AƘIDA TA

Par Ayshercool7724

20.4K 1.2K 102

Labarin wata matashiyar budurwa 'yar hamshaƙin attajiri me murɗaɗɗiyar AƘIDA, Tace So imagination ne da ɓata... Plus

AƘIDA TA
AƘIDA TA
AƘIDA TA.
AƘIDA TA
CHAPTER 6
AƘIDA CHAPTER 7
CHAPTER 8
AƘIDA TA CHAPTER 9
AƘIDATA CHAPTER 10
AƘIDATA CHAPTER 11
AƘIDATA CHAPTER 12
AƘIDATA CHAPTER 13
AƘIDATA CHAPTER 14
AƘIDA TA CHAPTER 15
AƘIDATA CHAPTER 16 _17
AƘIDATA CHAPTER 18
AƘIDATA CHAPTER 19 And 20
AƘIDATA CHAPTER 21_22
AƘIDATA CHAPTER 22_23 (DESTINY)
AƘIDATA CHAPTER 24_25
AƘIDATA CHAPTER 26_27
AƘIDATA CHAPTER 28_29
AƘIDATA CHAPTER 30_31
AƘIDATA CHAPTER 32_33
AƘIDATA CHAPTER 34_35
AƘIDATA CHAPTER 36_37
AƘIDATA CHAPTER 38_39
AƘIDATA CHAPTER 40_41
AƘIDATA CHAPTER 42_43
AƘIDATA CHAPTER 44_45

AƘIDA TA

677 42 0
Par Ayshercool7724

_*AƘIDA TA*_

*PART1*
_Page 2_

*written and edited by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*

Bismillahir rahmanirrahim, da sunan Allah me Rahama me jin ƙai, Wannan littafi ƙirƙirarren labari ne banyi shi dan cin zarafi ko cin fuska ga wani ko wata ko wata ƙabila ba, idan har wani ko wata yaga wani abu daya yi kaman ceceniya da rayuwar sa ko ƙabilar sa Amin Afuwa banyi dan cin zarafin wani ko wata ba.
Wannan littafin mallaka tane, ban yadda a juyamin labari ta kowane fanni ba ba tare da izinina ba.

What's App : 07063065680
Watpad : Ayshercool7724
Gmail : Www.ayshertadam@gmail.com

************************************

Wata Babbar Mace ce Zaune a cikin wani katafaren falo me girma sosai, cike yake da kayan more Rayuwa, Aƙalla zata kai shakaru hamsin, Amma kaman 'yar shekara talatin da biyar saboda hutu idonta sanye da glashi ta nutsu sosai tana danna Computer tana shan tea.

Wata matsashiya ce ta shigo falon a ƙalla za ta kai shekaru Ashirin da bakwai, tazo ta zauna a kusa da Matar.
Ba tare da Matar ta ɗago ba tace "Ya a kayi ne? Nasan akwai damuwa tunda na ganki yanzu meya faru?" ta ƙarasa maganar tana kallon matashiyar.

Ta ɗan yatsuna fuska tace " Mummy kin san wani abu?"

"A'a sekin faɗa" matar ta bata Amsa

Cikin shagwaba tace "Mummy ki duba girman gidan nan da cikar sa, kalli dukiyar dake cikin gidan nan, Amma mota ɗaya tak na mallaka, ko ɗan direba ma ba'a sama min ba, Amma kalli 'yar masu gida motocin ta nawa? Direbobi nawa ta wulaƙanta ta sallama a dawowar nan tata? Har motocin me gidan nan take hawa in ta ga dama gaskiya ana nuna mana wariyar launin fata, banda cin fuska da wulakanci da muke fuskanta seka ce wasu Bayi"

Matar ta cire glashin fuskarta tace

"Ramlah me kike so inyi? Alhaji Baya jin magana ko ganin girman kowa sena 'yar sa, abunda take so shi yake yi, Sannan duk abubuwan nan da suke faruwa na ɗan lokaci ne, Amma me kike so ayi? "

"Mum Mota nake so a canzamin sannan nima a ɗaukar min direba, bama mota ba motoci nima in dinga kece raini yadda yakamata, kalli daular da muke ciki, Amma a ce se abunda yarinya ƙarama take so akeyi, Mummy ina son inyi birthday ina buƙatar kuɗaɗe masu yawa fa wanda zan burge ƙawaye na dasu, Sannan naji labarin Akwai filayen da gwamnati za ta yi gwanjonsu a GRA ya kamata ace kin mallaka"

"Hmm Ramlah kenan samun wannan abubuwane masu Sauƙin samu a hannun me gidan nan, Amma kin san seda izini kokuma ince yaddar 'yarsa ko?"

