Part 28

188 7 0
                                    

*💫❤LOVE CYCLE✨*

Written by

*@nnafie🖤*
(Smll but mighty😉)

*writer of*
Saif
Adaan
Wata mafita
Saboda duniya
Love cycle......

Bismillahir rahmanir raheem

💫❤Love cycle❤ (28)✨
Sultan ya runtse idanu zuciyar sa nayi masa wani irin zafi.. Ya dubi su yusrah da take ta sauke ajiyar zuciya kasan kadan take jira ta fashe.. Farouq ya budewa chucu mota zuciyar ta fess ta shiga se kanwar sa wacce ke bima Jiddah.... Jiddah kam tare dasu mamie ta tafi.. haka ma yusrah motar su mom tafi dukan su babu wacce bata kuka.. Hafsat dama tafiyar su daya da Sadeeq..
Fareeda ta gaisar da Amoon ya kalleta ta mirror yace "fareedan umma ya sch".. Tace "Alhmdllh".. A hankali Fannah ta gaisar dashi.. Ya noke kafada "bazan amsa ba"..ta Langwabar da kai "why".. Yace "fareeda baki ji me tace ba wai good morning haka ya kamata mata ta gaisar da mijin ta kamar ma batayi murnan ganina ba".. Fareeda kam murmushi kawai take Fannah ta ware hannu "but you didn't tell me you're coming".. Yace "umm na koma knn".. Tayi murmushi batace komai ba...yace "zaki gane kurinki kika sani ma ko acan kafin mu dawo za'a daura auren"... Fannah ta ware idanu yadan kashe mata ido... Yace "kinga daga can kawai fit... Duk inda zanje tare zamu tafi yarinya".. Fannah de tayi shiru batace komai ba.. Ita kanta fareeda se murmushi takeyi.....
Tun basu yi nisa da barin Abuja ba suka fara bacci.. Ta mirror ya dubi fareeda ganin bacci take yasa ya maida idonsa a Fannah yanda take bacci se tayi masa kyau.. He just can't wait suyi aure yaga tana bacci tare dashi.. Dan kwantar mata da kujerar yayi yanda zataji dadin kwanciyar.. Snn ya shafa gefen fuskar ta a hankali... Dan bude idanu tayi se kuma ta lumshe..... Seda sukazo kaduna snn ta farka.. Tana kallon garin yace "kaduna".. Taita kallon garin.. Daga nan duk garin da suka wuce seya fada mata sunan sa.. Taita kallo cike da nishadi.. Idan kuma ta gaji seta koma bacci ... Zuwa 4 suka shiga cikin garin katsina... Fannah ta rinka kallon state din tata.. Ganin yanda take kallo yasa ya kamo hannun ta yace "kin gaji ko".. Gyada masa kai tayi ga azumi yace "anan za'a daura Auren mu".. Ya fada hankali yana dan murza hannun ta.. Fareeda setaji duk sun bata tausayi.. Hakika suna son junan su tasan idan akace za'a raba su zasu wahala... Tunda take tun tana yarinya ma bata taba ganin koda wasa Amoon ya nuna yana son wata ba.. Amma yau ko yanda ya rikayiwa Fannah a motar nan ya isa ta tabbatar cewa Amoon nason son fannah.....ita kanta ynx da sultan yaci ace ta ciresa a ranta amma ta kasa....
