AƘIDATA CHAPTER 34_35

571 33 0
                                    

                       _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA _
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

NOT EDITED

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 34_35


Saleh ya cigaba da ziga Alhaji Haruna, akan lallai yayi bincike, dan zata iya yuwuwa abokan harƙallaesa ne wani yasa a karɓo masa abun hannun Widad, shiyasa me Adda yace masa sun gudu.

Alhaji Haruna yace "Nagode sosai Saleh, Insha Allah zanyi tunani akai"

Saleh yace "bakomai yallaɓai, bari in ɗanje gida in huta, kasan bana jin daɗin jikin nan nawa"

Alhaji Haruna yace  "shikenan Allah ya sawwake"

Saleh ya tashi ya tafi

Sakina ce fuskarta ɗauke sa damuwa ta shiga ofishin Suleiman, Suleiman yace "Sakina lafiya kuwa?"

Sakina tace "Yallaɓai akwai damuwa, yau sati biyu sa sace Yusuf amma har yanzu babu wani kyakkyawan rahoto, da yake nuna ana bincike akan lamarin nan, anya anyi adalci kuwa duba da yadda Yusuf yake bada gudunmuwa akan harkar tsaro, amma ace shi wannan iftila'in ya faɗa masa amma babu wani yunƙuri da'ake gurin ceto shi, idan ya rasa ransa fa? "  ta ƙarasa maganar kamar zata yi kuka.

Suleiman yace "look Sakina, kiyi wani tunani kodan Albarkacin 'yar babban attajirin da' aka sace su tare, yaci ace an maida hankali akan nemansu, amma har yanzu shiru, shikansa Daulan yana gadon Asibiti a kwance, na kai ƙorafi akan abari muma mu gudanar da namu binciken, amma daga sama aka bani umarnin cewar ba'a samu ba, ana gudanar da bincike akan al'amarin, babu wani abu da zamu iya banda muyi musu Addu'a "

Sakina tace " shikenan Yallaɓai, ubangiji Allah ya kuɓutar dasu lafiya, bari in koma kan aikina"

"Shikenan Sakina, Allah ya taimaka"

Sakina na tafiya, telephone ɗin gaban Suleiman ta fara ringing, ya sa hannu ya ɗaga, jin muryar wanda ya kira shin yasa shi miƙewa tsaye cikin girmamawa yana amsa wayar.

"A cikin ma'aikatanka wa'aka saka akan binciken masu bibiyar Alhaji Nasir Daula?"

Suleiman yace  "Yallaɓai Yusuf ne, wanda aka ƙarawa matsayi kwanan nan"

"A gaggauta kammala binciken nan, a miƙo bayanan binciken nan headquarter"

Suleiman yace "Ok Sir"

Yusuf ya kalli Widad da tayi kicin kicin da fuska yace "ga kayan nan na wankesu, sun bushe ma gaba ɗaya"

Tasa hannu ta ciro kayan daga bokiti, taga kayan a haɗe dana Yusuf, kwashe nata tayi ta zube masa nasa a gurin, Yusuf yasa hannu ya kwashe ya zuba a jakarsa.

AƘIDA TAWaar verhalen tot leven komen. Ontdek het nu