Ramlah tace "Amma Mummy ba yadda za' ayi in samu kuɗin a hannun ki? Kina matarsa amma ace se Abunda 'yarsa take so haba dan Allah, yakamata ace Akwai wata Dama da zaki dinga mallakar kuɗaɗe bayan wanda yake baki"

"babu wannan damar, dan duk kuɗin dazan fitar seda sanin Lawyern sa, dan haka ba yadda zanyi, Karki manta muna da kyakkyawan shiri a ƙasa shiyasa sam bana damuwa, ni yanzu so nake in lallaɓa shi Amal me ta tafi turkey ta ci gaba da karatu a can"

Ramlah tace
"shikenan Amma yakamata kiyi wani abu akai kar wannan damar ta wuce mu, Amma kafin wannan ya batun canza motarfa?"

Mummy tace "Wannan kuma sekin yi tsani da 'yar masu gida, tana magana ko mota goma kike so kamar kin samu, batun kuɗi kuma zan tura miki kuɗi Account ɗinki base munjira ba, Amma ki same ta in ta yadda za tayi masa magana a baki wata motar"

Ramlah ta yamutsa fuska tace
"A' a Mummy ke zaki mata magana, kin san ba shiga sabgarta nake ba, bana son wulaƙanci da rainin hankali, kin san bama shiri da ita"

Mummy tace "ke kina tunanin idan nayi mata magana zata saurare nine? Yau kwana biyar rabon da in sata a idona fa yarinyar nan barta kawai"

Ramlah tace "bari in kira miki ita dan Allah ki mata magana ko zata sa baki, ni kin san bama jituwa da ita"

Mummy ta ɗan jinjina kai tace "shikenan Allah yabada sa'a"

Tana zaune akan stool a gaban dressing mirror ɗin ta wanda yake shaƙe da kayan shafe shafe na mata, towel ne a jikin ta tana ta ƙoƙarin tsane gashin kanta.
Ƙofar ɗakin aka turo aka shigo, wata matashiyar budurwar ce ta shigo ɗakin ba tare da tayi sallama ba ko wata doguwar maganaba tace

"Mum nasan ganin ki a cikin gida, zakuyi magana"

Wadda akewa maganar se kace da gini ake, ko gezau ba tayi ba ta ci gaba da abunda take yi, bata kalli me mata maganar ba ta cigaba da abunda take yi .
Cikin ƙosawa da fushi matashiyar wadda aƙalla ta girmi wadda take wa maganar nesa ba kusa ba tace

"wai ba kyaji ina miki magana ne? Kin min banza kaman baki san na shigo ba?"

Cikin isa yarinyar ta Ajiye Ƙaramin Towel ɗin hannun ta, ta miƙe ta nufi wardrobe ɗin ta, Subhanallah koda ta buɗe wardrobe ɗin sutura ce a ciki kaman shara, kamar inji ne ya shirya kayan ba hannu ba, kai in akace suturar mutum ɗaya ce seka riƙe baki tareda tunanin ina mamallakin suturar ze kai ta?

Ta saka hannu ta janyo wata 'yar riga ja mara hannu, tana ƙoƙarin sakawa ba tare da ta waigo ba cikin ƙasaita tace

"Ramla ki koma ki gayawa wadda ta aiko ki banyi budget da lokacin da zan bata ba a yanzu, ko menene idan ta damu tazo da kanta ta sameni in gani ko zan iya saurarta, idan kuma bame mahimmanci bane zata iya haƙura har se lokacin da Allah yasa na shigo cikin gidan, you can go out i need privacy"

Cikin ɓacin rai Ramla tace "Waike wace irin mara ɗa'a ce haka? Mahaifiyar tawa ce zata zo ta same ki? Kika san me yasa ta kira ki? Se kace sa'ar ki?"

"koma me zesa ta kira ni nasan baze wuce biyan wata buƙata tata ba kokuma ta 'ya' yan ta, ni kuma da ku da ita bani da lokacin ku a yanzu, ɗan fitar min daga ɗaki, zan kaɗaice inyi tunani"

Ramla tace "Amma baki da kirki, a gabana kike faɗan maganganu akan uwata, ke har Abada girma da shekarun mutum baya sa ki bashi girma, Ko ance miki rayuwar Turai hauka ce? Rayuwar turai fa ta saɓa da Al'adunmu, Ko kuma akanki aka fara Arziki?"