A babban family hause din nasu suka sauka.... Kafin ta fita Amoon yace "don't stress ur self wajen gaishe gaishen nan ki bari se ansha ruwa kinji"... Ta gyada masa kai snn ta fita... Duk yawan mutanen wajen da sultan ta fara hada idanu tana fita a motar dan kusan duk a tare suka isa.. Dauke kai tayi.. Tana kallon mutane dayawa da aka firfito sbd murnar ganin su.. Barin ma ita da kowa keson gani.. Kowa se zuwa yake yana rungume ta da yaba girman da tayi.. Fannah de se murmushi take ganin yanda kowa ke farin cikin ganin ta .. Dan daga kai tayi suka hada ido da Amoon yadan langwabar mata da kai... Alamar ta wuce daki mana.. Sede ta dauke kanta.. Ta cigaba da amsa gaisuwar da wata tsohuwa ke mata da tambayoyi se murmushi take ganin yanda tsohuwar ta hakimce saman kujera tana bayani da alama de kanwar baffa ce.. Chucu ce tazo ta kama Fannah tana fadin "Adda bari muje ta huta dan Allah kinsan ta gaji bakuma ta saba wnn doguwar tafiyar ba".. Adda tayi mata dakuwa "kinci ubanki Amadu haushi fa take ji bn kula ta ba".. Chucu ta murguda baki taja Fannah suka wuce wani daki daban... Fannah ta zuwa ta baje saman gado tana lumshe idanu "wlh na gaji ga wata irin yunwa".. Chucu ta harareta tace "bayan soyayyar da kukasha a mota se kuma kice kinajin yunwa na dauka a koshe kike".. "Ke da kika taho tare da yaya farouq kin koshi knn".. Chucu ta ware hannuwa "full wlh".. Fareeda data shigo ynx tace "itama a koshe take.. Dan yau nasha kallo nasan na biyo motar masoya ko kunya ta fa basaji"... Tashi Fannah tayi ta shige toilet tana dariya.. Ganin wani tsalle da chucu tayi ta rungume fareeda wai se ta bata lvri.. Ita kanta tun tanajin kunyar fareeda har ta ware ta rika biye Amoon a motar.. Kuma tasan daba dashi bane kila da tafi haka gajiya....
Adda ta dubi yusrah da idanun ta suka kumbura tace "ke kuma lpy keda baki rabo da fitina".. Yusrah ta murguda baki ta tashi ta shige dakin da mom ke ciki.. Adda ta tabe baki tana fadin "kyaji dashi nasan Aliyu ne ba wani ba".. Amoon da yadan kalleta ta gefen idon suka hada ido.. Dauke kai tayi ta nuna kamar ma bata gansa ba.. Dan murmushi yayi ya tashi ya koma kusa da ita tare da bata side hug. Ture sa tayi "kai nifa tsoro kk bani".. Daidai kunnen ta ya rada mata.. "Nifa na samu mata Adda".. Ta dan ware idanu.. Tayi masa alama da hannu akan wacece "ya rada mata "yanda tayi da fuska seda yayi saurin rufe mata baki dan karma ta daga zancen.. Ganin haka yasa tayi masa alama da zasuyi magana.. Tashi yayi ya fita yaki yarda ya kalli mammah ya yasan kallon sa take...
Fannah na idar da sallah ta kara kwantawa duk tsokanar dasu chucu suke mata bata bi takansu ba dan wlh ta gaji.. Quranin data gani ta dauko ta fara karantawa se gab da magrib snn ta aje .....
Fannah fareeda ce ta shigo masu da kayan shan ruwan su sukayi snn suka fita tarawi...
Washe garin ana idar sallah seda suka sha baccin su na gajiya snn suka tashi.. Ana yin azahar suka fara aiki kasancewar gobe sallah duk da akwai yan aiki dole su saka hannu sbd ayyukan dayawa.. Duk tare sukayi aikin amma babu wanda ya kula wata tsakanin ta dasub jiddah.. Sallah ce kade ke tashin su.. Chucu ta mikawa Fannah wasu kaji da aka gama gyarawa.. "Ki yiwa yaya dambun nama me yaji snn ki saka tafarnuwa".. Dagowa tayi suka hadu idanu dasu yusrah.. Taci fuska ta karba ta fara sarrafa ta... Tana gamawa ta saka a inda chucu ta miko mata ta dube ta tace "ina za'a aje".. "Kai dakin mu".. Fannah ta mike ta fita.. A parlor ta iskesu shida wani wanda da alama shima ba'a nan yake zaune ba jiya yazo "sageer" taji suna ce masa.. Dan gaisar dasu tayi ta wuce zuwa dakin su.. Ta aje .. Tana juyowa taga Amoon tsaye jikin kofa har ya bata tsoro.. Ta ja baya da sauri.. Se kuma ta shagwabe fuska tace "ka ganka ko" yace "nimene".. "Ka bani tsoro".. Ta gyara tsayuwa "to mene Acan".. Ta ware idanu "ina ruwanka".. Ya langwabar da kai "ke kikayimun da kanki".. Ta girgiza kai... Yy murmushi yace "just can't wait to teste it idan ansha ruwa zaki bani".. Fannah ta noke kafada.. Ya harde yace "sageer".. Ya amsa.. Ya dubi Fannah yace "come with me".. Bin bayan sa tayi bayan sun fita parlor yace "sageer waini za'a ma rowar nama".. Sageer ya ware idanu "wnn da kike gani maye ne mayen dambun nama ne ko bayan aure da kinyi ki boye".. Fannah tayi murmushi ta shige kitchen bama ta dauka sageer nada magana ba..
