Zumuncin Zamani

By Nazeefah381

7K 517 25

Labari mai saka rauni a zuciya bisa yarda aka yi watsi da zumunci aka martaba ku'di fiye da zumunci ta yarda... More

1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
30
31
32
33
34
35
36
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52

29

217 9 1
By Nazeefah381

Zumuncin Zamani....

Na

Nazeefah Sabo Nashe...

08033748387..

Hisham yana shiga gida harabar gidansa ya yi parking a wajen da ake ajiye motoci. Da kyar ya fito daga motar jiri na 'dibansa ha'de da ciwon kai mai tsanani. Ga kalaman Saudat da suke masa kara-kaina a k'wak'walwarsa. "Ka daure ka jure ka rabu da ni.." shine kawai abinda ya ke ji a kunnensa.

Tunani yake 'Ashe Saudat zata iya rabuwa da shi? Ashe har a yanzu soyayyarsa bata yi girman da za ta kasance tare da shi ko a mutu ko a yi rai ba. Da gaske Sauda bata fara masa SON MUTUWA BA? Son da zata ji ko za'a kashe ta ba zata iya rayuwa ba shi ba?

Farida na tsaye a bakin window tana ganinsa da tsawon lokacin da ya 'dauka a cikin motar, har zuwa sanda ya fito yana layi kamar ya sha kayan maye. Wani haushi ya turnik'eta ganin yadda ya zage ya lalace daga yau 'daya kawai. Tsananin tsanar Sauda ya sake shiga zuciyarta. Ta raya a ranta ko ta halin k'ak'a sai ta raba zuciyar Mijinta da soyayyar Saudat. Dubi ko tunaninta ba ya yi saboda an raba shi da Saudat.

Zuciyarta a zafafe ta fito daga 'dakin lokacin da ta fito Hisham ya shige 'dakinsa yana kwance flat a kan gado. Ba tare da sallama ba ta tura k'ofar 'dakin ta shiga direct. Da alama ita da kanta ta kawo kanta 'dakin mijin ba kamar kowace amarya ba da miji yake kai kansa wajenta a daren farko na aurensa.

Hisham ya bita da wani malalacin kallo tamkar zai yi magana kuma sai ya fasa, ya mayar da idonsa ya rufe.

A kufule Fareeda ta k'arasa cikin tsiwa ta ce "Hisham magana fa za mu yi ka ganni amma ka bawa banza ajiyata." Ta fa'da tana ka'da kafa'darta.

Ya bu'de idonsa da kyar ya zube a kan fuskarta ya ce "Please leave alone Fareeda, wallahi bana son hayaniya."

Cikin zafin rai ta ce "Ni ce nake maka hayaniyar Hisham?" Ba tare da ya tanka mata ba ya cije lab'b'ansa ya sake kulle idanunsa gaba 'Daya.
Fareeda ta da'de tana sababi kafin ta fice daga 'dakin cikin b'acin rai tana fa'din "Wallahi ka yi da 'yar halak, zan nuna maka Fareeda macece mai aji ba karabiti ba."


__________________

A sauri Saudat take shiri don tafiya makaranta saboda a ranar za su fara Exams, ta fito tsakar gidan bayan ta zura hijabinta "Umma zan tafi, sai na dawo na makara." Ta fa'da da sauri ha'de da saka kanta tana k'ok'arin barin gidan. Umman ta ce "Ga ruwan koko can ba za ki sha ba kike k'ok'arin tafiya?" Saudat tana murmushi ta ce "Umma kin manta yau ina azimi? Yau alhamis." "Haka ne fa, to Allah ya bada sa'ar jarabawa." Ta fa'da tana mik'a mata Naira 200 da ta kunto daga bakin zaninta Saudat ta karb'a tana godiya.

Hadarin da ta gani yana gangamowa a garin yasa take zuba uban sauri bata son ruwan sama ya zubo bata isa makarantar ba. Ga shi exams 'din da za'a musu mai zafi ce. Jin k'ugin mota ta yi a bayanta sam ba ta yi k'ok'arin juyawa ba ta sake jan k'afarta da sauri.

