Jasmine Baturiyya ce

By Amiratuoo

117K 8.8K 1.4K

Completed (Currently Editing and Re-uploading) JASMINE haifafiyar kasar ingila (England) ce. Ya'a ga hamshaki... More

🌷JASMINE🌷
🌷Shafi na 1🌷
🌷Shafi na 2🌷
🌷Shafi na 3🌷
🌷Shafi na 4🌷
🌷Shafi na 5🌷
🌷Shafi na 6🌷
🌷Shafi na 7🌷
🌷Shafi na 8🌷
🌷Shafi na 10🌷
🌷Shafi na 11🌷
🌷Shafi na 12🌷
🌷Shafi na 13🌷
🌷Shafi na 14🌷
🌷Shafi na 15🌷
🌷Shafi na 16🌷
🌷Shafi na 17🌷
🌷Shafi na 18🌷
🌷Shafi na 19🌷
🌷Shafi na 20🌷
🌷Shafi na 21🌷
🌷Shafi na 22🌷
🌷Shafi na 23🌷
🌷Shafi na 24🌷
🌷Shafi na 25🌷
🌷Shafi na 26🌷
🌷Shafi na 27🌷
🌷Shafi na 28🌷
🌷Shafi na 29🌷
🌷Shafi na 30🌷
🌷Shafi na 31 🌷
🌷Shafi na 32 🌷
🌷Shafi na 33🌷
🌷Shafi na 34 🌷
🌷Shafi na 35🌷
🌷Shafi na 36🌷
🌷Shafi na 37🌷
🌷Shafi na 38🌷
🌷Shafi na 39🌷
🌷Shafi na 40🌷
🌷Shafi na 41🌷
🌷Shafi na 42🌷
🌷Shafi na 43🌷
🌷Shafi na 44🌷
🌷Shafi na 45🌷
🌷Shafi na 46🌷
🌷Shafi na 47🌷
🌷Shafi na 48🌷
🌷Shafi na 49🌷
🌷Shafi na 50🌷
🌷Shafi na 51🌷
🌷Shafi na 52🌷
🌷Shafi na 53 🌷

🌷Shafi na 9🌷

2.8K 212 9
By Amiratuoo

Alamin bai sauke Jasmine a koh ina bah sai a bangaren sa. Ya na shiga falonsa ya zaunar da ita akan kujerar falon. Tafiya yayi ya dauko mata ruwa a fridge tare da kofi ya zuba mata a kofin ya mika mata sannan ya ajiye bottle a kan dan karamin table din da ke kusa da ita ko zata kara ruwan. Samu waje yayi nesa da ita ya zauna, shiru yayi yana kallonta tana shan ruwan har ta gama  ba wanda yace wa kowa uffan a tsakaninsu.

Sunkuyar da kanta tayi ba tare da tace komai ba amma a cikin zuciyarta babu irin tambayoyin da bata yiwa kanta ba domin sam bata fuskanci abinda yake faruwa ba. Ko dai Nadia ta gano abunda ke faruwa wato gayawa Jamal da tayi Nadia na dauke da juna biyu, duk yadda aka yi ma maganar ce ta fito shiyasa suka yi mata haka.

Anty Hafsat ce tayi sallama sannan ta bude kofar falon ta shigo, kai tsaye taje kusa da Jasmine ta zauna.

A hankali ta kamo hannunta  tace "Jasmine Kanwata, Dan Allah kiyi hakuri abinda su Nadia suka yi miki kinji. Nasan sai ta yi nadamar abinda ta aikata, fushi ne kawai ya ɗebe ta kasa amfani da hankalinta har hakan ta faru."

Murmushi takaici Jasmine tayi sannan ta ce "Ni fa ba da niyar cutar da ita nayi hakan ba ko dan na bata mata rai ko suna, I just wanted to help her and...." Kafin Jasmine ta karashe maganar Alamin yayi saurin tsayar da ita, cikin harshen Spanish yace mata "Ellos no saben sobre eso, No les dije.” (Ba sun san wannan zancen ba fa, ban fada masu bah)

Cikin Mamaki Jasmine ta dago ta kalle shi sannan tace "Then why did they act all rabid on me, Meyasa suka fara duka na?"

Anty Hafsat ce ta dan yi karamin murmushi sannan tace "Yarinta kenan, Jasmine, Saurayinta fa kika aura ranar da za'a daura masu aure aka daura da ke ba dole tayi kishi ba, duk da dai abinda tayi bata kyauta ba,"

Jasmine shiru kawai tayi tana kallon Anty Hafsat don itah sam bata gane me take nufi ba da an daura da ita, kamar yaya? gani take kamar wasa Anty Hafsat ke mata amma sai taga ba alamar wasa a tare da Anty Hafsat.

A hankali Jasmine ta zare hannunta daga na Anty Hafsat domin kuwa ta fahimci ba wasa take mata ba, juyawa ta yi a hankali ta kalli Alamin tare da yin wata yar karamar dariyar takaici ta gyra gashin da ya zubo mata a fuska, ta maida shi bayan kunnenta tace "A tunanina, a yanzu na gama iya hausa but sadly I am wrong ,because ni ban fahimci abinda ta fada ba."