Koda aka sha ruwa duk yanda Amoon yaso cin naman nan kin yarda su hadu tayi karshe ma cikin mutane ta shige inda baze iya zuwa ba.. Se can da daddare tayi shirin bacci ya tura mata message "just craving for it amma kin hanani".. Tura masa tayi "srry".. Yace "no bad hope it will be the first thing I will eaten tomorrow after eid".. Ta tura masa da inshaallah.. Daga haka ta kashe wayar ta ta kwanta bacci".. .
Washe gari eid.. Sukayi duk wasu dabiun daya kamata .. Snn kowa ya shirya cikin kayan sa masu kyau..Fannah ta rinka kallon yanda su chucu sukayi kyau kamar wasu larabawa.. Chucu tazo saitin kunnen ta tace "you look so take away kaman wata balarabiya zataje masallaci"....
Murmushi kwai chucu tayi.. Key fareeda ta amso masu na mota wajen Adda ita tayi drving dinsu zuwa masallacin.. Yanda Fannah taga musumai dayawa kowa nata addu'a se abin ya birgeta fisrt tym zatayi sallah a kasar ta cikin state dinta tare dakuma yan uwanta ga musulmai ta koina.. Dole ta godewa Allah daya nuna mata wnn rana"...
Seda fareeda ta zazzagaya dasu sosai snn suka dawo tunda tasan gari sosai tana zuwa... Sanda suka dawo kusan dayawa suna cikin compound din da alama kila duk dawowar su knn... Fannah ta rinka kallon Amoon dayayi wani irin kyau cikin manyan kayan snn ta dauke idanu ta maida kan dad dinta wanda kallo daya zaka mata kasan yana cikin matsanaicin farin ciki"..
Tana fita wajen dad dinta taje ta rungume sa cike da murna .. Kusan kowa wajen iyayensa ya tafi yana masa barka da sallah..
Daganan suka rinka yiwa junan su aka fara yin hotuna na wajen hotuna seda sultan yasan yanda yayi ya tsaya kusa da Fannah.. A hankali yace "Fannah are you doing the right thing".. Kamar bazatayi magana ba se kuma can tace "me nayi".. Yace "you're ignoring me".. Tace "hakan shine dede".. "Why" tace "baffa yace na rabu da dukan ku".. Ya danyi murmushi "but ai ni kade kika kyale bnd Amoon".. Fannah tayi shiru amma har ga Allah haushinsa take ji.. Yace "pls koda call dinane pls be picking".. Gyada masa kai tayi.. Sbd dagowar da tayi taga Idon Amoon a kansu.. Seda gaban ta ya fadi Amma ta dake.. Ganin ya bar wajen ma gaba daya yasa duk jikin ta yayi sanyi.. Dama shi be shiga hoton ba gaba daya..
