06

95 11 1
                                    

*ƘAYAR RUWA*
FitattuBiyar 2023.
'''Reposting'''

*©️Halima.hz*
*halimahz@arewabooks*
*Halimahz_@Wattpad*
*Halimahz@Bakandamiyahikaya*
____________________________________
'''for your business advert chartup 09030398006.'''
____________________________________
*(6)*
Ƴaƴan da aka ba ki! kalmar ta ƙarshe ta daki ƙirjina. Rumana da Atika, gaba ɗayansu ba su wuce shekaru takwas ba, yaran ba su kunya ga rashin ji shisa jininsu ya zo ɗaya, ko iyayensu kuka su ke da halinsu, shi ne ni kuma yanzu zai ce zai ɗauko min su in riƙe a wannan sanyin halin nawa?, salon wataran su fusatani in sauke musu fushina in ƙara baƙin jini, dama ya lafiyar kura bare an taɓota. na san dole akwai wata a ƙasa, sai dai ina roƙon Allah ya ɗora ni a kansu, ya kuma sauya duk wata baƙar manufa da aka ƙulla akan hakan.

murmushi na ƙaƙalo na ce da shi,"ai ko dai muna godiya matuƙa, Allah taya mu ruƙo, naji daɗi sosai, ko ba komai ma rage kewa".

na faɗa ina nuna jin daɗin da bai kai har zuci ba, domin cike na ke da fargabar rayuwarmu tare da yaran.

bai ce da ni komai ba yay shiru, na sauke ajiyar zuciya na fita daga ɗakin. ɗakina na koma na canja kaya, dama a falo na bar jakata da wayata, kuma da zuwan nawa na tarar da kiran Ummani, sai naji gabana ya faɗi ganin miscalls har guda biyar, take na fara tunanin anya lafiya don bata taɓa min miscalls irin haka ba, Ummani duk in da ta kira waya sau biyu ba'a ɗaga ba haƙura take yi, sai tace bata san uzurin mutum ba, idan ya gani zai biyo baya.

zama na yi kan kujera jiki na rawa na bi bayan kiran, sai dai ko da kiran ya tafi a lokacin kamfani ke shaida min bani da kati. ƙaramin tsaki nayi na ƙorafi tuna fa ashe tun shekeranjiya muna waya da matar Yashaik katin ya ƙare.
ina zaunen Hubbi ya fito, ina kallonsa ɓacin ran hana ni zuwa makaranta ya ƙaru, na kawar kawai na kasa share shi saboda ina so ya bani aron wayarsa. cikin shakkar masa magana na ce,"Hubbi don Allah aron wayarka in kira Ummani".

yana zama kan kujera ya ce min,"me ya sami taki?".

"babu kati".

har zai miƙo min wayar tasa sai kuma ya fasa ya ce,"bari in saka miki katin, wanne layin?".

"Airtel ɗin".

cikin wasu ƴan sakanni sai ga saƙon katin ɗari biyar ya shigo, nayi masa godiya sosai. na danna lambar Ummani na kira sai dai haka ta gama ringinga har sau biyu ba'a ɗaga ba. take gabana ya tsananta faɗuwa, ban san lokacin da nayi mazauni a gefen Hubbi ba ina damƙar gefen rigarsa.

"lafiya?".

a ruɗe kamar zanyi kuka na ce masa,"bata ɗaga wayar ba ne, kuma kaga miscall ɗinta biyar na tarar".

ganin yacca jikina ya ɗauki ɓari ya karɓi wayar daga hannuna, yana ƙoƙarin ƙara kiran sai ga kiran Hindatu na shigowa. ya ɗaga ya miƙo min amma sai na kasa karɓa don ban san me kunnuwana za su jiye min ba. shi ya amsa kiran sai dai maimakon muryar Hindatu naji muryar Ummani na cewa,"Sa'ida ina hanya ne shiyasa ban ɗaga ba, kuma na shigo gidan babu kati a wayar sai na ari ta Hindatu".

wata wawiyar ajiyar zuciya na sauke ina hamdala ga ubangiji, yayin da Hubbi su ka shiga gaisawa da ita yana shaida mata rikicwar da nayi akan rashin ɗaga kiran nata, bayan sun gama ƴar hirarsu ya miƙo min yana murmushin leɓe tare da tsokanata, wanda hakan ni kuma yasa raina sanyi, domin rabona da ganin annuri a fuskarsa har na manta balle kuma murmushi irin haka.
cikin wani irin jin daɗi mara misaltuwa mu ke waya da mahaifiyata, kira kawai tayi taji ya muke, ashe ma ko da ta bar min miscalls da yawa ba ita tayi kiran ba Yahanasu ta bawa, ita kuma dama bata iya kiran hankali ba, kusan kullum sai Abba yay mata faɗa akan hakan. muna wayar naji duk damuwata ta gushe, tana ta bani labarai masu daɗi, ni kuma ba ni da wani labari da zan bata wanda zai sanyata farin ciki, sai da naji muryarta ta fara sauyawa wadda ke shaida min tana ƙoƙarin gano cewar ina cikin matsala ne, sai nayi saurin gusar da tunanin hakan a ranta nima na bata labarin su Atika da aka bani, ina shaida mata cewar ma yau za a kawo su, aiko farin ciki kamar tayi me, taji min daɗi sosai tana ta yiwa su Yaya godiya da shi albarka, ta ce ma na bawa Hubbi shima tayi masa murna, ni kuma tayi min nasiha sosai a game da ruƙon yaran. sai kuma kawai naji ta koma ambaton wannan kyauta ce daga Allah na sameta ya bani ta silar wasu, na riƙe ƴaƴana da amana kar in cutar da su, yarda da aminta cewar zan kula da su yasa har iyayen yaran suka bamu duk da cewar sun yi domin ɗan uwansu ne, amma duk da haka don suna da yaƙinin matarsa mutuniyar arziƙi ce yasa su ka ba shi.

ƘAYAR RUWA Book 1 CompleteWhere stories live. Discover now