Jasmine Baturiyya ce

By Amiratuoo

117K 8.8K 1.4K

Completed (Currently Editing and Re-uploading) JASMINE haifafiyar kasar ingila (England) ce. Ya'a ga hamshaki... More

🌷JASMINE🌷
🌷Shafi na 1🌷
🌷Shafi na 2🌷
🌷Shafi na 3🌷
🌷Shafi na 4🌷
🌷Shafi na 5🌷
🌷Shafi na 6🌷
🌷Shafi na 7🌷
🌷Shafi na 8🌷
🌷Shafi na 9🌷
🌷Shafi na 10🌷
🌷Shafi na 11🌷
🌷Shafi na 12🌷
🌷Shafi na 13🌷
🌷Shafi na 14🌷
🌷Shafi na 16🌷
🌷Shafi na 17🌷
🌷Shafi na 18🌷
🌷Shafi na 19🌷
🌷Shafi na 20🌷
🌷Shafi na 21🌷
🌷Shafi na 22🌷
🌷Shafi na 23🌷
🌷Shafi na 24🌷
🌷Shafi na 25🌷
🌷Shafi na 26🌷
🌷Shafi na 27🌷
🌷Shafi na 28🌷
🌷Shafi na 29🌷
🌷Shafi na 30🌷
🌷Shafi na 31 🌷
🌷Shafi na 32 🌷
🌷Shafi na 33🌷
🌷Shafi na 34 🌷
🌷Shafi na 35🌷
🌷Shafi na 36🌷
🌷Shafi na 37🌷
🌷Shafi na 38🌷
🌷Shafi na 39🌷
🌷Shafi na 40🌷
🌷Shafi na 41🌷
🌷Shafi na 42🌷
🌷Shafi na 43🌷
🌷Shafi na 44🌷
🌷Shafi na 45🌷
🌷Shafi na 46🌷
🌷Shafi na 47🌷
🌷Shafi na 48🌷
🌷Shafi na 49🌷
🌷Shafi na 50🌷
🌷Shafi na 51🌷
🌷Shafi na 52🌷
🌷Shafi na 53 🌷

🌷Shafi na 15🌷

2.8K 225 7
By Amiratuoo

Jasmine da kyar ta tashi tayi sallar asuba domin ji tayi duk jikinta na mata ciwo saboda dan aikin da tayi jiya, tana idar da sallar ta koma bacci, ba ita ta tashi daga baccin ba har sai karfe 9:10am na safe, tana tashi ta tarar da tarin missed calls a wayarta, tana dubawa taga Basma da Khadija ce su ka kira ta, cikin hanzari ta kira Basma tayi ta ringing har ta katse bata dauka ba, sake kiranta tayi har sau uku amma sam bata dauka ba, sai layin Safna ta kira taci sa'a tana kira Safnan ta amsa. Safna ta faɗa mata sun shirya tun dazu, ita kadai suke jira gashi basu san inda take ba bare su zo su dauke ta, fada masu tayi cewa tana gidan Alamin na Abuja, amma kaf cikinsu babu wanda ya san inda gidan  yake sai kasa ta sauka tasa aka kwatantawa driver da zai kawo su inda gidan yake.

Tana gama wayar tayi sauri ta koma sama da gudu ta shiga bathroom tayi wanka dan su Basma sun taho, tana fitowa tayi sauri ta dauko kayanta,  dogon wandon jeans crazy ta saka tare da farar riga vest, ta zauna tana jiran su kawo mata T shirt din kungiyar da zata saka yau domin su hallaci taron ranar yaki da ciwon cancer Mama ta duniya (Breast Cancer awareness day) da ake yi duk shekara ranar 27th October a Abuja, daman halartar wannan taron ne ya kawo su Abuja, da duk shekara su Basma na halarta, wannan shekarar kuwa gayyata ta musamman aka yi ma Jasmine tana cikin guest speakers a taron a matsayinta na likita.

Styling din gashinta Jasmine tayi in curls ta sake shi ya sauko har kugunta sannan ta dauka yar karamar jakarta ta zuba abubuwan da zata bukata sannan ta saka sneakers dinta. Jasmine saukowa kasa tayi tana gyra Iwatch din da ke hannunta, ganin rana ta kwalle yasa ta bude jakarta ta dauko sunscreen dinta ta kara shafawa sannan ta saka bakin glasses da p-cap. Ma'aikatan gidan ta fara tambaya inda Alamin yake bayan ta gama shiryawa amma babu wanda yasan inda yake a cikinsu, hakan ta hakura da neman sa ta fito farfajiyar gidan domin tambayar Ma'aikatan waje koh ya fita, tana fitowa taga bakar Range Rovers ta shigo cikin gidan, Khadija ta fara bude motar ta fito sannan su Basma suka biyo bayanta.

