AƘIDATA CHAPTER 38_39

608 41 2
                                    

                      _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

NOT EDITED

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 38_39

Shi kansa Saleh abun ya ɗaure masa kai, ta yaya za'a je har Asibiti a sace mara lafiya, kuma bayan da jam'ian tsaro a cikin Asibitin da suke tsaron lafiyarsa, koda yake ba abun mamaki bane a haɗa baki dasu a sace shin, saboda da yawa mutanen yanzu suna iya yin komai saboda kuɗi.

Maman Nurat ce ta shigo ɗakinta, ta tarar da Nurat tana kan system tana danne danne, ta ɗago ta  kalli Mahaifiyarta tace "Mummy lafiya kuwa?"

Mummy tace "Mhmm, wani labari naji"

Nurat tace "labarin me?"

"wai an nemi Alhaji Daula an rasa a Asibiti, yanzu haka an kama Shugaban Asibitin doctor Sufyan da kuma Anwar"

Zare farin glashin idonta Nurat tayi tace "What are serious Mum?"

"did I ever lie to you?"

Cikin kaɗuwa Nurat ta girgiza kai tace "Na shiga uku da wannan masifa, daga wannan se wannan ana ƙoƙarin a kashe wannan amma se waccan ta faru, an sace masa 'ya har yanzu ba wanda yasan inda suke, yana kwance yana fama da jinya an bishi gadon Asibiti an sace shi, innalillahi wa inna ialaihi raji'un, Mummy me Anwar yayi aka kama shi to? "

Mummy tace " ina zan sani, ance dai har dashi a cikin suspect "

Nurat tace" idan harda sa hannun Yaya Anwar a ɓatan baban Widad, to tabbas beyi hakan dan cutar dashi ba, akwai dalili yakamata in ganshi "

Zare ido  Mummy tayi tace  " kiga wa? Ba dani ba Wallahi idan kika sake kika fita duk abunda yayi miki ke kika siya, na gaya miki babu ruwanki ki koma gefe ki taya su da Addu'a yafi "

Shiru Nurat tayi bata kuma cewa komai ba, Mummy ta gama mitarta ta tashi ta fita, ita kuwa Nurat ta shiga tunanin yadda zata yi ta fita.

Yanzu duk lokacin da aka idar da sallar Asuba, se Yusuf ya tsaya sunyi karatu a masallaci, aikuwa gasu da son karatun babu girman kai a lamarin su, dan haka yake jin daɗin koyar dasu, kuma ya basu damar yi masa tambayoyi, wasu tambayoyin idan kajisu sam bazaka ce musulmi ne ba, saboda tsagwaron Jahilci, Yusuf baya kyararsu ko hantararsu, haka yake amsa musu.
Akwai wanda yake tambayar Yusuf bayan an watse daga gurin karatun, wai shi ya zata in mutum ya kwanta da iyalinsa ba'a wanka se ranar Juma'a, Yusuf yayi masa bayani dalla dalla, kuma ya ƙudurce babu batun kunya, shine maudu'in daze musu gobe in Allah ya kai rai a gurin karatu "

AƘIDA TAKde žijí příběhy. Začni objevovat