"Enough Ramlah" Yarinyar ta katse ta ta nuna Ramlah da yatsa ta ɗora da cewa

"Amma kamar kin san ba'amin shouting ko? You know the consequences of doing that. Mahaifiyar ku, ku ta haifa, ni kuma Babana take Aure bata haifeni ba, what's the meaning of respect according to you ne Ramla? Your mother is just a human being like everyone, she don't deserve any special respect, i will treat her the same way i treat every human being, and mark you This is my father's house, if you are tired of what am doing, go back to your father's house, nan gidan mahaifina ne ina da right inyi abunda nake so, and no one should stop me from doing what I want, if you are tired of what am doing park your things and go, madam get out from my room, kaina ya fara ciwo ki fitar min daga ɗaki "

Cikin faɗa take maganar, hannun ta ɗaya riƙe da kanta, tana nunawa Ramlah ƙofar fita

Ramla ta ƙulu matuka ta fice a fusace tare da buga ƙofar ɗakin da ƙarfi.

Falo ta koma inda tabar mahaifiyar ta, kallo ɗaya Mummy tayi mata ta ɗanyi murmushi tace "yana ganki a fusace?"

"Mummy wallahi yarinyar nan bata da mutunci, kinga rashin mutuncin da tamin kuwa, wallahi badan ina gudun abunda ze biyo baya ba sena shaƙeta kowa ya huta"

"hmm Ramla kenan, baki ga komai akan halin ta ba, ni da nake tare da ita ni nake ƙunsar takaici da baƙin ciki, Amma ina jiran lokaci ne wanda...
Bata ƙarasa ba tai shiru tareda yin murmushi ta dafa kafaɗar Ramla tace "karki damu daughter, saura ƙiris komai ya canza, na sama ya koma ƙasa, na tudu ya koma ruwa, a wannan lokaci da dariya zata gagari kare, hmm kiyi hakuri ni da kaina zan canza miki mota, in ɗaukar miki driver kinji?"
Shiru Ramla tayi ba tace komai ba se faman huci da take yi. kaman an mintsine ta tace

"wallahi na tsani yarinyar nan Mummy, bana ƙaunar ganin ta ji yadda aka maida ke da mu kaman wasu bayi ko 'yan Alfarma a gidan nan, ai ko Albarkacin kina Auren mahaifinta ya kamata ace muna da matsayi na musamman"

Mummy tace
"nifa nace kiyi hakuri ko? Komai ya kusa zama tarihi"

********

Yusuf Yana zaune har Bayan sallar isha'i yana kallon labarai, yaji anyi Sallama amsa sallamar yayi tareda ɗan ɓata rai.
Me sallamar ta shigo falon ta ajiye jakarta da mayafi ta ɗan kalli inda Yusuf yake tace
"fushi kuma ake dani, ko a kalli inda nake? Ai gani na dawo"

Yusuf yace "haba Umma tun azahar kika fita se yanzu bayan isha'i duk kaɗaici ya dameni"

Umma tace "kai tafi can, sekace wanda nake shayarwa ba damar in ɗan fita, ka dinga damuwa kenan"

Cikin shagwaba yace "wana keda shi inba Ummana ba? Dole in shiga damuwa duk lokacin da kikayi nisa dani ummana, daga Allah seke se kuma Aikina ku kenan nake da su, niba Abokai ba ko wasu mutane na musamman ke ɗin ce dai, Allah ya jiƙan Abba na, tun abunda ya faru Umma ke kaɗai nake da yaƙinin ƙaunar ki a gare ni baza ta gushe ba, shiyasa bana son kiyi nisa dani"

Tausayin Yusuf ne ya mamaye ta, har zuciyar ta ta karaya hawaye na ƙoƙarin fita daga idon ta, da sauri ta fice ta bar ɗakin da nufin yin Alwala.

Bayan Umman Yusuf ta idar da sallar isha'i suka ci Abincin dare tare suna hira, Yusuf yana ta so ya sanar da Umman sa batun Aikin da'aka bashi a Office amma ya kasa, dan yasan idan har ya gaya mata ranta zata ji babu daɗi, ace ɗanta Yazama direban yarinya, Yarinyar ma mara tarbiyya wadda bata san darajar ɗan Adam ba, dan haka ya bar abun a ransa be gaya mata ba.

Haka ya kwana yana tunanin wace karɓa ze samu a gurin yarinyar nan? Ya aikin ze kasance? Haka yaita tunani har bacci ya ɗauke shi.

Washegari ma Yusuf yayi ƙoƙarin yiwa Umman sa zanncen amma ya kasa, haka yai breakfast ya tafi gurin Aiki.

