ZYNAH

By Ishamoha

77.7K 4.7K 61

Here is a story of a teenage hausa girl Zynah who happens to come from a wealthy nd peaceful family but was h... More

Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63

Chapter 36

1.1K 62 2
By Ishamoha

🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

             *ZYNAH*

(An Interesting Luv Story 2017)

By Aisha Muhammad (Mzz Daddy💋)

*BAIWA WRITER'S ASSOCIATION*

QUOTE:-"Some people are so lucky that even after hurting they get so much love and some are so unlucky that even after giving so much love they always get hurt."

                3⃣6⃣

     Su na fita daga dakin ba dadewa Humaira ta tashi daga barci, zama tayi kan gado tana tunanin *ASHRAF* dan koda ta kwanta seda tayi mafarkin shi, hango wayan *ZYNAH* tayi akan desk dinda take karatu,mikewa tayi taje ta dau wayan ta bude tashiga gallery tana kallon hotunan *ASHRAF* dukda ba wani wayane dasu ba, bude wayanta tayi ta tura hotunan sannan ta dauki numbern *ASHRAF* dayake tasan sunan da *ZYNAH* tayi saving dashi, seda ta gama copying din number din sannan wani zuciyar yake ceme ta "abun nan da takeyi hanya ya dace, wacce bstfrnd dinta keso shi itama ta fada tarkon sonshi", se wani zuciyan kuma yace "toh ai bani nasawa kaina sonshi ba, Allah ne ya doramin sonshi kuma ba yanda na iya dole one way or d other in samu hanyar da nabi na mallake shi".  Haka tayita sake sake a zuciyar ta har taji karan murda kofa wanda ya tabbatar mata da *ZYNAH* ce, a jiye wayan tayi a daidai lokacin da *ZYNAH* ke shigowa, tace "bestee na barki kadai koh", Humaira ta kalleta tace "a'a ai banma dade da tashi ba, daga ina", "wlh nida *ASHRAF* muketa hira tun dazo, yaki barina na shigo gida, seda nace mishi sallah zanje nayi",  Humaira a zuciyarta tace "kedai kenan", amma a fili cewa tayi "wai ni in tambaye ki, wannan relationship din tsakanin keda *ASHRAF* na wa da kanwa ne koh na budurwa da saurayi", murmushi *ZYNAH* tayi tareda zama sannan tace "za'a iya cewa duka, meyasa kika tambaya?", "saboda narasa gane takan ku, shi yaki yafito fili ya gayamaki yana sonki, se wasa da hankalinki yake kikuma kinata biye mishi gashi kema har kin fada tarkon sonshi", dariya *ZYNAH* tayi ta mike tana kokarin cire kayanta jikinta tace "maybe he's waiting for d ryt tym saboda he doesn't want to rush tins, bt as for me i will wait for him no matter hw long it will take", "himmmm ke a ina kika tabajin an jira na namiji, ba namiji bane yake jiran mace ba", itadai *ZYNAH* gudun dogon zance yasa tace "kinga an kira sallah magrib bari muyi sallah se muci gaba da hiran", sannan ta fada bathroom dan tayi wanka.