Cike da fara'a Jasmine ta karasa inda suke tana zuwa kuwa Basma ta rungume ta "Wallahi nayi missing dinki Jas."

Dariya Jasmine tayi "Kai Basma, jiyan jiyan nan fa muka rabu."

"Toh ba'a missing din mutum na kwana daya ne, naga ana fara missing din mutum mah in less than an hour," Basma ta mayar mata tana dariya.

Murmushi Jasmine tayi "Indan na koma London wallah zan yi missing dinku, mu shiga." Jasmine ta ja su cikin gidan suka zauna a livingroom bayan sun bata rigarta taje ta chanjo cikin hanzari domin ba dadewa zasuyi ba saboda har an fara taron ma, lema kawai Jasmine ta dauko suka fita.

Kallon da Khadijah ke wa Jasmine ne yasa ta tambayeta "Lafiya Khadijah?"

"Amma Sis zaki saka hijab koh?" Khadijah ta tambayeta.

"Hijab? Meyasa?" Jasmine ta mayar mata da tambaya.

Safna ce tayi murmushi tace "Tab, kinsan halin Yaya Alamin kuwa, Allah dai yasa kar ya ganki a haka, dan muma bah tsira zamu yi ba a haka balle ke da kike wifey dinsa."

"Amma ai wannan casual dressing ne, it's just jeans and a shirt and zamuyi tafiyar kafa." Jasmine ta fada tana kallon kayan jikinta.

Suna zuwa kuwa basu dade ba aka kirawo Jasmine tayi nata bayanan, Dr Jasmine Mahmoud Alejandro, mutane da dama sun ganeta musamman lokacin da aka kira cikakken sunanta har da na mahaifinta duk da bata amfani da sunansa ita family name dinsu Alejandro take amfani da shi. Mr Mahmoud Alejandro yayi tashen Arziki sosai a duniya lokacin yana da rai domin sai da ya rike matakin mai arziki na daya Uk kafin rasuwar sa, sannan auren Jasmine da Alamin yayi tashe a Nigeria saboda yadda videos da hotunan bikin suka ringa yawo a social media, news papers da magazines. Kowa albarkacin bakinsa yake fada akanta awajen domin wasu cewa ma suke christian ce ita saboda yanayin shigarta tunda tana da aure, wasu ko kyawunta suke yabawa, wasu kuma burgesu take a ganinsu irin shigarta wayewa ce duk da tana da aure kuma musulma ce ita.

Bayani tayi sosai cikin harshen turanci  sosai domin british accents din baya buya, sai kuma ta dan yi bayani da harshen hausa wanda ba ƙaramin burge hausawa wajen tayi ba, video  mutane suka ringa yi mata da hotuna.

Bayan ta sauko daga kan stage din ne aka fara tafiyar ta motsa jiki wato fun walk, tunda suka fara tafiyar da su Basma mutane ke ta zuwa suna selfie da hotuna da ita akan hanyar, Jasmine zama tayi tamkar wata celebrity a wajen duk da akwai celebrities sosai awajen suma sai hototuna ake dasu, harda matan gomnoni da masu mukami da ma marasa mukami, yan gayu sosai an cika a taron kuma manyan mutane sunje sosai.

Bayan sun dawo daga tafiyar suna tsaye Jasmine ta gama hoto da wata da tazo suyi hoto, ta juyo zata dawo kusa da su Safna ta ji an taka mata kafa da sauri ta dagowa ta ga wanda ya takata, amma kafin tayi magana yarinyar tayi saurin cewa "Dan Allah kiyi hakuri ban kula bane."

Murmushi Jasmine tayi mata ganin ta bata hakuri tace "It's fine." Tsayawa Jasmine tayi tana kallon yarinyar dan ta gane ta, ita ce yarinyar da take kama da Mamanta wacce aka ce mata yar gidan tsohon gomnan kano ce wato Neehla Kabir.

Murmushi Neehla tayi sannan tace "Kamar mun taba haduwa koh?"

"Aa, sai dai me kama da ni," Jasmine ta faɗa hade da murmushi.

