Washe gari
Manya manyan yan kasuwa da maikatan gwamnati sun hallara ga guma manyan sojoji duk sun zo dan shaida auren captain Muhammad da amaryar sa
Karfe biyu na rana aka daura auren Muhammad habib da khairat abdulrahman akan sadaki dubu ashirin
Kowa sai yi wa ango fatan alkairi da zaman lafiya yake
Anje inda akayi reception da ga nan kuma suka zo gidan amarya
Khairat na shiryawq dan ance ka ango nan zuwa , aunty fati ce ta shigo dankin tana guda kika ce kina so amarya da ba ki da ba shi ke ba , yarinya kin zama matar aure , nan adama ma ta shigo sai tsiya suke ma khairat ta zama dauko dauko, ta zama dauko Riga ta zama da ama furar nan
Wakar su suke ama ita kwa amarya kuke take idon nun ta sunyi ja ga ya kumbura dama bata samu tayi barci ba , falmata ce tace aunty dan allah kuyi hakuri kunga kun sata kuka kuma yanzu ango zai zo ko makeup ba ama ta ba...
Nabila ce ta shigo da kankara suka fita da khairat daga dakin aka kai ta wani suka rufe yanda ba mai shigo
Oya dan allah ki daina kukan nan Dan bai da amfani, falmata wai na zama matar aure , dariya nabila tayi tace sis in law Mrs mubarak
Mikewa tayi tace bara inyi nafila sai ki min makeup din
Nafila tayi tana rokon allah ya bata zaman lfy da kwanciyar hankali allah ya hada kawunan su , allah ya sa mata hakuri da juriya a zukatan su allah ya tabbatar masu da alkairi da ke ciki..
Ameen
Falmata ta fara aikin ta sai da suka sa mata iceblook a wurin idon sanan suka samu idon ya rage kumburi da ja
Sunaji ana knocking kofa wai su fito da amarya a dau hoto
Zasu tada min hankali su bari a gama shirya ta a kwanciyar hankali in ya so sa kwana suna daukan hoto
Ango ya iso nan suka jiyo guda da yake dakin da su ke ana iya gani ta window nan suka leka sanye yake cikin white boyel wanda ya sha aiki da bakin zare idon sa boye cikin glass sai gaisa wa yake da yan uwa
Khairat dai kasa tashi tayi saboda falmata tace yanzu sa ace ta fito
Minute kadan aka gama makeup, dauko asoebi da zata sa aka sa mata sanan ta nada mata dauri sai kunga yanda tayi kyau
Siyama ce da nabila suka riko ta aka fito da ita nan mutane suka fara su zasu fara daukan hoto da ita
Daker aka samu suka ratsa jama'a suka je falon baki inda ango da abokanan shi suke
Mubarak na ganin su ya mike ya rungume khairat yace alhamdulillah nan abokanan shi suka hau she wa
Ita kwa kasa motsawa tayi dan jin sabon abu shi kanshi yaji wani iri bai San a wacce duniyar yake ba ihun abokanan shi ne ya sa ya jawo hanun ta cikin palon suka zauna
YOU ARE READING
KHAIRAT
RandomA naki tinanin zan bari ki zauna a gidan nan ke kadai....kin kwace min miji kin kwace yayyana yanzu kuma mai kike so gareni...Khairat, farin cikin yayyana shine farin ciki na duk mai son ya batamin ya taba farin cikina.....ku biyo dan sanin ya rayuw...