     Da daddare bayan isha duk suka hallara a dinning gaba dayansu harda Abba da Uncle Yusuf dayake shima anje an kirashi, sun fara ci sukaji sallaman *ASHRAF* wanda rabonshi da yazo ya zauna aci abinci gabadaya harsun manta, zuwa yayi yaja kujeran kusada Uncle ya zauna ya dauki plate ze zuba abinci, Abba ne ya kalleshi yace "yau kuma meka tuna kazo nan?", murmushi kawai yayi sannan yace "kawai dai yau ina sha'awan zama naci abinci anan ne", kada kai kawai Abba yayi yaci gaba da cin abincin shi, Ammi tace "zaka fada gaskiya ne, miskilan yaro kawai", dayake yaje ya bata lbrn *ZYNAH* kuma ya fada mata ita yakeso amma be fadawa *ZYNAH* ba tukun se nan gaba, Minal ma kallonshi tayi dan tasan dalilinshi na zuwa cin abincin yau, Gimbiya kuma duk sanda tayi nasarar dago kai, toh se sun hada ido da shi. *ZYNAH* ta riga kowa tashi da sunan ta koshi, wanda tana tashi ya ajiye spoon shima wai ya koshi, gabadaya wurin kallonshi akeyi saboda ko spoon biyar be ciba, ganin yanda ake kallonshi yasa yagane ya tafka shirme, se yayi sauri ya wayance yace "abincin yayi yaji shiyasa, bazan iya cin dayawa ba", ba karya abincin da yaji amma tun farko besan da yaji ba seda sarauniya tace ta koshi. Ganin tayi hanyar daki yasa shima yayi waje, dakin shi ya shiga, yana shiga ya dauko wayanshi ya kirata, murmushi tayi tace "wannan anyi jarabbabe, sekace ba dazunnan muka rabuba", dauka tayi tace "hello", yace "meyasa bakici abincinki sosai ba, ni na takura miki koh?", "a'a wlh baka takuramin ba, kawai dai na koshi ne", yace "Ok, zanje wurin Sameer yanzu ina dawo zan kiraki karkiyi bacci", "toh ba zanyi ba", sallama sukayi suka kashe wayan. Bashi ya dawo ba se karfe goma, koda ya kirata tayi nisa a barci saboda haka bata dauka ba, Humaira kuma tana ganin call din amma takasa dauka tace mishi tayi barci.

*WASHEGARI*
     Yau Monday *ZYNAH* da *ASHRAF* zasu koma school for second semester, Uncle Yusuf kuma ana can ana jiran amsa daga wurin Minal, ita kuma kwakwalwarta duk yagama daburcewa dan harga Allah batason ta amince mishi daga baya kuma ya rabu da ita ya barta da jinyan ciwon zuciya. Sungama shiryawa *ZYNAH* da Humaira suka fito waje, Ummi suka gani dukae tsugunna suka gaisheta ta amsa musu tareda cewa su shiga wurin Ammi su gaishe ta se suzo suci abinci,amsawa sukayi da toh, sannan suka tashi, part din Ammi suka shiga, Basma ce a parlour tana shan grape tana kallo _keeping up with the Kardashians_ da sauri Humaira ta karasa ciki tace "Basma kema Kina kallon wannan program?", Basma tace "sosai kuwa, har banso yana wuceni, kefa", "ina kallo, dashi da Wags Miami da Life of Kylie, programs din akwai dadi", "sosai", Humaira tace "cikin Kardashians wa kikafi lyk?", Basma tace "gaskiya nafison Kourtney", "nikam nafison Kylie", haka sukata hira *ZYNAH* ganin Humaira batada niyyar tashi yasa taje wurinsu tareda tambayan Basma ina Ammi,  tace musu Ammi na daki su shiga,  tashi Humaira tayi suka shiga dakin Ammi suka gaisheta da fara'arta  ta amsa musu tareda da tambayan su sun kwana lfy  sukace eh, tareda ita suka fito dan itama wurin Ummi zata shiga.