Hisham ne ya yi parking a gabanta sai a lokacin ta lura da shi, ya sauke ba'kin glass 'din motar sanye yake da pyjamas kayan barci da alama daga barci ya tashi cikin ha'de rai alamar ba wasa a tare da shi ya ce "Shigo"

Saudat ta 'dan yi jim kamar ba zata shiga ba,Hisham ya daka mata tsawa "Ki shigo na ce"

Ganin hakan da ya yi sai ya tsorata  da sauri cikin rawar jiki ta bu'de motar ta shiga. Da sauri ba tare da Hisham 'din ya kalleta ba ya ja motarsa. Har suka isa makaranta bai mata magana ba. Al'amarin da ya tunzira zuciyar Saudat ta dinga tunanin wane irin mulki mallaka yake mata. Ba tare da ta masa magana ba itama ta saka hannu ta bu'de motar.
Da sauri Hisham ba tare da ya kalleta ba ya ri'ke hannunta  cikin tsare gira sosai ya ce "Daga yau na sauke shiga adaidaita sahu, ban amince ba hak'kina ne na kai ki makaranta tunda har a yanzu da aure na a kanki. Kina ji na?" Da sauri ta ha'de rai tana kallon gefenta turo bakinta za ta yi magana Hisham ya yi saurin rik'e bakin ya had'e rai sosai kafin ya ce "Ba na son jin komai daga bakinki Saboda na san ba alheri za ki fa'da ba." Ya mik'a mata envelope ha'de da cewa "That's all kina iya tafiya." Ta ha'diye abinda zata ce ta fice cikin sauri tana mamakin Hisham wannan fa shi ake kira 'K'arfin hali murmushin yarda ya tsare gira take kamar wani sarki da baiwarsa.

Ko da aka tashi daga lecture tana fitowa ta hango shi zaune a saman motarsa. Ba ta yi mamaki don ta san yana da time table 'din su.

Ya mata kyau sosai cikin tsarin shigarsa jar rigar polo da black jeans. Fuskarsa a ha'de take sosai duk matan da suka zo wucewa sai sun dube shi, yana rik'e da wayarsa a hannu yana dannawa.

Saudat itama fuskar ta ha'de sosai kafin ta isa wajensa. Don ba zai yiyu ya dinga 'daga mata hanci ba. Yana ganinta ya durgo daga saman motar idanunsa a kanta dariya na k'ok'arin kubce masa ganin yarda ta yi kicin kicin da fuska a zuciyarsa ya ce "Dama ya lafiyar kura..." tunda dama  k'iris take jira hakan ta faru. Ya san Saudat da fa'da da tsiwa, ta tsaya kawai a gefe har da rik'e k'ugunta tana sake tuno baki. "Ni fa ba wata motarka da zan shiga, don ban ga dalilin da zai saka na shiga motarka ba bayan kai kanka ka san rabuwar mu ta za.........

Wani kallo ya watsa mata, hakan ya sa ta ja 'dan bakinta ta tsuke a zuciyarta ta raya masifaffe kawai."  Ya dinga bin 'dan bakinta da kallo kafin ya ce "Da kin sake kin k'arasa Wallahi yau sai kin raina kan ki, ki kuma shiga mota mu tafi bana son rashin kunya."

Cikin tsiwa duk da idanunta sun rusuna ta ce "Idan na k'i fa?" Dariya sosai Hisham ya tuntsire da ita yana jan lab'b'anta ya ce "Sarkin tsiwa, abu mai sauk'i idan kika k'i sai mu kwana a nan don wallahi ba zan yarda ki shigar min motar haya ba, ba ki san yarda nake kishinki ba ko?" Saudat ta zumb'uri baki ta ce "Wallahi Y.Hisham da ka daina wahalar da kanka don kana ji kana gani zan auri........."

"Saudat!" Ya fa'da cikin k'araji. "Be careful, wallahi zan miki abinda za ki raina kan ki wuce mu tafi"

Ganin b'acin ransa ya bayyana k'arara da sauri ta shiga motar ba tare da ta sake jayayya ba.

