CHAPTER 6

655 40 1
                                    



_*AƘIDATA*_


PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends



ELEGANT ONLINE WRITER'S

PART1
Page 6




Widad kam koda ta fito daga banɗaki, da jakar turarukan nan data bawa Yusuf ta fara yin arba akan gadon ta, ta ƙarasa a hankali ta duba, sune dai turarukan da ta bashi,
"lallai wannan ɗan rainin hankali ne, ni zan bashi abu yazo ya ajiye min?"

Fita tayi falo ba kowa dan haka ta wuce part ɗinsu Amal, tana zuwa ta tarar da su a kitchen suna ta girki suna hirarsu, Wai Ramlah zata yi baƙi, se hada hada suke da kaji da sauran kayan masarufi.

Basu san da zuwan Widad ba se muryarta da suka ji cikin isa tace
"Ramlah kije gate ki kiramin driver na yanzu"
Cike da ɓacin rai, ba tare da Ramlah ta kalleta ba tace "to"
Haka Ramlah ta fita tana ƙunƙuni ta nufi bakin gate.

Tana zuwa ta tarar Yusuf ya siyo Abinci ze fara ci, Ramlah tazo kansa ta tsaya ta ƙare masa kallon up and down a wulaƙance, ta kalli gurasar gaban sa ta masu balango da nama ta kuma kallon sa ta taɓe baki ta ɗanyi tsaji taxe

"kai kazo inji waccan yarinyar"

Banza Yusuf yayi mata ya cigaba da ƙoƙarin cin Abincin sa.

"Wai baka ji ne?" ta masa magana cikin tsawa.

Nura direban Alhaji yace "Yusuf da kaifa take magana"

Yusuf ya ɗago ya kalli Nura yace "yawwa Sunana ka ambata, meze hana ta kirani da Sunana dan me zata cemin kai, kuma ni ban san wata yarinya a gidan nan ba"

Mamakine ya kama Ramlah, dama yana magana haka da wulaƙanci amma yake iya tsayawa Widad taci zarafin sa? Ba mamaki saboda kwaɗayin abun duniya kar a kore shi shiyasa yake shnaye wulaƙancin Widad, amma har ita wannan talakan ze buɗe baki ya gayawa magana a fusace tace

"kai saurara bazan kira sunan naka ba, uban waye kai da zaka dinga tambayar ban san sunan ka bane? Kai a wa? Ka kiyaye ni wallahi bana son shirme idan kace zakamin rashin mutunci zaka ga abunda ze biyo baya, sannan idan kaga dama kaje, in baka ga dama ba karka je ka san sauran"

Yusuf yayi kaman ba da shi take ba ya ci gaba da antaya gurasar sa. Ran Ramlah ne yai mugun ɓaci da ganin wannan rainin hankalin na Yusuf, ƙwafa tayi ta koma cikin gida.

Nura yace "Yusuf dan me zakayiwa Ramlah haka? So kake kaja wa kanka a kore ka?"

Yusuf yace "Nura kenan, to a korenin mana seme?" ya ci gaba da cin gurasar sa seda ya gama cin Abincin sa, Sannan ya miƙe ba tare da ya kuma cewa komai ba ya nufi cikin gidan.

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now