AƘIDATA CHAPTER 21_22

Depuis le début
                                    

"nice maka akayi bana sonta? Ko kuma so kake in kalli mahaifina ince zan bijirewa umarninsa"

Anwar yace "ni bahaka nake nufi ba amma nasani ka sani Baka dace da Widad ba, nasan halinka gaba da baya"

"kasan halina amma ka barni nake soyayya da ƙanwarka? Ko abun naka son zuciya ne?"

"son zuciya be wuce wanda ake shirin yiwa Widad ba, Ramla tasan dai dai tasan abunda take yi dan haka idan ta zaɓeka a matsayin miji ita taso hakan, Amma Widad fa Yarinya ce sannan...

"kaga Anwar ya isheni haka" Fahad yai maganar a tsawace

"Idan har ba so kake abotarmu ta samu matsala ba ka ƙyaleni, ka fita daga batun Auren nan"

"Idan kuma naƙifa?"

"Komai ze iya faruwa"

Anwar yace "to sonake koman ya fary Fahad, naga baka gane rarrashi zan ɓullo maka ta inda ya dace"

Fahad yace "Anwar karka kuskura kaje ka faɗi wani mummunan abu a kaina a gurin mahaifin Widad"

"Fahad dani da kai a ƙarƙashin kulawarsa mukayi karatu, ba abunda be mana na gata a rayuwa ba, bana jin Widad kanta ta moreshi kamar yadda muka moreshi, idan har aka lulluɓe kura da fatar Akuya ba muyiwa Alhaji Nasir Adalci ba, kaima kasan baka dace sa Auren 'yarsa ba"

"Amma Anwar kasan taimakawa zan in Aureta tunda mahaukaciya ce?"

"kabar taimakon naka mana, kaje ka auri Ramlah"

"Amma Anwar meyasa kake fifita Bare akan ƙanwarka? Idan har dagaske kake Ramla yakamata kace bazan Aura ba"

"Fahad ba goyon bayan bare nake ba, goyon bayan gaskiya nake kuma kaima ka sani"

Yana gama maganar ya fice a fusace cikin sauri.

**********************************
Ɓangarren Nurat kam lamarin mahaifinta yana bata mamaki, gaba ɗaya babu wanda ya gane inda yasa gaba daga ita har mahaifiyarta, ga ta'amali da wasu irin ƙarti da yakeyi wanda daka gansu zaka san ba mutanen kirki bane, suyita musu zirga zirga a gida, babu me ikon cewa uffan saboda duk tsoronsa suke ji.

Gefe guda kam tunanin Abokinta ya cika mata zuciya, zuciyar ta na matuƙar begen ta ganshi amma abu ya gagara, tasan ko giyar wake tasha bata isa taje gidansu Widad ba, tunda ta dena ɗaga wayarta tasan akwai wata a ƙasa haɗuwarta sa Widad ze iya haifar mata da matsala ne kawai.

Ba zata iya ƙirga adadin saƙonni da kuma kiran da tayiwa Yusuf ba, gefe guda kuma dai zuciyar ta na kwaɗai mata son sanin me mahaifinta ke ƙullawa wanda yasa shi yin mu'amala da wannan mutanen haka, suke ta musu sintiri a gida.

************************************

Anwar ne ya shiga ɗakin Alhaji Nasir da Sallama, cikin sakin fuska ya amsa masa, sedai mahaifiyarsa tana tare da Alhaji Nasir ɗin a wannan lokacin, fuskarsa ta nuna yana cikin damuwa kuma yana son yin magana ne.

Alhaji Nasir yace "shigo mana Anwar"

Anwar ya ƙarasa ya zauna a ƙasan carfet yana sunkuyar da kai, can yace
"Daddy, naji ka yanke wani hukunci, wai dagaske nan da ƙarshen wata zaka aurar da Widad?"

"eh hakane Anwar, halin ƙanwar taka ne se ita, gashi har yanzu ciwon ta yakan tashi, bekamata ace mamanku ta cigaba da ɗawainiya da ita ba, akwai buƙatar itama tayi Aure tunda ta girma"

"Amma Daddy kayi bincike akan wanda zaka bawan kuwa?"

Alhaji Nasir yace "bafa wani ne ba, Fahad ne ba wai wani guri aka samo mata mijin ba, Fahad ne Abokin ka ɗan gidan Bulama"

AƘIDA TAOù les histoires vivent. Découvrez maintenant