Alamin shiru yayi tamkar bai ji ta ba kuma ba tare da ya nuna wata alama a fuskarsa ba ya juya ya kalli Anty Hafsat tare da yi mata alama da ido na ta basu waje.

Tashi Anty Hafsat tayi zata fita karaf taci karo da Jamal wanda ke tsaye a bakin kofar, dan kuwa ya dade awajen, karasowa ciki ne kawai bai yi saboda shi kansa bai san ta yadda zai yi wa Jasmine bayyani ba. Anty Hafsat da Jasmine ce kawai basu san yana wajen ba, amma Alamin ya sani.

Ganin Jamal ya shigo yasa Jasmine mikewa da sauri tayi wajensa ta rungume sa tare da sakin wasu zafafafan hawaye suka zubo akan kumatunta, dan ja da baya  tayi sannan ta dago fuskarta tana kallonsa tace "Is it true?"

Shirun da taga yayi mata ne yasa Jasmine ta dan tsorata da sauri ta ja da baya ta matsa daga kusa da shi, kamar wacce zata kone idan ta taba shi, kara tambayar sa tayi "is it true? Jamal, Abunda suke fada gaskiya ne?" Kallon da yayi mata ne ya tabbatar mata da gaskiya Anty Hafsat ta fada, ja da baya ta fara yi har sai da bayanta ya daki bangon falon, ita abun ma mamaki yake bata tamkar a mafarki ko cikin littafi daga taimako. Ita sam bata yi zaton za'a fasa auran ba domin tasa a chan UK inda ta baro ana daura aure da ciki wani zubin ma da yara a tsakani kafin a yi auren, sannan a nata tunaninta ba'a  aurar da mutum batare da yardarsa ba amma sai ta tuna yanzu fa a Nigeria take ba a United Kingdom ba, komai na nan yasha bambam da na chan.
Jamal ne ya fara matsowa kusa da ita a hankali, amma tayi saurin daga masa hannun tace "Karka kuskura ka karaso kusa da ni."

Jamal yi yayi kamar bai jita ba ya cigaba da matsowa, "Nace maka ka rabu da ni." Jasmine ta sake fada tare da jan gashinta da ya zurzubo ta ko ina baya dan har ya rufe mata fuska.

Cikin fushi harshen ta ya juye ya koma yaren espanol (Spanish) ba tare da ya lura ba "No quiro verte Jamal, Tu no eres mi hermano, porque mi hermano nunca me hará daño.” (Bana son ganinka Jamal, kai ba dan uwana bane yanzu, ɗan uwana da nasani bazai taba yadda a cutar da ni ba)
Chak Jamal ya tsaya yana kallonta idanuwansa duk sun yi ja da jin kalamanta, domin tunda suka taso, Jasmine bata taba fushi da shi har haka ba, a hankali shima yace mata cikin yaren spanish din "Jazmín Lo siento pero déjame explicarte, Sabes que nunca haré nada para lastimarte.” (Jasmine dan Allah kiyi hakuri ki bari nayi miki bayani, ki saurare ni, kinsan bazan taba yi abinda zai cutar da ke ba)

Dariya takaici tayi, idanuwanta cike da hawaye tace "Cómo si fuera Verdad, Sal por favor, No quiero verte.” (Kamar da gaske, ni dan Allah ka fita ka bani waje bana son ganinka)
Jamal banza yayi da abinda ta fada ya matso daf da ita amma kafin ya tabata ta hankaɗa shi baya, ta fara dukansa a kirji tana kuka tana ta yi magana cikin yaruruka fiye da uku dan ita kanta bata san wani yare take yi ba acikin yarukan da ta iya. Dukansa ta cigaba da yi tana kuka, ya kyaleta ba tare da yace komai ba ko ya hanata domin yasan ta haka ne kawai zata fitar da fushi da fushi da baccin ran da take ji.

Alamin da ke gefe guda a tsaya a yana kallonsu cike da mamakin yadda ta kasa bawa yayan nata dama yayi magana, dan shi a nasa tunanin ko me mutum yayi maka at-least ka bashi dama yayi maka bayani mana kafi ka yanke hukunci. Ji yayi duk ransa ya bacci ganin yadda take ta kuka ta dau abin da zafi da yawa tamkar wacce aka yankewa hukuncin zaman gidan yari, gabaki daya fuskarta tayi ja.

Gani yayi kuka nata yayi yawa tabbas idan ya barta a haka zata iya jawo wa kanta wani ciwon, hakan yasa yayi sauri ya karaso wajen da suke ya janye Jasmine din daga jikin Jamal ya rike mata hannaye tana ta kokarin kwacewa amma ta kasa saboda irin riko da yayi mata.

Fuskar ba walwala ya ce "Jamal you can leave." kallonsa Jamal yayi ya sake kallon ƙanwarsa, ajiyar zuciya sannan ya juya ya fita bai ce komai ba dan ya yarda da Alamin yasan ba yi abinda zai cutar da ita ba.

