Murmushi yayi yace " qanwata tuqin dare Babu dadi Kuma Kinga hanya akwai nisa mama ne ma tace muzo yau mu kawo Miki sauran kayayyakin ki da aka kawo daga baya ko zakiyi amfani dasu Amman da sai kin shekara guda kafin muzo"

Ana cikin haka Khamis ya bude qofa ya shigo, ganin Yanda yake a firgice yasa gabana faduwa! Inada tabbacin motar ya Safwan da ya gani a waje ne ya daga Mishi hankali fata na Allah yasa kada yayi wani Abu da Bai dace ba a samu shaidan da za'a Kai ma iyaye na dan already nasan Aisha qiris take jira har yanzu yanayin ta bai nuna ta gamsu da Khamis ba,

Fuska a sake Safwan ya miqa mishi hannu suyi musabaha, Khamis ya tsaya Yana qare wa hannun kallo Wai gardin da ya shigo mishi gida ne saboda tsabar rashin kunya zai miqa mishi hannu su gaisa?,

Baice musu komai ba ya juya a fusace yayi ciki, Safwan na ganin haka Yaja hannun 'yar qanwar shi sukayi min sallama suka fita, sauqe ajiyan zuciya nayi ganin har sun tafi Khamis Bai fito ba da sauri na bi Bayan shi dan ganin me yake yi a ciki,

Shigana ke da wuya Naga Khamis ya nufo qofa zai fita da zuqeqiyar screw driver, a tsorace na rufe qofa na qaraso inda yake murya qasa nake tambayar shi me yake Shirin aikatawa,

Shaquro wuya ta yayi ya buga ni da garu Yana zazzare idanun shi da suka kada sukayi jaa ruwan bala'i kwance a cikin su,
"Kashe shi zanyi, wallahi sai na kashe shi kema na kashe ki Kuma nazo na kashe kaina, ba Zan boye Miki ba Yusrah tunda Naga rashin sani ne yake saka ki aikata ganganci, I'm evil when it comes to you, bani da Imani ko kadan akan abunda nake so abinda ya raba ni da family na da brothers dina Kenan"

Sake ni yayi ganin na fara qaqarin mutuwa a hannun shi, zubewa nayi a Kan guiwowi na Ina tari ji nakeyi kaman ya daure ni da kaca a wuya na, shima tsugunawa yayi ya matso kusa Dani har yana Jin sauqar numfashi na, sannan ya fara gwada ni da screw drivern hannun shi

"Dole nasa mahaifiyata ta rabu da sauran qanne na da yayu na ta dawo zama tare Dani kadai kinsan dalili? Because I love her so much, ita kadai nake so Dan haka itama dole ta Soni ni kadai I never share what I love I hate to share my loved ones,

Yusrah na gaji da boye Miki asalin dabi'u na da Kuma ni wanene, idan inaso dole a So ni Kuma ba'a so tare dani, Ina sonki kina Sona yanzu ya zamo Miki dole ki bar son kowa sai ni kadai Zaki bawa dukkan soyayya da kulawar ki kinji ko?" Ya qarasa a tsawace,

Amman bashi ya firgita ni ba, Jin wani zafi da azaba a gefen ciki na ne ya rikida ni, a hankali na sauqar da idanu na wurin don naga wani Abu ne haka, sai arangama nayi da screw drivern dake hannun Khamis ya bula ruwan ciki na, na saka hannu na na shafo jinin da ke malala daga jiki na Ina qare Masa kallo, lokaci daya naji wani jiri idanu na suka daina ganin komai sai duhu, rigib na zube a qasa tun daga lokacin ban sake gane inda kaina yake ba,

A hankali na bude idanu na inajin sunyi min nauyi, jujjuya kaina nake yi dan na samu gane inda nake, asibiti ne aka kwantar dani harda oxygen ana saka min ga Khamis zaune Yana riqe da hannu na daya ya kwantar da kanshi a jikin gado na,

Fara tunano abinda ya faru baya har dalilin da ya kawo ni asibitin nayi, Babu wacce ta Fado min a rai sai Aisha ,Ina tuna ranar da Aisha tazo gidan mu da daddare ta fada min gaskiyar Khamis Amman nayi Mata Koran Kare, Aisha is right Khamis is an evil person yanzu Kam na fara yarda da maganar ta,

Har yanzu Ina son Khamis Kuma har gaba Zan ci gaba da son shi, Amman tsananin tsoron shi ya Kama ni kuma zanyi takaicin kasancewar shi haka da bakin shi ya fada shi ba mutumin kirki bane Yaya yaranmu zasu ji idan suka taso suka ga uban su haka? Shin zasu dinga min addu'a saboda na sama musu uba na gari ko Kuma zasuyi Allah wadai dani da nayi zaben tumun dare?

Zare hannu na nayi daga cikin nashi a hankali Ina qoqarin tashi na zauna, firgigit ya farka da azama yayo kaina Yana dudduba ko Ina don ganin ko lafiya nake, runtse idanu na nayi gamm Ina tsoron Khamis ya sake qoqarin min wani abun bayan wanda yayi min a baya,

"Baby please open your eyes, I'm very sorry please ki taimaka ki kalle ni, kwanan ki biyu kina kwance a nan idanun ki a rufe look into my eyes please"

Takaici ne ya turnuqe ni duk abinda ya farun nan kalmar da Khamis zai fada min Kenan in yi haquri? Hawayen da bansan na meye bane suka fara bin kunci na Ina tausayin kaina a hannun Khamis wallahi I'm not sure ko yana da cikakken hankali,

Ganin hawayen fiska ta yasa ya sake rikicewa ya fara shafa fiskana Yana girgiza ni kaman want mahaukaci ya fara sumbatun da ni bani Gane komai a ciki bayan open your eyes da ya fada yafi qafa 50,

Qara zage qarfin shi yayi Yana girgiza ne harta hantan ciki na Saida suka jijjiga ga gefen ciki na da yayi min rauni inajin kaman Yana sake stabbing dina a Kan ciwon wurin sai qara fitar da jini yake yi, dukda oxygen din da aka saka min Amman Ina Jin numfashi na yana qoqarin daukewa,

nikam ta kaina da wannan bawan Allan, anya Khamis ba burin kashe ni bane a ranshi ya fake da wani soyayya? Ana cikin haka doctor ta shigo ganin abinda Khamis yake min yasa tayi saurin qarasowa wurin shi tare da ture shi gefe tana masifa,

Saidai da Khamis ya fara nashi sai ta saka ma nata bakin sakata banbami yakeyi kaman zai tashi dakin da muke ciki Wai dole tasa na bude Ido na kalleshi Kuma nasamu lafiya mu tafi gida,

Jin tana magana a Kira security yasa na bude Ido na tare da cire oxygen mask din fiska na da qyar nake iya magana a haka dai na lallabi doctorn ta haqura Bata saka an fitar da Khamis ba Amman Saida ta Kore shi kafin ta dudduba ni tana fita ya sake dawowa..........🤦🏻‍♀️

Don't forget to follow, vote, share and comment as you read💖

And also don't forget that this novel is fiction Naga fans are getting emotional😂 kowa sai masifa take tana qarewa Khamis tanadi🤣 just chill an enjoy the story, I agree that it happens sometimes but a case like this is rare and happens on contrary,

*Ummu Najma ce 😘*

MATAR KULLE(Short story)Where stories live. Discover now