Tunda ya ja motarsa bai sake magana ba har ya dangana da gidansu Saudat 'din. Tana ganin ya yi parking da sauri ta fice har tana ha'dawa da gudu. Hisham ya saki murmushi bayan da ya bi bayanta da kallo a hankali ya saki ajiyar zuciya ha'de da cewa "My Lovely Saudat!"

____

Alhaji Hamza ya dubi Hajiya Balaraba ransa a b'ace ya ce "Yaushe rabon da Hisham ya zo gidannan?" Sai da ta 'dan yi jum sannan ta ja ajiyar zuciya ha'de da cewa "Cab yaushe rabon da na ga Hisham a gidan nan ai na Sallama musu Hisham, Fushi yake damu tunda muka korar masa mata, ni kuwa da zamansa da wannan tsiyar gwara ya dawwama yana fushi da mu." Ta fa'da fuskarta cike da rauni da nuna zallar tashin hankalin da take ciki. Alh. Hamza ya ja tsaki "Yanzu shi sabida y'ar gidan Mustafa ya zubar da mu iyayensa." Girgiza kai ta sake yi kafin ta ce "Ni fa ba wannan ba, ba abinda nake tunawa zuciyata ta dugunzuma ta b'aci kamar idan na tuna sai da ya kusanci yarinyar nan sannan ya kusanceta fatana 'Daya da burina Allah yasa bai jefa mata k'wansa a mahaifa ba." Alhaji Hamzan ya sake b'ata rai sosai kafin ya ce "Idan ma ya shiga da fitar da shi." Haka suka cigaba da jimami da tattauna maganar yarda har ya iya ya yi burus da su, kamar ba Hisham mai k'aunarsu da gudun b'acin ransu ba...

___________

Haka rayuwar ta cigaba da garawa. Tun Hisham yana saka ran su Abban za su amince Saudan ta koma har gwiwoyinsa suka yi sanyi ya tabbatar Abban shima a wannan karan an kai shi bango tunda har ya kasa tausaya masa tsawon wannan lokacin. Tsawon wata guda ana magana 'daya ta k'i ci ta k'i cinyewa.

Yau ya ci alwashin sake k'undunbalar tunkarar Abban da zancen duk da yana gudun samun bahaguwar amsa daga Abban.

Sai da ya je gidan Abban yana lazimi don haka ya ja gefe ya zauna don ya san ko ya yi magana Abban ba zai amsa shi ba matuk'ar yana lazimi. Gaisuwar ma da kai ya amsa masa ya cigaba da laziminsa.

Sai da ya ja addu'oi sosai su da suke zaune a tsakar gidan suka 'daga hannayensu suka amsa, sannan ya sake mayar da kansa kan Hisham da yake zaune gefe ya takure. Sai da ya yi tasbihi da neman dacewa a wajen ubangiji sannan yasa harshe ya kira sunan Hisham 'din da kaurararriyar murya da bata yi kama da wasa ba.