Bayan an gama kowa ya shiga ciki.. Har aka fara hada hadar cin Abincin bataga Amoon ya shigo ba.. Gaba daya duk se taji ta kasa ci.. Kusan har aka gama Amoon be zo ba. Sageer ne kade taji ya tambayesa akace may be ya tafi wani wajen.. Amma ita ai tasan yana cikin gidan sultan ma ya sani amma beyi magana ba.. Ganin babu wanda ya kara maganar sa yasa ta tashi a hankali ta fita.. Hanyar data ga yabi nan tabi can ta hangosa zaune cikin wata er rumfa yana danna wayar sa.. Komawa tayi.. Seda taje daki ta dauko dambun sa snn ta wuce kitchen seda ta diba masa komai har zu drink snn tasaka a tray snn ta juya tabi ta baya.. Tana karasawa gaban ta na faduwa tayi sallama.. Ya amsa ba tare daya juyoba... Jin muryar sa kade ya isa ya tabbatar mata da yana cikin damuwa.. Kujerar dake kallon tasa ta zauna tace "why are you alone".. Ba tare daya kalleta ba yace "just".. Ta langwabar da kai.. "Is it because of sultan".. Yace "am just thinking of how to handle that guy"... Tace "but I love only you".. Ya zuba mata idanun sa da suka canza kala snn yace "I don't knw why but sultan nason shiga gona ta.. But idan beyi wasa ba se bakin ciki ya kashesa"... Kamar Fannah zatayi kuka tace "beb pls forget about that ga abinci". Dan murmushi yy.. A haka ta tsare sa seda yaci duk abinda ta kawo masa snn ta tashi.. Duk yanda yaso ta tsaya ki tayi.. Ta dawo parlo ynx duk babu iyaye se su yaran tare da Adda da alama labari take basu.. Fannah ta shigo ta zauna ba tare da Adda ta ganta ba ta boye bayan Hafsat... Babu jimawa sega Amoon ya shigo.. Duk suka bisa da kallo wajen farouq dake wani murmushi yaje ya zauna tare da dan tallabar masa keya...
Da yamma.. Sadeeq ya dauke su ya zazzagaya dasu cikin gari.. Basu dawo ba se dare shima sallah kawai sukayi suka kwanta.....
..
haka Washe gari ma wani fitan suka karayi tunda suka fita basu dawo ba se yamma.. Yanda Fannah taji dadin sallahr nan ba'a magana bata taba sanin haka ake sallah ba gashi har hawa sunje kallo duk da basu wani dade ba suka dawo amma abun ya kayatar da ita.. . A get suka hadu da Amoon da sageer zasu fito.. Tsayar dasu yayi yana kallon Fannah yace "ur bag.. Sbd kwai abinda yake son saka mata.. Da kamar ta cire wayar ta se kuma ta mika masa gaba daya... Ya tafi da ita.. Cikin motar sa ya shiga ya ciro wasu bngles masu kyau na gold ya saka mata a jakar. Snn ya dauko wayar ta sbd da tayi karar shigowar message.. Dubawa yayi ganin sultan.. "Dear pls lets meet by 8 pls don't ignore".. Amoon ya rinka kallon message din.. Da ynx yayi niyar maida mata da jakar amma se ya fasa ya shiga contact din sultan yana duba messages din yake tura mata bata reply".. Zuciyar Amoon wani irin tafarfasa kawai take.. Wayar ya saka aljihu jakar kuma ya barta cikin mota yacewa sageer suje... Suna dawowa sallahr ishai yaji wayar na ringing kara dubawa yayi ganin sultan ne.. Tuni idanun sa suka sauya kala.. Ya rasa gane me sultan yake nufi shi gaba daya.. Suna shiga parlor ya hango sultan dake zaune cikin wasu raw na kujeru yana danna waya.... Kiran ne ya sake shigowa Amoon yayi silencing wayar snn ta karasa kusa da sultan zuciyar sa na wani tafarfarsa a tym din ji yake ze iya yiwa sultan dukan tsiya dan ya kaisa bango.. Sultan be an kara ba se ji yayi an fizge wayar an bugata da kasa... Ya dago da sauri yana kallon Amoon da idanun sa sukayi jawur... Tsabar fitina da kishi dake cinsa a lokacin.. Cike da fusata sultan yace "what? Amoon, my phone," Amoon yace "an fasa do what ever you think you can do.. And if you did not stay away from Fannah I will do worst than this".. Sultan ya rinka kallon sa ransa a mugun bace.. Before ramadan ya siyi wayar nan amma ba wnn ne damuwar sa ba yanda Amoon yazo ya fasa masa and yana masa magana cike da isa kamar ya haifesa shi yafi komai bata masa rai.. Sultan yace "an kula ta din who are you to give me rules.. Wlh Amoon kai baka isa ka hanani abinda raina ke so ba yanda kake son fannah nima haka nake sonta kuma".. Ai be idasa ba Amoon ya shake wuyar sa "don't ever se that again Fannah tawace ni kade." Hakan yasa shima sultan ya kaimasa wata shakar... Tuni akazo ana kokarin raba su.. Amma yanda kowa ya harzuka da yanda kowa yake jin haushin dan uwansa se aka kasa raba su... Seda mom ta fito ta taka matsu tsawa snn suka rabu amma basu bar gayawa junan su magana ba... Wata tsawar ta sake daka masu.. Se ynx suka kula da Abie, abu, se daddy da kuma Abban sageer.. Da alama shigowar su knn.. Abie yace "you guys should meet me and Fannah should join".. Duk bin bayansa sukayi kowa fuska a hade..
