ZYNAH

De Ishamoha

77.8K 4.7K 61

Here is a story of a teenage hausa girl Zynah who happens to come from a wealthy nd peaceful family but was h... Mais

Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63

Chapter 33

1K 68 0
De Ishamoha

🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻

             *ZYNAH*

(An Interesting Luv Story 2017)

By Aisha Muhammad (Mzz Daddy 💋)

*BAIWA WRITER'S ASSOCIATION*

QUOTE:-"Great personality will always make you more attractive than someone who only has a great face."😎😊

              3⃣3⃣

     Suna shiga gida suka shirya suka fito, Abba yace *ASHRAF* ya dauki mota ya kaisu hotel su kwaso kayansu daga nan ya kaisu airport, ai kuwa nan da nan yaje ya fito da mota kirar Honda accord dan a wurin shi alfarma aka mishi, dan ze raka sahibarsa airport, sunzo tafiya Juwairiya tasa kuka ita seta bisu, da kyar aka lallasheta tayi shiru sannan su Daddy sukayi sallama suka kama gabansu, tafiya sukeyi a hankankali wanda duk dagowa in *ZYNAH* zatayi seta hada ido da *ASHRAF* ta mirror, suna hada ido ze sakar mata murmushi itama ta mayar mai da martani, a haka har suka karasa hotel din. Duka wannan bidirin da akeyi Fahad beda masaniya akai dan wannan weekend din besamu zuwa gida ba.

Sunkai hotel din matan kawai ne suka shiga ciki inda *ASHRAF* da Daddy suka wuce masallaci dan yin  sallar la'asar sannan duk suka sauko da kayansu, jirgin karfe 6 na yamma zasubi saboda haka 5 sukeso ya musu a airport, ai kuwa Allah ya taimake su rannan Sunday ne saboda haka ba'ayi hold up sosai a Kaduna ba ranan, kafin 5:30 har sungama abunda zasuyi suna jira a fara kiran masu tafiya, *ASHRAF* yaki tafiya ya tsaya yana hira da *ZYNAH* harseda Daddy ya lura dashi yace yakamata ya dau hanya saboda kar dare ya mishi a hanya, se a lokacin ya musu sallama tareda fita ya shiga motanshi ya dau hanya cike da kewan *DAMSEL* dinshi. Suma ba dadewa jirgin su ya tashi, *ZYNAH* dukda ta fara kewan *ASHRAF* wannan be hanata jin dadin yau zatayi kwanan gidansu ba, zata kwana a dakin ta, tayi barcin yanda takeso,(gida gidane, duk wanda yabar gida gida ta barshi).

