AƘIDATA CHAPTER 13

591 34 4
                                    

                    
                    _*AƘIDATA*_

         *AYSHERCOOL*

      

                         PART1
                              Page 13

ELEGANT ONLINE WRITER'S

Ba ƙaramin firgita tayi ba da abunda Yusuf ɗin yayi, sedai riƙon da yayi mata tana iya jin huci me zafin da jikin sa ke fitarwa, masifa take son yi amma gaba ɗaya Yusuf yayi mata wani irin kwarjini ta kasa cewa komai se binsa da tayi da manyan idanunta.

Cike da jarumta Yusuf yace "Meyasa koda yaushe idan nayi abu seki ƙarya tani? A koda yaushe ina ƙoƙarin gaya miki iya gaskiya ta amma seki ce ƙarya nake, kin san yadda mutum keji kuwa idan aka ƙarya tashi, it's really hurts, duk abunda nake yi ba inayi ne dan in samu kusanci dake ba, nasan AƘIDARKI nasan abunda bakya so, ina ƙoƙarin kiyaye dokokin da kika kafamin ne, dokokin dana sawa hannu amma koda yaushe burinki kici zarafina"

"Malam cikani ko"  ta faɗa tana masa wani irin kallo

Cikata yayi ya koma gefe ya tsaya.

Seda tayi ajiyar zuciya sannan tace

"hmm tunda nake babu wanda ya taɓa Yimin abunda kayi min a yanzu, ina ɗaga maka ƙafa ne saboda wasu dalilai biyu zuwa uku, dalilai biyu bakomai ne a gurina ba, dan ba zasu hanani yanke hukuncin dana ga dama akan ka ba, dalili ɗaya ne me ƙarfin da yazo da ƙaddarar da ni ban isa in canza shi ba koda hakan bemin ba, ba yadda zanyi da kai dukda har yanzu ina doubting akan wannan dalilin, Anyway zamu fita yanzu zamu je gidan gona"

"A wace motar?" ya tambayeta a taƙaice

"kowacce ta bashi amsa"

Har ya juya ze fita yaji tace 
"meya sameka a fuskarka?"

Ya juyo ya kalleta

"kar kayi min ƙarya" ta faɗa kafin ya bata amsa

"Duka ne" ya bata amsa

"Kamar ya ya duka? Suwaye suka dakeka?"

"Nima ban sansu ba"

Ɗan tsayawa tayi tana nazarinsa, yayin da ya ɗauke kai yaƙi kallonta

"Shikenan, muje"

Suka fito falo, yana gaba tana bayan sa, Amal ta bisu da wata uwar harara.

Ramadan yace 

"Allah ya temaki 'yar masu gida, Gimbiyar gida a biki a zauna lafiya, a ɓata miki mutum yai kwanan baƙinciki,' yar gaban goshi sha lelen masu arziki, tun ɗazu nake zaman jiranki anan, Megida ne ya aiko ni, yace yana son ganinki"

Ta yamutsa fuska tace  "Ina da abunyi, da  haka ba zani ba"

Ramadan yace "haka zanje in gaya masa"

"Eh haka za kaje ka gaya masa, bazan zo ba, bazan ƙara zuwa inda yake ba"

"shikenan, kunfi kusa keda shi"

Ta juya suka fice ita da Yusuf.

Amal tace  "Ramadan, dan Allah yanzu baka jin haushin irin abunda takewa mahaifinku?"

Ramadan yace  "to me zance Amal? Ni meye nawa a ciki? Da mahaifina da mahaifinta tashi nayi na gansu tare, kuma haka muka tashi muka ga an sangartata se abunda take so sukeyi, sun ɗauki son duniya sun ɗora mata, ba'a kwaɓarta komai tayi dai dai ne, meyasa zanji haushi, tunda ba yau ta fara ba, kuma idan tayi baya jin haushi, a gabana a gaban sa idan bata ga dama ba  Bulama take cemasa kanta tsaye, an riga an barta ta tashi akan wannan AƘIDAR"

AƘIDA TADonde viven las historias. Descúbrelo ahora