Duk suna ciki mom ta shigo tare da Fannah.. Kanta kasa bata yarda ta kalli kowa ba se Amoon.. Kansa a kasa yake amma kallo daya zaka masa kasan a zuciye yake....
Abbu ya tambayesu a binda ke faruwa. Sultan ne yayi karfin halin yin bayani Amoon de be dago dan babu ma alamar zeyi magana.. Abbu ya dubi Amoon "why did you did that. Aliyu".. Ba tare da Amoon ya dago ba yace "he should stay away from Fannah".. Abbu yace "you're very stupid the two of you.. Fada akan mace.. And wait baffa yace you guys should both let her..nether one of you will marry her.. Oh kun manta.. Sbd kunga mun zuba maku idanu" ya dubi Fannah yace "mamana" ta dago idon ta yace "inshaallahu gobe zan sama maki wani daban basu ba inde har ya maki in few days time za'ayi maku baiko"... Fannah ta amsa idanunta cike da hawaye.. Yace "Allah ya maki albarka.. Duk wanda ya sake maki magana ki kawomin karar sa and I will deal with that person" ta gyada masa kai tana kallon Amoon da har lokacin kansa a kasa yake.. Snn ya koma gasu Amoon yace "and duk wanda ta kawomin zancensa a cikin ku wlh zaku sha mmki na inshaallah inde har wanda na kawo yayi mata ranar Friday za'a masu baiko kuma ku shirya cos tun ba yau ba nariga nayiwa su yusrah alkhawari dan haka Amoon ka shirya auren ka dasu babu fashi... And you sultan.. It seems lyk you're not on ur ryt sense.. Kaima ka sani har fareedan kafasa auren ta itama I will get her one and before Friday ka tabbatar ka fito da wacce zaka aura".. Kaji na rantse inde har kuka saba dokata zaku sha mamaki".. Sultan ya rinka kallon Abbu jin wai har fareeda ya fasa basa.. Shifa bece bayason fareeda ba.. Yana mugun sonta kawai de baya so Fannah ta subuce masa ne shiyasa amma yanason fareeda.. Yace "Abbu kuyi hakuri wlh na hakura da fannahr zan auri fareeda wlh. Inasonta.. Tsawa mom ta daka masa "will you shoutup my friend you're very stupid se ynx kasan da haka to wlh koda wasa inga ka kara kula fareeda da neman rigima ne yasa ka kyale ta".. Kasa yayi da kansa cike da tsoro dan yasan kila wnn shawarar mom ce dan ba wani ba... Abbu ya rika masu fada.. Sosai yaga karaya da nadama a idon sultan.. Amma ko daya be gani a idon Amoon ba.. Babu ma Alamar ze karaya.. Ana sallamar su Amoon ya tashi ya fice ba tare daya kara kallon kowa ba.. Sultan kau tsayawa yayi ze bata hakuri.. Abie ya masa wani kallo yace "get out".. Ya kalli mom dinsa ta zuba masa harara hakan yasa ya tashi jiki a sanyaye...
.....
Urs
✨✨✨
Nafeesatu....😍😍

LOVE CYCLE❤✨Where stories live. Discover now