GIDAN MIJINA

63 1 0
                                    

🚨🚨GI DAN MI  JINA🚨🚨

Story &  Written by

MAMAN AFRAH

Page NINETEEN & TWENTY

Wai humaira me kike ne a daki sai kira nake Amma baki fito ba"umma tace daga tana rike da buta.

"Ki hkr umma na amsa Kaya nake linke wa Gani Nan zua."humaira tace tana fito wa daga Daki gabanta na doka wa da karfi.

"Ki kula kizo ki yi alwala,ki yi sallah"umma tace tana fara tata alwalar.

"To umma na"Tace tana sauke wani numfashi, ta dauki buta ta nufi bayi tana mai gode wa Allah da umma bata tamba yeta me yasa ta dade a hanyar islamia ba.dan bazata boye mata komai ba ita kuma bataso ran ummar ya baci tun da dai matukar zata fada mata dole ranta ya baci ita kuma haka ne bataso.

  Tun daga wannan rana kb kullum sai ya tare humaira sai dai kuma bai kara yinkurin taba mata Yatsa ba,bare Hannu ba ko kuma wani abu mai kama da wannan.sai dai ita bata mishi maga na sai dai ta yi murmushi idan yana mata maga na amma kuma bata wani bata lokaci take tafia.

Yanzu ta saba dashi sosai in ma ba scul tana shiga damua in bata Ganshi ba.dk da ba gane ko kuma fahimtar Kalamai da yake gaya mata take ba.a haka har ta shiga s.s. two  domin lokacin ta gane manufar kb ta saba da komai da yake gaya mata wani lokaci tana maida masa marta ni. domin sabo da soyay ya ne suka shiga zuka tansu.dk da har time din gaba daya bangaro rin biu basu gane meke farua ba.illa dai ummar humaira data gane yarta na tuna ni da kuma kadaice wa ita kadai,haka ne yasa ta fara zargi kota fara kula saura yine basu da masa niya.haka ne yasa ta kara sa ido Kan tarbi yarta domin ta kai wani mataki da maza zasu ke kai hari na nemam luv a gunta.ta girma sosai halittar ta,ta kara fitoa diri kira da dk wani abu da mace zatai takama dashi in ta kai baliga.

Kb da yake so ya auri aysha sai ya mai da hankali domin yanaso ya samu wani abu da zai dogara dashi wanda in ya tashi aure za,ace yana da sa na,ar yi tun da ba wani karatu mai zurfi ya yi ba bare ya samu wani aiki da zai dogara dashi.haka ne yasa ya nutsu sosai dan yanaso dad ya dorashi kan kasu wanci dk da Hajia bazata Amince ya auri yar talaka ba amma yana da tabbaci dad zai mallaka masa komai yakeso bare ma dad bai Kin talaka.damuar da yake  da ita itace ko iyayen aysha zasu Amince masa ya aureta?a yan da yakeso dan shi ko karatu baiso taci gaba daga na sec.kuma ya lura abum dunia bai damesu ba ya lura da haka a gani na farko da ya musu.

So ya shiga Rai da zuciar aysha yay kane kane dan a yan da take ji yanzu zata iya amince wa kb da aure in ta kammala sec.yanzu ji take dk wani buri da take dashi na karatu ya kau, so take ta auri kb kalamai da yan da ya gina kanshi a günta Suna matukar tasiri a zuci yarta.kullum kalamansa "aysha ki amince da aure na bazaki taba danasa ni ba,aure ne da zaki yi alfahri dashi zaki rayu cikin farin ciki da kanciyar hankali,zaki zauna karkashin kula wata rayu war da babu bakinciki kunci ko takaici.Yayanmu zasu yi alfahri damu a matsa yin iyaye na gari tabbas zasu ce Sunyi dace.aure ne da babu yaji bare wani saki ni babu saki a tsari na,domin nima bazan taba iya rayu wa babu ke ba aysha ke kadai mata ta har karshen rayu wata,bani da buri na auren mace sama da daya🙊 Zana dauki iya yenki tamkar mahaifa na zan daraja su suma zasu yi alfahri da aurenmu"wannan kalami su suke sa aysha ta ji dk dunia babu wani namiji da ya dace da ita face kabeer wannan ne kalaman da suka yi tasiri akanta dan ko Bata yi niyyar tsaayawa ba In ya ya fara jero kalamai yanzu zata tsa ya tana murmushi.domin yanzu an rage musu lokacin tashi a islamia dn haka in ta taso suke shan hirar su Ita da kb dn ko a gida ba tace an rage musu lokaci ba sai dae kb ya tare kullum.so ya  mata  ga kuma yarinta dake dawaini ya da ita.domin kb ya fita shekaru da kuma bude war Ido.

A haka Suna tare a boye har dai humaira ta shiga s .s tree lokacin sun kara shakuwa sosai da Juna.kullum maga nar kb bata wuce bazai taba dena sonta ba,itama kuma a nata bangare haka ne.sai dai har yau bata taba karbar wani abu a gunsa ba,komai ya bata kin karba take har waya ya bata suke waya a boye amma taki karba dk wani abu daya bata taki karba sai yace zai a dan a mata a gunsa har sai Ranar da sutka yi aure zai bata.ta Kanyi murmushi amma bata ce masa komai.a  time dn ne dady ya bashi ku dade ya kuma hadashi da abokan kasu wanci tuni harka ta bude ya bude  shago a kasuwar kwari ya cika da Atamfofi shand do di lesi na d.s
Hajia ta yi murna sosai da natsu war da danta ya yi bata Sän aure yake so ya yi ba shisa ya natsu ya kama zuwa kasua😀
Baya n wata uku
***********************
Hajia ta je kaduna gun kan warta zuminci da ta tashi taho wa ta taho da yar kan wartata ummul khairi ,dn bata da ya mace.ummul khairi bata Jim maga na ko kadam ga raina na gaba sam sam bata da tarbi ya.ta kammala karatu n ta na sec.

Tun data dawo ta dora rai a son kb dama can tana son sa amma bata masa ba.ta shir ya gaya wa hajia kome zai faru ya faru.

Yau ya kama alhamis babu islamia humaira ta shir ya tsaf domin zua gun kaka nimta ta gaishe dasu.fitar ta ke n n wata mota ta faka a kofar gi dansu,wasu yan mata ne su biu suka tsa ya suka kare wa gi dan kallo na wulakamci Suna wani yatsi na fuska.shiga suka yi ciki ba tare da Sun yi Koda sallama ba,umma atika dake Shan rake tana tara cito a plate ta dago tana bin su da kallo na mamaki.
"haba yan mata ya kuka shigo mana ba sallama"umma tace tana murmurshi .

"Nan bai mana kama da Inda mutane zasu rayu ba,bare har mu yi sallama yafi kama da Inda karnuka,ko dabobi  zasu Zauna amma ba Mutane ba"1 daga ciki tace Tana cire glases dn dake Ido Tana wa ko ina kallo na banxa.

"Bama wannan banzar yar taki da take min hira da saura yina kullum a lungu,yau nazo ko ni ko ita"dayar tace tana hararar umma.

"Hira da saura yinki kuma a lungu"umma tace cike da mamaki tana tashi tai jifa da plate mai sosu war rake ,ji tai kanta na wani iri sauri ta yi ta rike bango dan kar ta fa di kasa.............

😍😍😍😍😍🥎
بسم ا

GIDAN MIJINAWhere stories live. Discover now