AƘIDATA CHAPTER 44_45

1.4K 48 21
                                    

  _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

NOT EDITED  (BANYI EDITING BA)

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 44_45

Yusuf ne yayi saurin ɗagowa ya kalli Hanne, Yusuf yace "Subhanallah, garin yaya kika ɓarar da Abinci?"

Widad kam ko motsawa ba tayi ba balle ta tashi daga jikin Yusuf.
  Cikin rawar jiki Hanne tace  "Tuntuɓe nayi shine ya zube, bari in samo in kwashe"
Ta juya ta fita da sauri, tana fita tsakar gida Gwaggo ta kalleta tace "ke meye haka, ba dai Abincin da nace ki kaiwa mara lafiyan kika zubar ba?"

Cikin inda inda tace "Amm.. Mm... Tuntuɓe nayi shine ya zube"

A fusace Gwaggo tace "kekam kamar mara hankali wani lokacin, kije ki kai Abinci kawai seki zubar dan shirme"

Hanne ba tace komai ba ta tafi ta ɗau tsintsiya da abun kwashe shara ta tafi gyara inda ta ɓata musu, cike da zullumin me zata je ta sake tararwa.

Gwaggo tace "Hindu tashi ki duba sauran kunu a ɗakina ki kai musu ba'a bar mara lafiya da Yunwa ba"

Sukam Maƙota da suka rako Yusuf ne suka dinga jinjina rashin ta ido irin na Widad, a gabansu ba kunya taje ta rungume mijinta.

Wani da'ake kira da Lado me Jakai yace "to ai kunsan su ba namu ne na nan ba, jama'ar birni ne baku ga matar tasa bama kamar balarabiya, su sun saba irin wannan bakomai ne ba"

Ɗayan da'ake cewa Liti yace "Aradu amma ai kunya wani abuce, tunda nasan duk abu Hausawa ne"

Lado yace "ku kuga haka, su a gurinsu ba wani abun bane ba"

Liti yace "Sumi sumi dashi haka, Amma ta rungume shi ya wani basar abunsa, memakon ma ya ɗanyi mata tsawa ya hanata"

Wani me shekaru a cikin su yace "Kai waye ya gaya maka suna hantarar matansu, lallaɓasu suke yi, ni wallahi birgeni ma suka yi"

Kwashewa sukayi da Dariya gaba ɗayansu, harda ƙyaƙyacewa.

Hindu tayi Sallama, da kofin kunu tace "gashi inji Gwaggo, tace dan Allah kuyi haƙuri Hanne ta zubar da Abincin"

Yusuf yace "bakomai Hindatu hakanma mungode"

Hindu tace  "Amarya yau za'a ci Abinci, tunda me gidan ya dawo"

Yusuf yace "Ai naga alama bata cin Abinci ta rame sosai"

Hindu tace  "bata ci, Gwaggo taita fama da ita sedai tayi ta kuka, ko bacci bata iyayi"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now