Zumuncin Zamani

By Nazeefah381

7K 517 25

Labari mai saka rauni a zuciya bisa yarda aka yi watsi da zumunci aka martaba ku'di fiye da zumunci ta yarda... More

1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52

24

116 8 0
By Nazeefah381

Zumuncin Zamani...

Na Nazeefah Sabo Nashe.

08033748387

Wattpad @Nazeefah381

Daga k'ungiyar Elegant Online✍🏽

****************

Haka dai lamarin biki ya kankama daga b'angaren amarya Fareeda. Sauda kam babu abinda take shiryawa da ya wuce harkar walimarta da saukar Alkur'ani.

Fareeda dai tanadi sosai ta yiwa bikin. Events biyar ta shirya na kece raini akwai Rainbow day, Ladies Night, Dinner, Mothers Night, da kuma Bridal shower.

Ita kuwa Saudat walimar ma sai ranar da za'a d'aura auren sannan zata yi ta, saboda su gajartawa kansu hidima.

Babu wanda yake bibiyarsu a sha'anin bikin da y'ay'an Inna Sahura sai na Inna Maryam, duk danginsu kowa yana can gidan su Hisham inda ake son zuwa bikin kece raini.

Su Zainab d'in Inna Sahura ne suka dubeta cikin takaicinta ta ce "Wallahi Babyn nan kin kwafsa mana, da tuni muna nan muna hidimar biki amma kin ce wani nan Dinner kawai ke za ki yi. Ni dai yau wallahi Dinner Fareedah zan tafi na je na kashe kwarkwatar idona, wannan wajen na kece raini a Amani event center fa za'a yi." Sauda da murmushi a fuskarta ta ce "Sai kun dawo, ni kam ba da ni ba gad'a a kabari. Bana ra'ayin wad'annan bidio'in banzan. Ba abinda suke janyowa sai kwashe albarkar aure, tunda Allah ne kad'ai ya san Fasadin da ake aikatawa a wajen. Cakud'uwar maza da mata haramun ba da ni ba."

Tab'e baki Zainab ta yi kafin ta ce "Kanki ake ji, baki da aikin yi sai wa'azi, lokacin abu ayi shi wallahi bikina sai an gwangwaje." Saudat da mamaki take kallonta ta ce "Wa'azin ne rashin aikin yi? To Allah ya kyauta A dawo lafiya ai ban hanaki ba."

K'arfe 8:00 na dare Hisham ya kirata daidai lokacin yana ta shirin dinner a gaban dressing mirror da yake gabansa. Tana d'agawa ya saki murmushi had'e da cewa "Uwargidana ya aka yi?" Ta d'an lunshe idonta kad'an kafin ta ce "Bakomai Y.Hisham." Ya saki murmushi ya ce "Ban yarda ba da komai, ni tunaninki ne ya cika min k'irji yasa na kiraki, ke ba kya missing d'ina?" "Mhmn" kawai ta ce tana sake k'ank'ame wayar a kunnenta jin yarda husky voice d'insa ke neman tafiya da nutsuwarta. "Menene Hmnnm, feel free ki yi magana Malama bana son k'aiyanci fa." Ya fad'a cikin sigar tsokana. Ta marairaice murya ta ce "Just tunanin ka." "Ya wuce just." Ya fad'a yana dariya "Me kake yi?" Ta samu kanta da jefo masa tambaya ya d'an yi Jim kamar ba zai gaya mata ba, sanin halin mutuniyar tasa sai dai ya na son ya ga wannan kishin nata, wani irin farin ciki yake ji ya san son da take masa ne yake janyo wannan zafin kishin don haka ya ce "Kin ganni nan ina shirin tafiya Dinner.." Tsit ta yi wani abu ya tokare mata a k'irji ta kasa had'iyeshi d'if ya ji ta kashe wayar.
Hisham ya bi wayar da kallo yana sakin murmushi ya sake dialling numberr sai dai bata d'aga ba daga k'arshe ma sai ya ji ta kashe wayar gaba d'aya. Ya girgiza kai yana jijina zafin kishi irin na Saudat.

********.        ***********.

Mak'il wajen dinnerr ya cika, kai daga ka shiga ka san biki ake na girma harkar ta manyace, Naira ta sha kashi a jikin mutane da dama kowa ya sha shigarsa ta kece raini.