     Suna shiga sukaci abinci, sannan suka fito, dama *ASHRAF* su yake jira su tafi tare, shiga motan sukayi *ZYNAH* na gaba Humaira na baya suka gaishe shi ya amsa tareda juyawa wurin *ZYNAH* yace "kin saba alkawari jiya, nace karkiyi bacci shine kikayi inata kira baki dauka ba", hakuri tashiga bashi dan taga missed call dinshi, cewa yayi ya hakura daga nan suka shiga hira jifa jifa suna saka Humaira ciki, da haka har suka isa school, kallon school din *ZYNAH* tayi dan koba komai tayi miss din school din, Humaira ma school din ya mata kyau a haka har ya isa inda zeyi parking, yana parking suka fito yace "kince 12:00 zaki fito daga lectures koh", tace "eh", "ki jirani in kin fito, ni sai 1:00", "ok ba damuwa" wucewa sukayi shima yabi hanyarshi, tafiya sukeyi *ZYNAH* na nunawa Humaira department daban daban daga sama taji ance mata "hello, baby girl, long tym no see", dago kai tayi taga wanda tafi tsana a rayuwarta ne a gabanta wato KB, cikin daga murya tace "wai fisabilillah se yaushe zaka hakura ka kyalle ni ne?", kallon wurin yayi yaga ana kallonsu dukda ba mutane dayawa yace "keep down ur voice before u embarrass me here", tsaki tayi taja hannun Humaira suka wuce, shikuma ya bita da mayataccen kallon wanda shikadai yasan fassaranshi. Humaira ce ta tambayeta "waye kuma wannan", "shine KB", Humaira a zuciyar ta tace "well he's nt looking bad, kyakyawa ne sedai baki ne kuma bakinshi me kyau", nuna mata wurin zama *ZYNAH* tayi tace "zauna nan kafin infito,  in kuma kinaso ki zagaya school din toh, amma dan Allah kafin sha biyu ki dawo nan kar in saura nemanki", "jeki kawai karki damu",  shiga lecture hall *ZYNAH* tayi inda tana shiga Shaheeda tayi wani ihu tareda zuwa ta rungumeta tace "oohhhh my babe i missed u a lot", dariya tayi tace "i missed u more, ykk kwana dayawa", "wlh ina nan fyn, tun ran Friday nadawo, nazo hostel dinku, kinsan Ashanty bata pata lokaci wurin dawowa, saboda haka ita kadai nagani, take cemin wai kince mata ba'a school zaki sauka ba wannan karon", "eh ba'a school na sauka akwai lots of gist, amma se anjima na hango wannan mummunan lecturer nan zuwa", ai kuwa bata gama rufe baki ba segashi ya shigo duk suka nema wuri suka zauna dan baya wasa wannan lecturer, student ma Mr No Nonsense suke kiranshi.

     Minal ta fito zata wurin dinki ta hango Uncle Yusuf tsaye shida gate man suna hira harda dariya, sosai ya burgeta ganin yanda yake dariya gashi kuma beda girman kai tunda har ya iya ya tsaya yana hira da mai gadinsu, sauke kai tayi taci gaba da tafiyanta wanda batasan cewa tun fitowarta ya hango ta ba. Har ta kai bakin motanta taji yana mata sallama ta bayanta, amsawa tayi tareda juyowa tana fuskantar shi, yace "se ina?", "wurin dinki zani", "koyo kikeyi ne?", "eh, nama kusa kamallawa", "okkkk toh ya maganan mu", sunkuyar da kai tayi tana murmushi tace "ka bari inna dawo, ", shima murmushin yayi ganin yanda kunya ya lullubeta yace "wannan kunyan kuma fa, koda yake gado ne, na Fulani, an sansu da kunya, karfe nawa zaki dawo", "se 6 zan dawo", "toh ai kafin lokacin na kuma dan 4 zan bar nan, amma ba matsala ban contact dinki, inyaso na kiraki", ciro wayan yayi ya bata tasa mishi number nan ya kirata saboda ya tabbatar ba wrong number bane, kuma yaji ringing din a jakanta yace "number na kenan kiyi saving dinshi", tace "toh", sannan ta shiga motanta, kwankwasa mata glass din motan yayi ta bude yace mata "drive carefully", murmushi tayi tace "i will" sannan ya bata hanya ta tada motanta me gadi ya bude mata gate, ta fita shikuma be wuce ba seda yaga fitanta sannan ya wuce cikin gida dan yayi wanka.