Yana fita Alamin ya cikata ta faɗa kan kujera, mikewa tayi zata tashi ya daka mata tsawa "Sit back and shut up."

Dan firgita Jasmine tayi saboda bata saba ba, da ba'a yi mata tsawa a gidansu ko fada Papá da Jamal basa yi mata duk abunda take so shi ake mata. Komawa tayi ta zauna a dan tsorace, sannan shima ya zauna a kujerar da ke kallon tata.

Sai da ya ja yan mintuna kafin yace "I never expected something like this from you Yasmine, na dauka zakiyi handling case dinnan differently ba kamar yadda Nadia tayi ba with violence."

Shiru tayi masa fuskarta a rufe da gashi domin har ta gaji da gyara shi, ganin tayi shiru yasa ya cigaba da cewa "Da kin bari an miki bayani kafin ki yanke ko wani irin hukunci, beside ke kika fara wannan mission din na taimakon Nadia fa and it's all part of it."

Jasmine dagowa tayi ta gyra gashinta sannan tahl kalle shi tace "This is ridiculous, taya Aurena da condition din Nadia suka hadu, it doesn't make any sense."

"Well, kinsan dai mu musulmai neh ko?" Ya tambaye ta bata bashi amsa ba sannan ya cigaba da cewa "Musulci ya gindaya mana wasu Sharuda Yasmine, kamar yadda ya bamu damammaki, wanda dole mu bisu domin samun zaman lafiya a duniya da kuma samu rahma a lahira."

Shiru ya dan yi sannan ya cigaba da cewa "Yasmine, Haramun ne Auran mace mai ciki a addinin Musulunci. sannan kince bakya son Nadia tai abortion wanda shima haramun ne kuma zai cutar da lafiyarta, Kinga kuwa idan ba abortion tayi ba, ba zai yiwu na Aure ta ba. Gashi mun tara mutane da yawa, jama’a sun zo domin bikin nan, ya zamuyi da su? you know I can't just call off the wedding at the last minute, mutuncin gidanmu ne zai zube."

Jasmine dagowa tayi tana kallon shi domin ta fara fahimtar abinda yake nufi, Sannan ya cigaba da cewa "Kinga ke kadai ce kika san komai akan wannan maganar, so you're our only option akan aure. nan, bayan an gama all this wedding drama idan zaki koma Cambridge, I'll divorce you, it's nothing serious."

Jin kalmarsa ta karshe ne ya sa hankalin Jasmine kwanciya, domin kuwa indai zai saketa idan zata koma garinsu ai bata da matsala da auren tunda ba auren gaske bane domin ko yan'uwanta na Spain baza ta bari su san zancen nan ba, balle Matthews Masoyinta, baza ta so yaga kamar ta ci amanarsa ba, saboda haka dole tayiwa Jamal magana akan kar ya bari kowa ya san maganar Auren nan.

"Na yarda as long as you keep your words." Jasmine ta fada tare da daukan Jarkar ruwan da ke kan karamin table din gefenta ta sha, sannan ta kara da “And, bazan tare a Gidan da zaka saka Nadia ba anan zan zauna and it’s a phony marriage no strings should be attach.”

Murmushi yayi mata yace “You have a deal, zaki iya zabar ko wani daki kike so nan sai ki zauna,” Sannan ya tashi zai fita, "Alhamdulillah." ya fada a hankali yadda shi kadai yaji abunsa, har ya kai bakin kofa ya sai kuma ya tsaya ya juyo, "Yasmine." Ya kirata a hankali.

Dagowa tayi ta kalle shi, sannan yace "Duk abinda ya faru fa ba lafin Jamal bane, bashi da zabi ne and you're our only hope in saving Nadia and my Family’s reputation, You should talk to him."

Ya na gama magana ya fita daga bangaren nasa domin zuwa ya warware sauran matsalonin.
.
.
.

Don't forget to comment and vote
Follow on
Instagram: @amiratuoo or @amiratuoowrite
TikTok: @amiratuoo
Facebook: Amina Umzak
Inkitt : @amiratuoo

Continue Reading

You'll Also Like

274K 20.2K 28
Love between a muslimah and christian✍
37K 1.3K 32
Karki kashe! Tsura ma screen din wayar tayi tana kallo, ta rasa me Rayhan yake nufi da ita sam a rayuwarta. Send me you pic I wanna see that beautifu...
1M 53.2K 46
အမိန္႔စည္း+သခြပ္႐ိုး ( ႐ွင္မႈန္းနံ႔သာ) အမိန့်စည်း+သခွပ်ရိုး ( ရှင်မှုန်းနံ့သာ) ခြင့္ျပဳခ်က္မရပဲ ငါ့အနားကထြက္ခြာခြင့္မျပဳနိင္ဘူး အသက္နဲ႔ခႏၶာတည္ျမဲေနသ...
720K 55.9K 81
It is a story about a typical Fulani Muslim girl with a perfect background and up bringing from a very wealthy family, who later meet with a destiny...