     *ASHRAF* na kaiwa gida yafadawa  mahaifinshi cewar ya kaisu, kuma yanajin yanzu jirginsu ya tashi, Abba yasa mishi albarka sannan ya koma dakinshi, ai yana shiga ya tarar da Sameer a kan gadon shi yace "kai kuma shikenan dakina beda privacy, kashigo duk sanda kaga dama ka fita duk sanda kaga dama", Sameer ya mike zaune yace "mallam daga dawowanka ko hutawa bakayi ba zaka fara harzuko min, ni zo ka zauna, da magana nazo shiyasa na jiraka har kadawo", *ASHRAF* zuwa yayi yaja kujeran dressing mirror dinshi ya zauna yana facing din Sameer yace ina jinka, kallonshi Sameer yayi yace "naji wai Abba da mahaifin *ZYNAH* frnds ne?", "wannan shine maganan da zaka min, amma bakada serious", mikewa *ASHRAF* yayi ze bar wurin Sameer yayi saurin rikemai hannu yace "tsaya mana, ni ba wannan ba, to b serious akwai maganan da zanma, nd i hope u will give me a helping hand", zama *ASHRAF* yayi tareda cewa "y nt, indai befi karfina ba am willing to help", "befi karfinka bama, kasan wani abu, i hav a crush on ur sister", "i already knw abt dat", "wat, hw did u knw", "ai ni na dade da sanin kanason Minal, dama jira nake naji zaka fito ka fada ko kuwa", sauke kai Sameer yayi sannan ya dago ya kalli *ASHRAF* yace "u ar mistaking, ni ba Minal nakeso ba", cike da mamaki *ASHRAF* yace "inba Minal kakeso ba toh wa", kai tsaye yace mishi "Basma", kallonshi *ASHRAF* keyi sannan daga bisani yace "all dis while u've been fond of Minal, in ka ganta kata janta da wasa kenan kuna hira kuna dariya, den y all of a sudden kace Basma kakeso?", "look *ASHRAF* i want u to understand something, ina wasa da dariya da Minal ne badan komai sedan u guys a close nd abunda yasa nima nayi close da ita kenan bawai dan inasonta ba, whereas Basma kuma tun tasowanta nake dauke da dakon sonta a zuciya na, kuma naga yanzu ne lokacin da ya kamata in fito in gayamata kar wani ya rigani, kagane", ajiyar zuciya *ASHRAF* ya sauke sannan yace "na fahimci ka dari bisa dari amma zaka iya fada min abunda yasa kakeson Basma?", "well,  ba komai yaja hankali na zuwa ga Basma ba illa, Basma akwai gayu, ga kyau, ga iyayi,ga tsiwa sannan uwa uba ka jan aji", dariya  *ASHRAF* yayi yace "Lalle kanada jan aiki dan in Basma ce zakaga iyayi da tsiwa, nidai nabaka go ahead kaje ka sameta kuyi magana", "a'a *ASHRAF* ba haka zamuyi da kai ba, inaso kai kafara zuwa mata da maganan sannan daga baya ni se inje", "a'a baza'ayi haka dani ba dan banson raini, kaje kamata magana wannan tsakaninku ne", yana gama fadan haka ya tashi yasoma cire kayan jikinshi dan ya watsa ruwa, shikuwa Sameer tunani ya shigayi na yanda ze tunkari Basma dan yaga alaman *ASHRAF* ba taimaka mishi zeyi ba.

      Karfe 9 na dare *ASHRAF* ya dau waya ya kira *ZYNAH* amma be shiga, wannan ya tabbatar mishi da basu sauka ba tukun, 9:30 jirginsu ya sauka, suna fitowa Uncle Yusuf yazo ya daukesu, cikin mota ta kunna wayanta wanda tana kunnawa kiran *ASHRAF* na shigowa, kashewa tayi sannan ta tura mai text cewar "sun sauka suna cikin motane, in ta kai gida zata kirashi", tafiyan 30min yakai su gida, duk sun gaji saboda haka suna zuwa gidan bayan sun gama gaishe gaishen su da masu aiki duk sukayi daki sukayi wanka tareda sallolin da ake binsu sannan suka sauko dan Jummalo ta musu girki,  suna gama cin abinci kowanen su yayi daki, *ZYNAH* na shiga daki ta dau wayanta ta soma kiran *ASHRAF*, kashewa yayi sannan ya kirata sukasha hiransu sannan daga baya tace mishi barci takeji sukayi sallama ta kwanta, bajewa tayi a kan gadonta sosai tareda cewa "i miss u my luvly bed, i knw u miss me too", sannan tayi kissing din gadon taja comforter, ba dadewa ta dauke wuta,(toh madam *ZYNAH* a tashi lfy). Da asuba da kyar ta tashi tayi sallah saboda gajiya, nan inda tayi sallah ta kwanta taci gaba da barcinta. Karfe goma na safe gidan kowa ya tashi Daddy har ya tafi office, Uncle Yusuf ma ya wuce aiki, Islam ma ta wuce school, amma gimbiya na nan na barci, Momcy ce ta fito taga dinning ba'a kwashe kullolin da sukayi breakfast dashi ba ta tambaye Jummalo, Jummalo tace " Hajiya *ZYNAH* ce batazo taci abincin ta ba", girgiza kai Momcy tayi tace "wannan yarinyar har yanzu bata canza ba kenan", sannan ta haura sama, shiga dakin *ZYNAH* tayi ta ganta kwance a kasa tana barci, karasawa tayi tana tashinta wanda da kyar ta iya bude ido dan ji take kaman an mata duka, "tashi kiyi wanka, kizo kici abinci seki koma barci", da kyar ta amsa da "toh", sannan Momcy ta fita.