     Humaira ganin zaman ya ishe ta yasa ta tashi danta zagaya, ta Kai wurin wani  café taji ana kiranta da "jimana dan tsaya", juyowa tayi dan taga wani dan iskan ne ke mata irin wannan kiran, mamaki ne ya kamata ganin KB a gabanta, murmushi yayi yace "kin gane ni, nine na dazun da...... ", bata bari ya karasa ba tace "naga neka menene me kakeso?", "kinga ba wani abu bane illa inaso muyi wata magana dake", "ba damuwa inajinka", "mudanje can mu zauna, dan maganan me tsayi ne", ba musu ta bashi suka zauna kan wani benci yace "ko baki fada ba nasan ke kawar *ZYNAH* ce shiyasa naga ke yadace in nema muyi magana ta fahimta dake", kallonshi takeyi ba tareda tace komai ba yace "sanda *ZYNAH* ta koma Lagos hutu nasa abinta har can wanda wannan yasa nasan ku kawaye ne", cike da mamaki tace "ka bari aka bita saboda me?", "nasan kinsan komai a kaina dan haka bazan boye miki komai ba, ada nayi sha'awar kawarki, kuma alokacin plan dina be wuce in kawar da kwadayina a kanta ba, amma yanzu d story has change sonta nakeyi kuma da aure", "se kuma aka ce maka zata auri watsastse irin  ka", dukda kalman ya mishi ciwo amma seya danne zuciyarshi yace "kinga ni sonta nakeyi ba komai ba, kuma abunda yasa kikaga ina miki magana yanzu saboda nasan kema Kina son *ASHRAF* ko nayi karya?", kasa bashi amsa tayi se dai mamaki da takeyi ya akayi ya sani, ganin bata bashi amsa bane yasa yasan cewa tarkon da ya dana yafara kamuwa, kallonta yayi yace "saboda haka indai zaki bani hadin kai in samu *ZYNAH* toh ni namiki alkawarin samun *ASHRAF*", dago kai tayi tace " ta yaya", "kedai bani hadin kai tukun sena fada miki abunda zamuyi", seda ta tsaya tayi tunanin hanya bataci amanar kwance ba, amma saboda idonta ya riga ya rufe bata gani se tace mishi taji ta amince, wani munafikin murmushi yayi yace "shikenan ban number ki, anjima zan kiraki semuyi magana", ba musu ta bashi number yayi save bayan ya tambayeta sunnan ta, sannan ya tashi ya bar wurin bayan yamata alkawarin ze kirata. Ita kuma tana nan zaune a wurin tana tunani sannan ta tashi ta koma inda take jiran *ZYNAH* .

     _Mzz Daddy 💋✍🏻✍🏻_

Continue Reading

You'll Also Like

173K 10.6K 126
တာတေရဲ့ အထက်လမ်း အောက်လမ်း စုန်းကဝေ ပရလောက စွန့်စားခန်းတွေအကြောင်း။ နည်းနည်းပြောချင်ပါတယ် တာတေရဲ့ဇာတ်လမ်းတွေက သရဲစာပေgroupတွေမှာလည်း တင်လေ့ရှိသလို...
1.3M 83.5K 40
နေမင်းတမာန်-"ခုလောဆယ်ကိုယ်က ဒုတိယူလူဖြစ်နေပေမဲ့ လျမ်းထက်မောင်ဆိုတာ အစောထဲကကိုယ်ဟာပါ~" -------------------------- လျှမ်းထက်မောင်-"နေမင်း ကငါအတွက်အရံ~...
130K 10.5K 33
က်ိန္စာဆိုးမ်ားႏွင့္ျပည့္ႏွက္ေနေသာ ေၾကာက္မက္ဖြယ္ဝိညာဥ္ဆိုးမ်ားျဖင့္ ဆာေလာင္မြတ္သိပ္ေနေသာ "ျမနန္းစံေတာ္" အတိတ္ဘဝရန္ၿငိဳးေတြႏွင့္.. အမုန္းတရားေတြျပည့္...
32.9K 4.2K 44
لە هەفتە یەکدا تەنها یەک ڕۆژ بە ئاسای بژی18 کووکی : من خیانەتم نەکردوە ن/ت :بینیم کە ماچی ئەوت کرد