chapter 8

531 85 4
                                    

(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)
 
😈 *MATAR KULLE*  😈

     _(Thriller)_

_Short story_
©️2020 special

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

Blog : prowritersnovels.blogspot.com

Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

         *BY*
        *UMMU NAJMA*

08🧛🏽‍♂️
Cike da farin ciki na dago Ina kallon fiskar ta ita dinne da gaske, iso nayi musu cikin gidan Ina mamakin zuwan su, nasan duk daren dadewa wasu zasu zo daga garinmu Amman banyi tunanin Aisha bace zata zo saboda Yanda mukayi rabuwan rashin mutunci,

A parlo suka yada zango na kawo musu drinks da snacks sannan na koma gefen Aisha na zauna muna gaisawa da ya Safwan, dukan wasa takai min a cinya ta hade rai tace

"Haba bestie, meye a cikin duniyar Nan da Zaki guje mu dan kinyi aure?? Ko sau daya baki Kira ko a way kinji lafiyar mu ba gashi kema idan an Kira wayan ki bayi shiga gaba daya kin tada hankalin mama kinsa ta dago mu Babu shiri"

Murmushi nayi Ina murza zoben hannun na cike da kunya da Jin nauyin Aisha dan har yanzu ban manta zagi da tozarcin da nayi Mata ba Amman gashi yau tazo gareni kaman ma Babu abinda ya raba faruwa,

"Sorry bestie waya ta ne ya samu matsala Amman next week yace zai gyaro min insha Allah, Yaya gida Yaya momy Yaya kowa da kowa?"

" Hmmm abubuwa da yawa sun faru Bayan Baki Nan ai da masu dadi da marasa dadi, kwanaki irin ciwon da Nasreen tayi bamuyi tsammanin zata rayu ba wallahi yanzu Haka kwana biyar Kenan da Mata operation din appendix"

Dafe qirji nayi hade da zaro Ido Ina maimaita "innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, Yaya akayi hakan ta faru ban samu labari ba?"

" Bake 'yar aure dadi ba? Har aunty suhaila ta rasu da 'dan cikin ta anyi 40 shima Baki sani ba"

Cike da jimami nake girgiza Kai Ina " hasbunallahu wa ni'imal wakeel, Allah sarki ya Safwan Yaya haquri"

Murmushin Yaqe yayi yace " haquri alhamdulillah"

"Allah ya jiqansu ta yasa ta huta, Allah yasa aljannah ce makomar ta"

Da "ameen" ya amsa lokacin da wayarshi ya fara ringing, yayi excusing kanshi sannan ya fita waje don amsa Kiran, Yana fita Aisha ta matso kusa Dani tare da daka min duka a cinya wannan karon zafin shi ya shige ni na fara sosawa Ina binta da harara,

"Ke an kawo sadaki na fa? Za'ayi Aure na in 3 months time, Ina ta so in disa Miki gurmi Amman na kasa samun ki Nima na kusa Shiga layin ku"

Ta qarasa tana wani rangwadi tare da rausaya Kai kaman wata qadangaren gobara, hannu na miqa Mata muka tafa da bayyanannen Jin Dadi saman fiska na nace "Masha Allah gaskiya nayi Miki murna best inama ace Ina Nan a adamawa za'ayi komai tare Dani!"

" Ai kin riga kinyi missing, sai fa haquri Dan Allah ya gani ko sahun qawaye na ba Zaki Shiga ba kije kiyi ta saka Burma burman hijab Wai gaki matan aure"

Muna cikin zantawa ya Safwan ya shigo ko zama baiyi ba yace ma Aisha "mu tafi ko? Kinga dare nayi Kuma da tafiya sosai a gaban mu", marairaice fuska nayi nace "Allah sarki Yaya ka Dan Bari zuwa anjima Mana ko minti 30 fa bakuyi ba Kuna nasan idan kuka tafi sai na dade ban sake ganin ku ba",

MATAR KULLE(Short story)Where stories live. Discover now