     Da kyar ta tashi ta shiga bathroom tayi wanka, ta fito ta shirya sannan ta sauka kasa, koda ta sauka Momcy na parlour, ta gaisheta sannan ta koma kan dinning taci abincin ta, tana gamawa ta wuce sama, wayanta ta dauka taga 5 missed calls, biyu daga *ASHRAF*, daya daga Humaira, daya daga Shaheeda, se last one din daga Ashanty, taso tasake kiransu amma kuma tana so tayi barci kuma tasan muddin ta kira *ASHRAF* toh ba ita ba barci, ajiye wayan tayi, ta kwanta tareda jan comforter ai kuwa nan da nan barci ya dauke ta, Karfe 1:30 Humaira ta fado gidan, ba kowa a parlourn se motsi da takeji a kitchen, kitchen ta shiga taga Jumallo na juye abinci a cooler, nan ta gaishe da ita sannan taje ta dauko plate tace a zuba mata taci dan yunwa takeji saboda daga school take, ba musu Jummalo ta zuba mata tana mata dariya, sama ta nufa da abincin a hannunta, dakin Momcy tafara shiga saboda Jummalo tace mata tana daki, da sallama tashiga Momcy ta amsa tareda cewa "Humaira ce a gidan yau, lalle, wato dan kawarki ta dawo ko, aini nayi fushi tunda bakya zuwa se in *ZYNAH* na nan", karasawa tayi ciki tana cewa "Momcy ba haka bane, wlh school ne yasani gaba, yanzu haka ma mun fara test", "OK, toh ya karatu", "alhmdllh", "toh a maida hankali sosai, jiya ma munyi waya da mamanki take cemin karatu yasa bakida lokacin kowa yanzu", "wlh Momcy ba sauki bane, ai ni naga kokarin *ZYNAH* ita me karatun medicine", dariya Momcy tayi tace ke bazaki iya ba kenan?" ,"kaiii gaskiya bazan iya ba, nida ko jini nagani se tsigar jikina ya tashi ina ni ina medicine ko nursing, gwara dai pharmacy dina, ya fiye min", dariya Momcy tayi tace "kinjiki da wani zance, ga abincinki na sanyi, *ZYNAH* na daki", Humaira tace "nasan bacci takeyi", "ai kema kinsan aikinta kenan", tashi tayi tace "bari inje in tashe ta", tana shiga dakin taga *ZYNAH* kududdine cikin bargo wacce ta dade da tashi amma tayi kaman tana barci dan taji shigowan Humaira, Humaira zuwa tayi ta ajiye abincin ta akan tebur dinda *ZYNAH* ta jera kayan system dinta akai na computer sannan ta ajiye jakanta da mayafi tayi kan *ZYNAH*, yaye comforter din tayi sannan ta dane kan *ZYNAH* ta fara mata chakulkuli, tun *ZYNAH* na gimtse dariyan ta harta kasa ta sake dariya me dadin saurare tareda fadin "dan Allah dena, wayyo Allah na, bestee dan Allah dena", tana fada tana dariya, sakinta Humaira tayi, gabadayansu suka dinga maida numfashi, seda ta nutsu sannan ta mike zaune itama Humaira ta tashi zaune suka kalli juna sekuma sukasa dariya sannan suka rungume juna tareda exchanging i miss u da miss u too, sakin juna sukayi sannan Humaira ta tashi ta dauko abincinta ta soma ci tareda cewa "so,  wats up, gist me nw, hw hav being, ya school, ya Zaria nd most importantly