Sosai Hisham ya ji Kiran sunan har cikin ransa, don haka cikin azama ya 'dago ya zubawa Abban idanuwa cike da rauni. Sab'anin hasashensa da zatonsa sai ya ji Abban ya ce "Lokaci yana ja Hisham,  har yanzu ban ji komai ba. Zuwa yanzu ya kamata na san matsayar wajen da muka kwana kai ka samu hutu, itama yarinya ta huta da aurenka da yake kanta take yawo da shi, da nauyinka da yake kanta. Abu 'd'aya yasa har aka kai yanzu ban maka magana ba, shine na baka lokaci ka nutsu ka yi shawara da zuciyarka ko kai da kanka zaka gane rabuwarku itace mafi a'ala sai aka yi rashin sa'a soyayya ta k'unshe maka ido. Zaman aure ba zai tab'a yiwuwa tsakaninka da Saudatu ba, bisa la'akari da tarin hujjoji da bai zama lallai kai ka hangosu ba tunda sonta ya rufe maka ido. Akwai nisan banbanci a tsakaninku mai tarin yawa. Dama na amince wa aurenku bisa bin umarnin Baffan Wudil kada ya ce ban mayar da shi uba ba. Don haka a yanzu nima ina son sanar da kai ko yaya ka kai ga Son Saudat ba zan amincewa zaman aurenku ba, wallahi ka ji na rantse maka ba Zan amince Saudat ta koma gidanka ba, ba kuma fushi na yi ba ko kuma ina ganin laifinka ba a'a ko ka'dan har abada kana da k'ima da mutunci a idona kuma ko yanzu zan iya baka dama ka aurar da Saudat ga duk wanda ka so don in nuna maka kana da iko da Saudat. A kullum ba na banbanta ka da yaran da na haifa a cikina Soyayyar da nake maka ce ya sa bana son ka fa'da fushin sab'awa iyaye, fushin iyaye yana salwanta rayuwar yaro ya tab'arb'arata, tunda ba su amince da aurenku ba to nima ban amince ba ka dubi girman Allah ka kawo k'arshen badak'alar nan da ta k'i ci ta k'i cinyewa. Ka tuna su iyayenka tuni suka tsammaci ka saketa don haka kaje na baka kwana uku kacal ka kawo min takardar Saudat nan gaba na, Allah ya maka albarka ya baku hak'uri da danganar rashin juna." Daga haka Abban ya ja baki ya tsuke Hisham kuwa ya rasa a duniyar da yake sam bai gama gane zantukan Abban ba, wani irin jiri yake ji. Abba kuwa duk da tausayinsa ya dabaibaye zuciyarsa bai nuna masa ba madadin haka sai ya dinga jan adduoi a zuciyarsa na nemawa Hisham 'don sauk'i da taushin zuciya.

Sosai zuciyar Hisham take bugawa jikinsa ya jik'e sharkaf da gumi da kyar ya mik'e idanunsa na neman zubar da hawaye ya kalli Abban ya ce "Abba Nagode, sai da safe."  Ya mik'e yana ha'da hanya ya fice daga gidan.

Abba ya bi shi da kallon tausayi yana jin kamar zuciyarsa zata karye ya ce yazo ya amince masa ya tafi da matarsa, sai dai baya jin ko mutanen duniya za su ha'du zai amince da hakan.

Umman Saudat ce ta fito daga 'dakin fuskarta fal murmushi ta ce "Sai yau na samu Saida Abban Saudat, wallahi da na zata mayar masa da Saudat za ka yi ba ka ji yarda zuciyata take taratsatsin bamabaman b'acin rai ba. Yau kam ka burgeni Abban Saudat su je can su ci arzikinsu mu ma mu rungumi talaucinmu. Yana kawo takardar sakin a ranar Zan aika a jide kayan tas daga gidan 'dansa. Idan ya so bayan y'ar senator su ha'da masa da y'ar shugaban k'asar amuruka ma."

Dakata Maryam!" Abba Mustafan ya fa'da cikin zafin rai "Bana son irin wannan kuma sam ban ji da'din furucin Ki ba. Ban kuma jin da'din kallon da kikewa yaron nan ba, haba kada ki bari fa yaron nan ya fuskanci kina k'insa fa, zaki zama butulu mai manta alheri me kika aikata haka da wani ido za ki kalleshi idan ya fahimci kina goyon bayan rabuwar aurensa da y'arki duk da tarin halaccinsa garemu? Bari in gaya miki har a zuciyata ina jin ra'da'din raba aurensu da zan yi yadda na 'dauki su Khalil haka na 'daukeshi a zuciyata sam ba banbanci. Don kuwa shima bai banbanta ni da mahaifinsa ba, ina tarin kawaicinki da kararki Maryam? Na ce Ina suka tafi? Ina kika bar fulatancinki har ki ke son ki fifita soyayyar y'arki akan 'dan wani? Anya kuwa Maryam ba za ki ji kunya ba? Ba 'a san nagartattun mutane da wa'dannan halayen ba. Mutumin kirki shine mai rufe ido ya k'i nasa akan 'dan wani don kawai kawaici da alkunya, amma nema kike duk ki zubar da wa'dancan halayen k'ek'e da k'ek'e ki ke nuna son y'arki akan mutumin da ya yi mana halarci mutumin da bai k'yamaci takaucinmu ba duk da tarin arzikinsa kada ki sake shiga lamarin nan bana so kina ji na? Ki bar ni da shi  na san ta yarda zan biyo masa ba tare da ya yi tunanin mun masa butulci ba. Ko kuma mun fi son farin cikin y'ar mu akan nasa farin cikin. Idan kika yi abinda ya fahinci hakan ba zan iya ha'da ido da Hisham ba ina tabbatr miki, ya min komai a rayuwa ya so ni lokacin da dangi suka juya min baya, ya girma mani lokacin da dangi suka k'ask'anta ni. Bai cancanci tozarci a wajenmu ba, kada ki sake Maryama Bana so!! Bana so!!" 