Hisham zaune kawai yake a wajen dinnerr amma hankalinsa gaba d'aya yana kan Saudat, duk da ga Fareeda a gefensa kuma ta sha matsanancin kyau kamar y'ar tsana. Mintuna kad'an ya sake dialling numberrta amma stiil a kashe take.

Ita kuwa Saudat tana can zuciyarta na wani irin turirin kishi don ta san tabbas yanzu suna tare yana can ba mamaki yana zuba mata kalaman soyayya. Ko ma har ya rik'e hannunta oho.... Ta d'au wayar a zafafe ta shiga kiransa, sai dai an samu Akasi har ta gama ringing bai ji ba bai d'aga ba, hakan ya k'ara hura mata tunaninta na yana can ya manta da ita ya luluk'a duniyar masoya ya za'a yi ya ji kiranta?

Daidai lokacin da su Zainab suka fad'o d'akin a gajiye lik'is. Zainab ta d'aka mata duka a zafafe ta ce "Wallahi kin cucemu kin ga kuwa Dinner? Ke na manta tashi kije In ji Hisham yana waje yana jiranki yace a gaya miki sam yau ba zai iya barci ba har sai ya gan ki. Gaskiya Hisham yana matuk'ar son ki da gaskengaske, shi fa ya kawo mu daga can gidansu don
Kawai ya gan ki."

Saudat ta ja tsaki ta ce "To aku ni kin cika min kunne mai zan je in masa bayan ya dawo daga wajen masoyiyarsa?" Dariya sosai suka yi har da buga k'afa Zainab ta ce "Kishi k'umallon mata." Bata kula su ba ta fice daga d'akin don itama tana muradin ganinsa.

A tsaye a k'ofar gidan ta same shi yana nad'e da hannunsa a k'irjinsa. Kicin-kicin ta yi da fuskarta had'e da cewa "Ga ni." Ya bud'e ido yana kallonta sosai "Me kenan Saudat wace irin magana ce wannan ba rusunawa bakomai. A haka kike so ki mallaki soyayyata ke kad'ai, ya zafin kishi yake son saka ki ki aro tarbiyyar da ba taki ba." "Me zan yi da ragowar wata?" Ta fad'a cikin karyayyiyar murya Da sauri Hisham ya ce "Ni ne ragowar? Shikkenan nagode sakayyar da zaki min kenan? Duk da na biyo dare don na gan ki. Zo mu je mota na baki ragowar cake d'in dinner ne na rago miki? Kema ina so na baki a baki mu yi hoto." Wannan karan Saudat kasa mallakar kanta ta yi sai ji tayi hawaye na zubo mata ta dinga jijjiga kai tana cizar lab'ba ta fara zabga masa harara. Da sauri ya rik'o gefen gyalenta ganin tana shirin shigewa gida "Ni ki ke harara? Wallahi zan yi maganinki ashe tsiwar tana nan rusunawa ta yi, yarda Faree..." Ai bata bari ya k'arasa ba ta figi gyalenta ta shige gida da gudu. Hisham dariya ya yi sosai kafin ya ce "My Heart kenan."


**********

Ranar lahadi ne ya kama d'auri. Aure. Don haka kowane gida damk'am yake da jama'a babu masaka tsinke, musamman b'angaren ango, inda dandazon jama'a suka d'unguma suka tafi gidan Sule Jami'i don halartar d'aurin auren y'ar senatorn. Mutane da yawa ma ba su san har da y'ar gidan Mustafan za'a d'aurawa aure ba.

Can kuwa b'angaren su Saudat Limamin unguwarsu Alh.Hamza ne kawai da wasu tsirarin mutane suka wakilci uban ango daga b'angarensa. Sai ko angon da wasu daga cikin abokansa wad'anda suka bawa abin duniya baya. Mahaifinsa Alh. Hamza a cike yake da shi musamman da ya tambayeshi kud'in sadaki ya ce ya basu. Ya dinga surfa bala'i tamkar zai aro baki.

Duk da zuciya mai laushi irin ta Abba Mustafan, tabbas abinda yau suka masa ya tab'a zuciyarsa, ganin ba wani d'an uwansa li'abbi (na wajen uba) da ya halarci d'aurin auren y'ar tasa, duk da cewa wanann shine auren y'a da zai yi na farko. Duk don matsayin da Allah ya ajiyeshi na zamowarsa talaka. Babu wanda zai masa Waliccin y'arsa sai abokinsa. Allah ya kyauta.