"Kina da Yaya ne ko karamar Kanwa?" Neehla ta tambaye ta.

"Aa." Jasmine ta bata amsa a takaice.
"Ikon Allah, amma wallahi ganin nake kamar na sanki." Neehla ta kara faɗa
Murmushi Jasmine ta sake tace "Kinsan daman haka Allah yake Ikonsa, maybe wata relative din tawa kika gani,"

"Hakane, I'm Neehla Kabir, it's a pleasure to make your acquittance," Mikawa Jasmine hannu Neehla tayi tana murmushi.

"Likewise, I'm Jasmine Alejandro," Haunnuta Jasmine ta saka a cikin nata suka gaisa sannan Jasmine ta bar wajen.

Tabo kafadar Basma Jasmine suka juyo suna kallonta dan tarar da su tayi suna hira suke da wani namiji, "Kin gama pictures din Celebrity?" Safna ta tsokaneta.

Murmushi tayi "Ina wani celebrity anan, I'm exhausted wallahi, Ku taho mu tafi gida," Janyo Basma Jasmine tayi amma ta cije tayi taki binta sannan ta  janyo Jasmine baya tace "Okay naji but first ku fara gaisawa da Sabeer, cousin din mu ne,"

Murmushi Jasmine tayi masa tace  "Hi."

Dariya ya danyi sannan yace mata "Hi," yana kare mata kallo yayi sannan ya kalle Basma yace "A ina kuka samo wannan Beauty din?"

Kallonsa ta yi ta dan bata rai saboda bata son irin kallon da yake mata, Hannu ya mikawa Jasmine su gaisa, ta kalli hannun nasa ta dauke kai, bata ankara ba taji ya kamo hannunta, janye hannunta tayi da sauri hade da galla masa harara, shiko kara yake baki yayi yana mata murmushi yace "Oh I'm sorry, I thought....." sai kuma yayi shiru.

"You thought what?" Basma tayi sauri tambayarsa "Matar Yaya Alamin ce fa."

"Aa, ba Nadia zai aura ba?" Yayi saurin tambayarsu.

"Kana chan kana shashancinka ta Ina zaka san wacca ya aura." Khadija ta bashi amsa rai a bace ganin har yanzu bai chanja halinsa na san mata ba.
Juyawa yayi ya kalli Khadija sannan yace "Ina ruwanki to."

"Ni wallahi matsala ta da kai kenan, daman na sani baza ka taba chanjawa ba, Allah ya shirye ka," Basma ta hade rai "Ku taho mu tafi." ta faɗa tare da jan hannun Jasmine wacce ta tsaya tana kallon ikon Allah.

Suna shiga mota Jasmine tace "Wai waye wan chan mutumin."

Khadija ce ta bata amsa "Cousin dina ne, ɗan gidan Yayan Mamana(Yayan Hajiya Saudat) ne kiyi hakuri Dan Allah, haka halinsa yake shi yasa ma bama shiri ko kaɗan."

"Ba komai, ya wuce ai," Jasmine ta faɗa hade yi mata ɗan murmushi.


Assalam Alaikum
Da fatan kowa yana lafiya, yah sanyi?
Dafatan dai kun kula da cigaban da muka samu, yanxu update baya kaiwa sati daya yay 😀 💃🏻💃🏻💃🏻.
Kar dai ku manta ku fada min ra'ayoyin game da wannan shafin domin honestly speaking Comments dinku neh ke motivating dina na cigaba da rubutu, and every single comment matters ❤️❤️.
NA GODE

Instagram @amiratuoo
Twitter @AminaUmzak
Facebook Amina Umzak
Inkitt @amiratuoo

Continue Reading

You'll Also Like

2.2M 146K 91
လူတိုင်းပါးစပ်ဖျားမှ ဇမ်းဆိုတဲ့ကောင်က အပေအတေကောင်လို့သမုတ်လဲ သူတို့သတ်မှတ်ချက်အတိုင်းသွားပါစေ.....ကိုယ့်ထမင်းကိုယ်စားပြီး သူများစကားတွေကိုထိုင်ခံစားန...
347K 22.5K 36
unexpected relationship last longer,,,, as east meets west in love....
720K 55.9K 81
It is a story about a typical Fulani Muslim girl with a perfect background and up bringing from a very wealthy family, who later meet with a destiny...
1.2M 42.1K 61
Myanmar × BL Uni/Zaw Warning..... Start Date: 29.9.2023 End Date: 20.11.2023 Photo Crd