Cikin wani yanayi yake magana wanda hakan yasa Maryama ta fahimci ba k'aramin b'ata masa rai ta yi ba ta kuma hango b'acin ran kwance a fuskarsa. Tuni dana sani itama ya shigeta ta ji tana kunyar ha'da ido da Hisham ba da wani idon zata kalleshi?

Kina jina?" Maganar Abba Mustafan ta sake katseta da sauri ta 'daga kai "Na ji Abban Saudat ka yi hak'uri In sha Allah hakan ba zata sake faruwa ba."

Ya saki ajiyar zuciya ha'de da cewa "Allah yasa Maryam, hakan na fi buk'ata."

Saudat kuwa tana shimfi'de akan gadonta kuka kawai take risgawa zuciyarta na tsananta bugu a yanzu ta tabbatarwa zuciyarta rabuwa da Hisham kamar saka ranar mutuwarta ne. Ta dinga jimanta kwana uku kacal ba ka Hisham a zuciyarta da sauri ta dinga jijjiga kanta tana fa'din kada ka soma Abba Rabani da Hishma kamar rabani da numfashina ne." 

Hisham fa? .......

Da kyar ya kai kansa wajen motarsa sabida jiri da layi da yake yi. Yafi minti talatin ya kasa sarrafa kansa ya ja motar sai da yaga lamarin yana ta'azzara sai ya kira k'aninsa Mahmoud don ya zo ya kai shi gida.

Mahmoud bai b'ata lokaci ba ya iso. Daidai lokacin khalil ya zo shiga gida har zai wuce sai ya ga rashin dacewar hakan ya dawo ya k'arasa wajensu yana mik'awa Mahmoud hannu, amma Mahmoud ya shareshi fuskarsa babu wani annuri ya 'd'aga masa hannu. Khalil murmushi ya saki don ya girmewa Mahmud nesa ba kusa ba don bai wuce sa'an Sa'eed ba. Hisham ya sauke glass 'din motar yana kallon Khalil ya ce "Ka dawo?" D'aga masa kai ya yi kafin ya ce "Ya na ganka hakan? Ko baka jin da'di ne?"

Hisham ya saki yak'en murmushi ya dafa kafa'd'ar Khalil.  "Khalil ka taimakeni kada Abba ya raba ni da Saudat ya kafa min shara'di nan da kwana uku na saki Saudat ba zan iya ba Khalil? Menene Mafita?" Mahmud da yake gefe Cikin mamaki yake kallon yayansa wato dama bai saki Saudat ba su iyayensu suna can suna hauka da zaton ya saketa cab ai kuwa a daren nan zai kai musu labari.........




Jikar Nashe.😊😊😊❤️

Continue Reading

You'll Also Like

Alina By ihidethisapp

General Fiction

1.5M 37.3K 75
The Lombardi family is the most notorious group in the crime world. They rule both the American and Italian mafias and have many others bowing at the...
3.2K 275 25
bana nada bayani kawai ki bibiyeni
16.9K 882 32
DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace m...
222K 16.4K 21
Avantika Aadish Rajawat Aadi, with his fiery nature, adds intensity and excitement to their relationship, igniting a spark in Avni. Avni, like the ca...