Chapter 8

1.3K 80 0
                                    

🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

             *ZYNAH*

(An Interesting Love Story 2017)

By Aisha Muhammad (Mzz Daddy 💋)

QUOTE:- "Some people pass through our lives in a shorter time frame than we had hoped to teach us things they never could have taught if they stayed".

     _I dedicate dis page to my lovely aunt *Anty Sadiya(Iyan Ummima)*._

                 0⃣8⃣

     Duka familyn *ZYNAH* ne zaune a parlour  suna jiranta ta sauko sutafi airport, sunyi zaman minti uku sai gata ta fito sanye da blue jallabiya tayi rolling kanta da pink veil. Tayi kyau sosai sai faman  jan  trolley takeyi. Uncle Yusuf ne yaje ya taimaka mata suka sauko shi ya wuce da bag din mota itakuma tazauna kusa da Daddy tana gaishe su duk suka amsa sannan Momsie tace"kingama shiryawa,baki manta da komai ba","eh ban manta ba".

     Nan suka mata dan guntun Nasiha sannan suka fito suka shiga  mota. Uncle Yusuf, Islam da *ZYNAH* mota daya sai driver ,Momsie da Daddy suma mota daban da driver dinsu. Suna fitowa se ga Humaira, parking tayi suma sukayi parking tafito taje ta gaida su Momsie sannan ta koma motansu  *ZYNAH* ta gaida Uncle Yusuf ya amsa mata  suka kama hanyar  Murtala Muhammad  Airport suna  zuwa Uncle  Yusuf  yaje ya musu processing komai duk suna zauna kafin a kira su.

     Fifteen  minutes  to  twelve  ido yafara rena fata nan Humaira ta rungumeta tace" take care of urself wen u get der " kwallan da take boyewa ne sukayi nasarar zubawa tace "i will Bestee" sannan suka saki  juna ta rungume Islam tace" take care of Daddy nd Momsie ok" tace "ok sis" sannan taje wurinsu Daddy ta rungumesu tayi musu sallama  itada Uncle Yusuf suka shiga  departure . 12 on dot aka soma kiran suna duk suka shiga jirgin suka zazzauna. Jirgin be tashi ba sai 12:25pm , sai alokacin su Daddy  suka koma gida cike da kewar ýarsu.

     Yau an wayi gari en gidan  Allah Sagiru Fillo sun tashi cike da farin ciki da murna saboda yau mahaifinsu zai dawo daga dogon tafiyan da yayi zuwa Ghana amma daga Lagos jirginsu zai tashi zuwa Kaduna.

     Ummi da Ammi ne a babban kitchen din gidan tareda masu aiki ta fannin girke girke, sai girki  sukeyi, su dora  wannan  su  sauke  wancan  a yayinda Minal da Basma ke kaiwa dinning  suna  jerawa, kowa kaga  fuskanshi zakasan suna cikin  tsantsan  farin  ciki  sai  kai da komawa sukeyi.

     *ASHRAF* ne ya shigo fallon da saurinshi yana kallon agogon  hannunshi kirar I-watch na kampanin I phone wanda ana iya kira koma ayi receive  dashi. Su Minal yagani zasu  fito suka gaidashi  ya amsa tareda tambayarsu "ina  su Ummi" Basma  tace "suna babban kitchen" nan ya nufi kitchen din  yaga sunyi busy sunata aiki ya gaishe  su suka amsa.

     Cike da mamaki Ummi ke cemasa "Babana har yanzu baka tafi dauko Abbanku ba? kai da na cema 2:00pm jirginsu zai sauka". Wlh Ummi na makara ne bantashi da wuri ba amma yanzu zan wuce koma In Sha Allahu i will meet  up". Ammi tace "a dai yi  driving a hankali banda  gudu  kaji  son" yace "toh  sai na dawo tareda fita daga kitchen din ya nufi parking lot ya dau motarsa sai Kd.

     Tsaki yaja ya kalli agogon  hannunshi  yasake  jan wani tsakin  kaman tsaka ganin har 1:42pm tayi amma  hold up din Kaduna ya rikeshi, shi  dinda yake sauri saboda ko kadan baya son Abbanshi yayi  zaman jiranshi saboda ba girmanshi  bane, yafi son shi yaje ya jira akan ace Abbanshi  ne ke jira.

     A hankali motocin ke tafiya har yasamu hanya ta bude sannan ya fara sharara gudu saboda ya kai kan lokaci. Yana isa yayi parking tareda duba lokaci yaga 2:19pm da sauri ya fito ya shiga daga ciki sai dube dube yakeyi ko zaiga Abbanshi amma ba alamunshi, nan yaje ya tambayi wani security guard ko jirgin  Lagos ya sauka  yace mishi  a'a. Ajiyar zuciya yayi tareda godiya  sanna ya nemi wurin zama ya ciro wayanshi yana latsa wa.

