sakin wani karan tana cewa "nashiga uku ni hawwa , yazanyi da rayuwata?, ina akeso incusa raina?, ko i'na an tsane mu ansamu a gaba yakukeso muyi...yanzu fisabillahi hajjja bakin ciki kike da zaman samha kenan da har zakisa danki ya koreta?..i'na kikeso taje ? Batada kowa duk dangin mahaifinta sun mutu nikadai takeda a rayuwarta."  Tabe baki hajja tayi tace"wnn kuma damuwarku ne, mema mata yanda zataje kawai zakiyi don zamanta yakare a gidan d'ana kam." Sai yanzu samha ta fahimci inda inda maganar ta dosa, "wato korata hajja takeso tayi daga gidannan knn?." Shigowan doctor ne yakatse kowa duk suka juya suna kallonsa,  baidamu da tsatstsayen dasukeba dakuma kallon sa da suke yanufi gurin abba hanunshi rike da wata farin fefa yana kokarin mikama abba , hajja tazo da sauri tana cewa"kul mahammadu, kada ka kuskura kakarbi wnn takarda don nasan bata arziki bane bazai wuce ta sayan maganiba, kuma kaga wancce zaka kaiwa don itace uwarta." Tanuno mishi mom.  Murmushi likitan yayi yace "mama, dakin kwantar da hankalinki don wnn ba takardar magani bace, sakamako ne na bincikenmu damukayi mungano cewa yarku tana dauke da cikin sati biyar." A matukar razane duka suke kallon likitan barin samha da tuni zufa yagama wanketa kirjinta sai fat2 yake kamar zai fadi kasa , tsananin tashin hankalin data shiga baya misaltuwa, mom kam neman guri kawai tayi ta zauna don jirin dake kokarin dibanta, hajja salati tarinka yi tana tafa hanu tana fadin"kaga irinta ko?, gashi ka'ijiye karuwa a gidanka tana ta zuba gantalinta kai baka saniba,,,ea dama tsintacciyar mage bata mage!."  Nuna samha da yatsa abba yayi bakinsa na rawa cikin wani kakkausan murya yace " samha a gidana!?."  Ga mamakinsu sai sukaga tasaki murmushi tana fadin"abba ea bani zaka tambaya ba, wanda yamin cikin shizaka tambaya,,,,danka na cikinka shine yamin ciki a cikin gidanka !."

View wattpad @ habiebahlurv

💖SAHRA💖Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang