*_______________________________________*🚨🚨GIDAN MIJINA🚨🚨
Short story
Story & written by
MAMAN AFRAH
Page
40🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
"Ba su kad'ai aka kai ba gyatumarsu ta je dasu shi ne ta shuka rashin arzik'i ta taho ta baro su a can"Ummulkairi ta ce tana kanne ido d'aya.
"Bangane ba ita Aysha ce ta je ta yi rashin mutunci" Kb ya ce da mamaki.
Aysha kwa da ke tsaye sakin baki ta yi galala tana kallonsu."Eh mana har fa zagin Hajia ta yi"
"Zagi "ya fad'a a zafafe.
"Wlh kwa dan Hajia har da hawaye ta yi na takaicin zagin da Aysha ta mata...
Ai kafin Ummulkhairi ta kai aya ya yi kan Aysha kamar zai kai mata duka, ta in da yake shiga ba ta nan yake fita ba, Aysha tana so ta masa bayani ya k'i saurarenta, Fauzy ma da zata yi magana ya dakatar da ita kai a tak'aice sai da Kb ya zagi Aysha ta uwa ta uba .Aysha kawai hawaye ke zuba a idonta itama Fauzy ba, a barta ba a baya dan tana da wayo sosai kuma tasan ba,a kyautawa mahaifiyarta ba, ta kuma san Mamanta bata zagi Hajia ba tana so ta yiwa Abban bayanin yadda aka yi amma yaki ya saurareta. Ummulkhairi kwa ranta fari kal ta had'a ta ji dad'i dan da sanin Hajia ma ta taho ta yi had'in wannan.Wannan shi ne abin da ya janyo Kb ya sakeni lallai namiji duk hak'urin da nake k'unsa a cikin gidansa amma bai gani ba sai da ya ci wa iyayena mutunci!
Da asuba bayan na yi sallah na yi azkar, karamar trolly na d'akko na sanya kayana a ciki tare da abubuwan da zan buk'ata, fitowa na yi na je d'akin hindu mai kula min da yara na sanar mata zan tafi ta kulamin da yara na, na dauki kud'i masu yawa sosai ta ji babu dad'i jin sakin da na ce mata yaa shiga tsakaninmu. Haka na shiga d'akin yaran na gansu suna ta barci abinsu, na fito jin hawaye na neman kufce min ni kuma bana buk'atar yin kukan yanzu. Sashe na na dawo na dauki jakata da akwatin sai wayana, fitowa na yi na bude kofar na fita mai gadi na ta bani hak'uri domin ya san ba lafiya bace za tasa na fita da akwati da sassafen nan kuma ba tare da yaro ko d'aya ba.
Ina fitowa bakin titi na samu napep dan lokacin gari ya yi haske sosai akwatin na sanya a xiki nima na shiga na zauna na fad'a masa in da zai kai ni. A dede kofar gidan mu nasa ya tsaya na biyashi kudinshi na kinkimi akwatina na shiga buga kofar gidanmu, wata iya salame da suke zaune tare da Umma a gidan kanwar maman Ummance ita ta bude min kofar gani na da akwati yasa jikinta yin sanyi, jakata ta karba ni kuma na shigo da akwatin Umma dake shara ta yarda tsintsiya ta tsaya fuskarta da tsahin hankali tana kallona, jikina ne ya k'ara yin sanyi ganin damuwa k'arara a fuskar Ummana. D'aki na shiga da akwatin na ajiye, haka muka zauna jugum jugum na fad'a musu duk abin da ya faru ina fad'a ina kukan takaici dan gaba d'aya sai nake jin kamar ma yanzu ake min duk abin da aka mini.
BAYAN WATA UKU
Lokacin har Aysha ta yi iddah, dan haka kawu habibu yasa ta yi jamb kuma Allah ya taimaketa ta ci aka nema mata admission a B. U. K nan take Aysha ta fara karatu babu kama hannun yaro, dan dama tana son karatu gata da bala, in k'ok'ari sannan kuma ta hadu da k'awaye wayayyu suke koya mata komai na rayuwa dan idan ka ga Aysha ba zaka ganeta ba. Kamar ma ba ita ta haifi yaranta ba ba wanda zai ganta yace ba budurwa bace. Ta kwantar da hankalinta tana yiwa y'ay'anta addu, a tana karatun ta hankali kwance. Sai dai samari da manyan Alhazai da ke mata tururuwa ita kuma tana sallamarsu dan babu sha, awar aure a ranta yanzu dan kayan d'akinta ma tuni aka kwaso ta sai da wasu wasu ta jerawa Ummarta .Sannan ta kan sari takalma da pad ta mata da kayan shafa tana tafiya dasu makaranta tana siyarwa abinta.
YOU ARE READING
GIDAN MIJINA
Short StoryLabarin wata wacce ta tsinci kanta a ckn uƙubar miji a gidan aurenta