Zaman 10min yayi sannan yaji ana anouncing  arrival din jirgin Lagos , kallon time yayi yaga 2:34pm, tsaki yayi cikin zuciyanshi  yace "Nigeria  will neva  change, komai sai an mishi African time , jirgin da yakamata ya sauka tun biyu amma sai biyu da rabi , yanzu da mutum yana da  appointment  haka zaiyi miss, i  don't  knw wen Nigeria will change"(Ni ko nace in zaka iya ka canza mana).

     Tashi yayi ya tsaya inda yasan Abbanshi zai iya hangoshi sannan yafara dube2 can ya hango shi da trolley  din tura kaya lode da kaya a kai, da sauri yakarasa  wurin shi ya rungume mahaifinshi  tareda da fadin "welcome home Abba","thanks son","i miss u very much Abbana","I miss more son". Sannan suka saki juna cike da murnan ganin juna.

     "Erm, *ASHRAF* inaso ka kai kayan nan mota, akwai wanda nakeso nagani wai yana zuwa yanzu, nan da fifteen  minutes  zamu gama abinda zamuyi sai muwuce". "Ba damuwa Abba, bari na tafi da kayan","yawwa". Ya kai kayan  mota ya dowa ciki saboda Abbanshi be san ta inda yayi parking  ba. Wayanshi yayi ringing ya tsaya  ya dauka Sameer  ne mai kiran, nan yasa wayan a kunne sannan yaci gaba da tafiya yana waya.

     Tafe take ta bude jakan hannunta kaman wacce ke neman wani abun arziki nan ko cewing gum takeso ta ciro. Daga sama taji tayi karo da mutum jakanta ya fadi duka kayan tarkacenta  suka zube, ita bata yunkura da niyyar kwashewaba haka zalika kuma bata dago ba ballantana taga wanda ya buge, shima kuma haka be kwashe ba koma be dago ba. A zuciyanta  kuwa  cewa take "waye wannan arrogant person din da ya buge mutum kuma ko sannu gashi kuma beda niyyar dauko abunda ya zubar" shikuwa a nashi bangaren cewa yake "wannan kuma ji kayan da take yawo dashi saikace yarinya kuma wai ta tsaya kikam kaman an shuka bishiya maimakon ta kwashe". A tare suka dago da niyyar balbale juna amma me wani shock sukaji gabayamsu marar misaltuwa, a zuciyanshi ya "Wat a beauty" itama tace "ashe dai kyakyawa  ne shiyasa yake da girman kai amma zan gyara mishi zama".

     Cike ta tsiwa ta bude baki tace "Mallam hala sanda kake school ba'a koya maka five magic words bane da zaka bige mutum amma koma ko sannu bare a je ga maganan tattara abunda ka zubar" shiko ba abunda yakeyi sai kallon red lips dinta, sai da ta gama sannan yayi murmushi yace " Mallama ba'a koya min ba ko zaki koya min" bata kai ga bude baki ba ya hango Abbanshi zuwa kawai sai ya wuce, a hankali tace "so arrogant" yajiyo yace mata" i  heard u" sannan ya wuce ,sosai mamaki ya kamata saboda batayi  zaton zaiji ba kawai sai ta tsugunna ta fara tattare kayanta.

     Muryan  Uncle Yusuf  taji yana cewa " *ZYNAH* keda nace kijira in nemo taxi ina kika shiga" tace "Uncle na shigo ne saboda in zauna dan nagaji sai kuma wani ga bugeni shina na tsaya dauke jakata","naji muje me taxi na jira a waje" nan suma suka fita suka shiga taxi din tareda cema me taxi din "Zaria zaka karasa damu" yace " yallabai saidai na kaiku tasha inda zaku  samu  motan Zaria","ok muje ba matsala". Nan ya kaisu tasha suka shiga motan Kaduna to kano amma zasu sauka a Zaria. *ZYNAH* cikin ranta tace "tunda nake ban taba shiga  mota haya ba amma yau Allah Allah kawo ni na shiga duk na  takure kuma wai kudi  za'a biya a hakan".  

     _Toh readers  yau ga *ZYNAH* a hanyar Zaria Zazzau, ku biyo  danjin  yanda wannan lbr zata kasance nan gaba_

     _Mzz Daddy💋✍🏻✍🏻_

ZYNAHWhere stories live. Discover now