ya boo boo dinki", pillow *ZYNAH* ta wurga mata tareda cewa wani boo boo kika bani?", Humaira na dariya tace "kin fini sani ai", dariya sukayi gabadayansu sannan suka shiga hiran da baya karewa, suna cikin hira Humaira taga alamun wayan *ZYNAH* na flashing wuta alaman ana kira,  nuna mata wayan tayi ta dauka, taga *ASHRAF* ne kira,  murmushi tayi tace "shike kira", "dauka toh kar ya tsinke", dauka tayi tareda cewa "hello yayana ina wuni", yace "ban wuni ba,  wato har kin manta dani ko", tace "a'a wlh, na saura ina baccin gajiya ne, se yanzu bestee dina tazo ta tashe ni", "i see, toh ykk, ya gd, ya kowa da kowa, ya bestee dinki?", "duk lfy lau, bestee gatanan wai tana gaida kai", "bani ita mu gaisa", nan ta mikawa Humaira waya suka gaisa wacce muryan *ASHRAF* da taji yasata rudewa, mikawa *ZYNAH* wayan tayi sukaci gaba da hiran su, wanda ba dadewa sukayi sallama tareda kashe wayan, tana ajiye wayan Humaira tace "ni kuwa wannan *ASHRAF* ban taba ganinshi ba koh a hoto,
swthrt kodai rowanshi ake mana?", *ZYNAH* tace "lahhh, bestee yi hakuri bari in nuna miki shi", tareda dauko wayan tashiga gallery take ciro hoton *ASHRAF* ta nuna mata, kallon hoton takeyi bako kyafta ido, a zuciyarta tace "aminci ya tabbata ga Allah wanda ya halicce dan adam sannan ya fifitashi akan duk wani abu da ya halitta a doron kasa", mikawa *ZYNAH* wayan tayi tace "naga abunda yasa ake mana, rowanshi", dariya *ZYNAH* tayi tareda kaima Humaira duka tace "ke kika sani", hiransu sukaci gaba dayi, karfe shida Humaira ta wuce gida, *ZYNAH* na dawowa daga rakiyan Humaira taje wurin Momcy ta tambaye ta meyasa  Islam bata dawo ba,  "Momcy naga har past six amma Islam bata dawo ba", "eh, Daddyn ku yasata a extra lesson saboda zukancin ta", *ZYNAH* batace komai ba illa tashi da tayi ta nufi dakin Islam inda ta bude drawer dinda Islam ke ajiye school accessories dinta ciki, nan taga script din Islam na test dana exam which she performed woefully a result dinda girgiza kai tayi tareda daukan alwashin seta canza Islam kafin ta koma school. (Is dis possible? mu dai je zuwa).

     _Mzz Daddy 💋✍🏻✍🏻_

Continue lendo

Você também vai gostar

1M 87.7K 102
(Unicode & Zawgyi) ပင်လယ်နဲ့တူတဲ့ ဘ၀.. လှေငယ်နဲ့တူတဲ့ သူ.. မုန်တိုင်းကြားမှာ ခရီးဆက်နိုင်ပါစေ..
493K 89.4K 177
Fan translation of 这个电影我穿过 [I've Transmigrated Into This Movie Before] Author 梦魇殿下 [Mèngyǎn diànxià (Her Highness, the nightmare)] ...
3.2K 334 13
Hi guys. ඔන්න මමත් කතාවක් ලියන්න පටන් ගත්තො 😁. මේක mafia mix love story එකක්. මූලින්ම කියන්න ඔනී මේක +🔞, +21 තියෙනවා ඒත් මම කියන්නෙ නෑ මේක පොඩි අය...
33K 6.7K 61
"Do you think betrayal never gonna pay back?" Come on let's go and seek it! One line ⬇️ It's a crime thriller love story. All based on 2 best frien...