SEVENTEEN

1.3K 171 13
                                    

🏵🏵🌸🏵🏵
       _RAYUWARMU A YAU!_
                      *TWELVE*
🏵🏵🌸🏵🏵

✍🏻AMMIN SU'AD
  
Shatuuu095@wattpad.....shower me with your votes and comments I'll love that, show me some love and spoil me a little..... ILYSM

Some Weeks After

Tundaga parlor nake jin yadda Zainab ke kwalla min uban kira, sake duban kaina nayi gabana Yana wani Irin mugun faduwa, Menene wannan? Me yake shirin faruwa dani kuma? Kawai se naji lema ashe hawaye ne Ke bin kuncina daidai shigowar Zainab, kallona tayi tace

Bakiji kiran da ake miki.......

Bata karasa ba sakamaakon abinda ta gani, idonta ta zaro Tana bina da kallo Tana kuma bin inda Nike tsaye da kallo, me zanyi banda kuka na shiga uku! Shi ne furucin dake fita daga baki na. Hannunta na kamo ganin ta kasa magana nace

Don girman Allah Zainab ki rufa min asiri, Wallahi is not abinda kike tunani.

Warce hannunta tayi ta bugeni tare da fadin

Ashe har Kinsan Abinda nake tunani, lallai yarinyar nan.

Ban ankare ba naji ta fisgo hannuna tana Jana, Duk yadda naso In kwace hannuna Abu ya gagara kuma nasan matsawar na fita to na kade har ganyena Amma Zainab Seda ta kaini har tsakiyar parlour kafin ta kwallawa uwar ta kira wadda Ke cikin kitchen , ai kuwa se gata ta fito hannunta rikeda perforated spoon, kallonmu ta tsaya yi ganin yadda nake kuka Tun karfina,

Meye haka Zainab?

Kalleta mummy Bakiga yadda jini ke binta ba? Kinga yadda ya Bata mata daki

Kirji ta dafe tace

Na shiga uku ni Sakinatu! Jini kuma?

Da yake gidanmu duka farin tiles ne ga jini wanda na rasa na Menene Tun dazu yake bin jikina Tun safe nasa pad anma a banza, kuka ne ya kara kwacewa min ganin mummy tayo kaina tana fadin

Shegiyar yarinya ciki kika yo a gidannan Shiyasa Kwana biu kike kiba da haske Ashe iskanci kikayi!

Ya hayyu ya kayyum! Nikam Wacce Irin rayuwa Allah ya tsara min, Daga Wannan se wannan, hannuna na kwace don ni daya nasan yadda nake ji ga Ciwon mara me axaba, kafin na kai kofa ta saka Zainab ta bini ta kamo ni, hayaniyar da ake yasan jawo hankulan sauran mutanen gidan, Feey da Salma dasu hafsa suka fito suna tambayar abinda Ke faruwa nan mummy tace ai ciki nayi shi ne na zubar asirina ya tonu

Mummy Wallahi ba Abinda kike tunani bane, Wallahi ban taba yin wani abu ba

Rufe min baki don ubanki, har Kinsan Abinda ake a samu ciki shegiya

Haka na dinga kuka ina Rantsuwa amma baki daya zagina suke zan bata musu family name, addinin karya nake. Salma dake ta kallona kuma batace komai ba se lokacin tace

Mummy ku kyaleta me outcast ta sani bare har tayi ciki?

Zainab tayi caraf tace

Illar college kenan kije university kiga yadda yara ke iskanci, Nanayen ce bata san komai ba....

Zainab kuji tsoron Allah, Kada Ku dauki alhakin yarinyar nan.....

Itama katse ta tayi tace

Idan bazaki kalla ba koma daki Amma babu shegiyar da ta isa ta bata mana suna a gidannan.

Hayaniyar su tasa Abba da Anty Binta sakkowa, ganina Inata kuka yasa Abba karasowa gurin yace da mummy

Sakina Meye haka? Me ya sameta

Saboda makirci Irin na mummy kawai se mukaga tana kuka tare da fadin

Adams yanxu duk kokarin ganin tarbiyar Hassanah ta tafi daidai Amma yarinyar nan da cikin shege zata saka min?

RAYUWARMU A YAU!Dove le storie prendono vita. Scoprilo ora