part 1 page 66-70

312 24 4
                                    

 *LABARIN RAYUWAR*
 *ASMA'U HUSNAH*


By *Maryam S Indabawa*
*Mans*

🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*

Dedicated to *My habibaty. My Ummu*

*65-70*

*Idan ka Dauki Alqur'ani Shedan yakan fusata. Da zaran ka bude shi sai ya fashe da kuka. Kana yin Bisimilla zai fadi qasa warwas. Da ka shiga cikin karatu sai ya suma ya fita hayyacinsa. Mu yi qoqari mu rinjayi Shedan*




Washe gari kamar yadda ta tashi tin asuba ta tashi.

Sallah tayi ta zauna tai karatun al kur'ani sannan ta janyo littafin ta ta kara dubawa ta jima tana duba littafin sannan ta mike ta sauka kasa. Mami ta dan kamawa abubuwa ssannan ta koma sama.

Wanka tayi ta shirya cikin wata maroon kalar doguwar riga mai dogon hannu.

Golding din takalmi da jaka ta dauka sai bakin hijab da ta saka iya kar sa kirji.

Ba karamin kyau tayi ba fuskar ta tayi fes a ciki.

Idonun ta sun kara gaske da girma girar nan tata a kwance luf luf. Leben ta sai kyallin man lebe yake.

Dakin Dady ta shiga suka karya sannan tai musu sallama ta fito ta tafi dakin Ya Buhari.

Yana zaune a gaban system ta same shi. Karasawa tayi ta ce,
"To su Yaya me ake aka tashi da sasafen nan.""

Bai kula ta ba. Dan durkusawa tayi ta gaishe shi. amsawa yayi yana dagowa ya kalle ta.

Baki ya tabe ya ce
"Baki kyau ba."

Murmushi tayi ta ce,
"Kyan kaga nayi."

"Ahakan?"
Kai ta gyada masa.

"Uhmm dauki abonki afirij."
Ya fada yana nuno mata firij din.

Gun firij din tayi ta bude. Ice cteam ta gani a ciki dayawa. biyu ta dauka ta ce,

"Yaya in na dawo na dauki sauran."
Kallon ta yayi ya ce.
"A dawo lafiya."

Sannan ta fita. Dakin Mami taje tai mata sallama sannan ta sauka kasa.

Baba yana ganin ta ya taso yayi wajen motar ya fito da ita.

Sai da suka gaisa sannan ta bude gidan baya ta shiga.

Kiran Yaa Aslam ne ya shigo dauka tayi,
Bayan sun gaisa yake cewa "amman dai tana ckul ko?"

"Aah Yaya yanzu dai zan tafk.""
"Amman dai kinsan kin makara a yadda kika fadan kina da test ko?"

"Ah haba dai!"
"Eh man tara saura minti goma. Minti goma zai kai ki ckul ne."

"Insha Allahu!"
"To Allah bada sa'a sai kin dawo ki turon pics din ki ina jira."

Ta katse wayar selfie ta dauka ta tura masa sai anan taga ashe dai da gaske Yaa Aslam yake ta makara ta tabbata nan da minti goma da kyar zasu karasa.

Addu'a take Allah yasa kar ya shiga har sai ta shiga.

A hankali Baba ya dinga jan su har suka karasa makaranta.

Lokacin tara da minti goma. Da sauri ta fita daga motar.

Hango shi tayi yana nufar ajin cikin takun kasaita yake tafiya.

Yana sanye da golding kala shadda ya saka brow kalar takalmi da hannun sa rike da waya ya kara a kunne daga gani amsawa yake.

Ba kara min kyau yayi ba. Fatar sa ta kara kyau da sheki. Gashin kansa ya kwata luf luf dashi.

Rayuwar  Asma'u Husnah 1 & 2 Complete ✔Where stories live. Discover now