AƘIDATA CHAPTER 30_31

Start from the beginning
                                    

Maman Nurat taji zafin marin da yayiwa 'yarta, dan ba taga laifin da tayi wanda harta cancanci wannan marin ba.

Taja hannun Nurat zuwa ɗakinta, ta kalleta tace "kema Allah ya ƙara, gobe ma ki sake, gashi nan ya mareki a banza, kin fiye rawar kai Nurat"

Nurat ta share hawayenta tace  "Ni ban san wani tantirin munafikin ne ya gaya masa naje ba, Amma idan harna cika 'ya ta halak inason mahaifina ya dace da rahamar Ubangiji, dole in shiga rusa duk wani mummunan ƙudirinsa, ta haka ne kawai zan huce wannan marin da yayi min"

"kinga karki jawa kanki wani tashin hankalin, ki ɗakko mana magana kin san halinsa sarai"

"Mummy, wallahi zubawa Mahaifina ido yana abunda yaga dama, alhalin nida ke munsan ba dai dai yake ba bamu kyauta ba, babu ruwanki a ciki nikaɗai zanyi komai.

" Na sani, amma Nurat ina jiye miki matakin daze ɗauka akanki, idan ya gane abunda kikeyi "

Nurat tace "ba abunda ze gane, sedai inke zaki gaya masa"

Ta ɗau jakarta ta bar ɗakin, ta nufi nata ɗakin.

Amal ta zama kamar wata me jinya, ta rame sosai dan ko Abinci bata iya ci Sam, sedai abunda ba'a rasa ba, yanzu ma Mummy ce da Ramlah suke cin Abinci suna hirarsu, yayin da Amal juya cokali kawai take, ba ta kai ko loma ɗaya bakin ta ba.

Ramlah tace "wai Abincin ne bakyaci, kokuwa? naga se juya spoon kike"

Hajiya Halima tace "na lura da yarinyar nan, kwanakin nan sam bata walwala ta takure kanta da yawa"

Amal tace "Nifa wallahi ɓatan Yusuf ne ke ɗaga min hankali, wallahi na damu sosai beji ba be gani ba am sace shi, Allah kaɗai yasan wahalar da yake sha"

Ramlah tace "Ai kece 'yar wahalar, dama abunda yasa kike wannan damuwar kenan?"

Hajiya Halima tace " waini Yusuf ɗin nan ko tare mukayi Naƙudarki ne muka haifeki ban sani ba? Ubanki ne shi? Ko haifarki yayi idan baki kiyayeni da maganarsa ba sena fasa miki baki, kije ki kashe kanki saboda wani ɗan iska, Allah yasa su haɗa dashi su kashe"

Zare ido Amal tayi tace "Mummy a kasheshi kuma?"

"Eh a kashe shi, munafikin yaro na tsani yaron nan wallahi ba ƙaramin daɗi naji ba da aka sace dashi"

Ramlah tace "wallahi nima naji daɗin hakan, munafuki yaita sunkuyar da kai kamar na Allah, saboda shi ba irin wulaƙancin da wannan makirar ba tayi mana ba, yanzu da suka ƙara gaba se hutawarmu muke"

Amal ta dire cokalin ta miƙe ta bar musu dining ɗin.

Mummy tace "Allah ya kawo lokacin da burinmu ze cika, ita kuma tana wani shirme daban"

Ramlah tace  "kedai bari Mummy, nifa harna fara tunanin irin bushshar da zanyi, da yadda zan fantama in kece raini a cikin manyan yara, wayyo Allah daɗi"

Mummy tace "kedai bari yarinya, ai komai yana tafiya daidai"
Suka kwashe da wata uwar dariya, hakan yayi daidai da shigowar Anwar, hakan yasa suka ja baki sukayi tsit.

Ganin yadda sam halin da Daula ke ciki baya gaban mahaifiyarsa da 'yan uwansa yasa ya girgiza kai, tunda Daula ya kwanta a Asibiti bata taɓa kwana a gurinsa ba, se tafi kwana uku ma bata je ba.

Hajiya Halima tace  "Allah sarki yaron kirki, Anwar duk ka rame fa, anya baza' a nemi me kula da Alhaji a dinga biyansa ba, ba haƙƙinka bane yin jinyarsa, duk kayi wani iri jinya ba sauƙi fa"

Ya kalli mahaifiyarsa yace "Ciyar damu ɗaukae ɗawainiyar karatunmu da sauran buƙatunmu da yake haƙƙinsa ne? Me yasa lokacin da yakw ɗawainiyar damu baki ce masa ba haƙƙinsa bane, babanmu yayi mana ba tunda yana raye?"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now