A ranar da aka d'aura auren, ranar ne ya zama ranar kai amare. Inna Maryam ta ce da Umman Sauda "Shigar sauri
Zamu musu tamu ta zama uwargida ko an k'i ko an so.." Shi kansa Hisham dalilinsa kenan da ya dinga yiwa Inna Maryam waya akan ya turo motocin d'aukar amarya. Inna maryam babu ja ta ce "Su taho maza ayi a kaita an shiryata." Hisham ya zubawa abokinsa Nura ido ya ce "Nura ka hanzarta d'auko min matata please!" Nura ya zabga masa harara ya ce "Wallahi Hisham ka ji tsoron Allah, don na lura k'iri-k'iri kake nuna banbanci ka ji tsoron Allah kada ka tashi da shanyayyen jiki wallahi." Hisham tsaki ya yi yace "Ce maka na yi bana musu adalci? Ina adalcina a inda naga zan iya zuciyata kuwa ba ni nake iko da ita ba Allahn da ya yi ta shi ya saka min don Saudat fiye da na Fareeda. Sai yaya?" Duk abokansa suka zuba masa ido ba tare da sun ce komai ba.


***********

Hakane kuwa ya kasance k'arfe 4:00 na yamma dandanzon motocin suka ci burki a bakin lungun su Saudat. Ta sha kuka sosai har ta bawa jama'a da dama tausayi tabbas yau ta tabbatar da maganar hausawa da suke cewa Aure yak'in mata. Yarda ta kanainaye Ummanta shine abinda ya sosa ran wasu har suka fara zubar da hawaye. Haka suka yi sallama da Ummanta tana sake jaddada ba sai na ce miki komai ba Saudat in dai kin biyo ni ba yabon kai ba zaki zauna k'alau cikin aminci a gidan mijinki tunda dai kin san ni ko yaji ban tab'a yi ba."

Gidan Amaren babu kowa don kuwa ba su san za su musu shigar sauri ba. B'angarenta ya yi kyau sosai daidai gwargwado ba zaka ce min d'iyar Abba Mustafa bace ta samu wannan tagomashin. An had'a mata kicin d'in nata daidai da tsarin y'an boko ba wani tarkace. Hakanan falukanta sai son barka. Haka kowa ya shiga yabon b'angaren nata.

K'arfe 6:00 daidai dandazon motocin suka kawo fareedah, da tunanin ita aka fara kawowa. Sai dai murnarsu ta koma ciki sanda suka tarar an kawo Saudat d'in Ta tabbata babu musu itace Uwar gida. Haka suka shige suna shewa da habaice-habaice ba tare da Addu'oin da malamai suke kwad'aitarwa a yi ba idan an kai amarya. Sab'anin Saudat da suka shiga da addu'oi fal bakinsu.

Ba su yi k'ok'arin kaita d'akin Saudat ba sai ma harara da kallon banza da suka dinga watsa wa d'akin.

Dangin su Abba Mustafa ne suka shiga sashen Sauda ga tunaninsu za su ga fayau, sai dai suka ga sab'anin haka ga mamakinsu Abba Mustafa ya yi tasa bajintar sai dai madadin yabo sai ka ji suna cewa "Ai Hisham ya yi k'ok'ari don Mustafa ba shi da kud'in da zai yi wannan."

Kafin 8:00 gidan ya yi wayam, idan ka d'auke sashen Fareeda da k'awayenta suke zaune jingin suna jiran siyan baki. Suna kuma aikin zuga Fareedan akan kada ta amince ta tsaya ta jajirce ta zama itace uwargida duk da an Riga kawo Saudat d'in......

Jikar Nashe ce... 😊😊🙏❤️

Continue Reading

You'll Also Like

1.5M 128K 62
RATHOD In a broken family, every person suffers from his insecurities and guilt. Successful in every field but a big failure when it comes to emotio...
77.4K 3.5K 32
labarin BURINA labarin Zainab (Zee) da Khalil ( IK) da Abdallah (Alhaji) labarin soyayya ban tausayi da nishaÉ—i.
220K 16.2K 20
Avantika Aadish Rajawat Aadi, with his fiery nature, adds intensity and excitement to their relationship, igniting a spark in Avni. Avni, like the ca...
443K 16.2K 192
Won Yoo-ha, a trainee unfairly deprived of the opportunity to appear on a survival program scheduled to hit the jackpot, became a failure of an idol...