AƘIDATA CHAPTER 16 _17

558 36 0
                                    

_*AƘIDATA*_


PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends




ELEGANT ONLINE WRITER'S

PART1
Page 16_17

(Ayimin afuwa jiya nayi mistake ɗin pages)

Ko kallon inda Daddy yake bata kuma yiba ta fice ta bar masa ɗakin.

Komawa ɗakinta tayi, tana jin yadda zuciyarta ke wani irin bugu kamar zata fasa ƙirjinta ta fito 'kenan har yanzu Daddy be janye maganar nan ba? Daddy why?'
Tayi maganar da ƙarfi, tana sauke numfashi a hankali ta zube a ƙasan carfet, gaba ɗaya kanta ya kulle ta rasa abunyi, tabbas wannan karon Daddy dagaske yake, idan kuwa har Daddy ya dage a wannan ƙudurin nasa to tabbas zata bijre, koma hakan yayi sanadiyyar ya rasa ta gaba ɗaya, kuma seta shata babban layi tsakanin ta da Bulama.

Ramla tunani take me zata yi wanda zesa a janye maganar Widad da Fahad, ya za'ayi mutumin data daɗe tana tararirayar soyayyar sa lokaci ɗaya a wargaza mata komai, sam hakan bame yuwuwa bane, dole tasan abunyi dan yiwa wannan tufkar hanci.

************************************

Kallo ɗaya zakayi wa iyalan kasan suna cikin farin ciki, gaba ɗaya sun hallara a katafaren falon gabansu shaƙe da nau'ikan Abinci kala kala, kowanne fuskarsa ɗauke da farinciki.

Ramadan yace "Wallahi broz Fahad gaba ɗaya kaima ka zama kamar Bature, kaga yadda skin ɗinka tayi fresh kamar wani jariri"

Alhaji Bulama yace "Wannan Ƙaton ne fatarsa kamar jariri, kai dai Ramadan ka fiye shiririta"

Hajiya Sarah tace "Haba Daddy, ka kalli yadda ya wani murje yayi ƙalau dashi"

Iman tace "Nikam banga abunda ya canza ba sedai yayi haske ya ƙaro iyayi, ko hausarma bata fita sosai se kace Widad"

Ɗan ɓata fuska Hajiya Sarah tayi jin an ambaci Widad.

Alhaji Bulama yace "se suje can su cigaba da gwarancinsu"

Sam Fahad be fahimci abunda mahaifinsa yake nufi ba, haka suka ci gaba da ciye ciyensu suna hira cike da ƙaunar juna.

Yusuf kuwa tunda ya baro falon nan ransa a ɓace kai tsaye gida ya wuce, zuciyar sa nata faman tafasa, tabbas ƙarshen wulaƙanci yau Widad tayi masa, banda dalilin aikin sa da kuma mutuncin mahaifinta da baze sake komawa gidan ba.

Nurat bata da aiki se tunanin Yusuf, ko bacci ta kwanta mafarkinsa take, gaba ɗaya zuciyar ta ta kasa samun nutsuwa, ta kira lambar Yusuf harta gaji, ta koma kiran ta Widad, amma itama bata tafiya, abun duniya duk ya ishe ta.

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now