A office ma kasa wani aikin kirki yayi, wayar sa ya ɗakko yana kuma duba hotunan wannan tsaleliyar yarinyar, ya kuma tuna irin halayen ta da Abbas ya bashi labari. Ɗan tsaki yayi ya ajiye wayar ya jingina da kujera ya dafe kansa yana tunani.

Sallamar Abbas ce tasa ya ɗago kansa, Abbas yace "Yusuf dama ka shigo yau baka nemeni ba?"

"na shigo tun ɗazu ina aiki ne shiyasa ban neme ka ba"

"OK tashi muje, Yallaɓai Suleiman na son ganin mu yanzu"

Yusuf ya miƙe yabi Abbas suka fice, suna zuwa suka gaisa cikin girmamawa, yai musu umarni suka zauna.

Yallaɓai Sulaiman yace "Yusuf nace kuzo tare da Abbas ne dan tabattar da cewar aikin da muka ɗora muku zaku iya, mussman kai Yusuf nasan kana da kula da aiki kuma kana da haƙuri matuƙa"

Cikin girmamawa Yusuf yace "Insha Allah Yallaɓai baza'a samu matsala ba"

"Good kayi taka tsan2 kabi a hankali, karka kuskura wani yasan bincike ne ya kaika gidan, kasan aikin ka base na gaya maka ba, samun matsala a wannan aikin gagarumin hatsari ne da kuma Asara ina fatan kun san hakan"

Yusuf ya risinar da kai yace "Insha Allah ba zamu baka kunya ba sir"

"kai kuma Abbas ku kula yadda ya kamata"

Abbas yace "Insha Allah sir za muyi iya ƙoƙarin mu"

Haka suka ci gaba da tattauna wa akan harkar aiki, sannan Yallabai Suleiman ya sallame su.

Bayan fitowar su Abbas yaita bawa Yusuf ƙwarin gwiwa tareda bashi shawarwari, suka tsara yadda tafiyar tasu zata kasance ranar Asabar zuwa gidan Alhaji Nasir Daula.

Tunda gari ya waye Asabar gaban Yusuf yake faɗuwa, ya rasa dalilin da yasa tun da'aka gaya masa Aikin daze yi yaji gaban sa na faɗuwa a duk sa'ar daya tuna, har seda Umman sa ta fuskanci ya rage walwala, ta tambayeshi yace mata "bakomai" haka Yusuf yaci gaba da Adduo'i.

Yana nan zaune a ɗakin sa ya rasa abunda yake masa daɗi, misalin ƙarfe sha ɗaya na safe Abbas yazo, ya tsaya a tsakar gida suka gaisa da Umman Yusuf sannan ya shiga ɗakin ya same shi.
Abbas ya kalleshi daga sama har ƙasa yace

"gaskiya Yusuf wannan kayan naka ba suyi kama da wanda zeyi aikin direba ba, gaskiya ka canza kaya, ni baka ga kayan da na saka ba"
Se lokacin Yusuf ya lura da koɗaɗɗen Yadin dake jikin Abbas, Yusuf ya ɗanyi murmushi yace "Taɓɗijan, wannan wane irin kaya ne?, ni ban san wani kaya zan saka ba"

Abbas ya buɗe wardrobe ɗin Yusuf, duk kayan Yusuf masu kyaune, da ƙyar ya ɗakko masa wasu ƙananan kaya ya bashi ya saka suma dai basu ji jiki ba, Yusuf ya karɓa ya saka, yace "Allah yasa kar Umma tayi min magana akan kayan nan"

har zasu fita Abbas yace "ɗan tsaya idan muka je gidan Sunana Sani me mangwaro ba Abbas ba "

Yusuf ya jinjina masa kai sannan suka fito, Yusuf ya kalli Ummansa dake kwashe kayan wanke2 yace "Umma zamu fita"
Umma tace "to Yusuf, Abbas ka gaida gida sekun dawo"

Har zasu fita Umma ta kira yusuf tace "Yusuf zo nan"
Dawowa yayi tace "Wannan wace irin shiga kukayi, kalli kayan jikinka be kamata ace ka fita da su ba, Allah ya rufa maka Asiri amma kasa wannan kayan kana yawo a gari"

"Umma shima hakan cikin harkar Aiki ne, idan na dawo zan miki bayani Insha Allah"

Umma tace "Amma harkar aiki shine zaka fita da wannan suturar kamar mara galihu"

"haba Umma wallahi kayan nan da kyansu, kiyi min Addu'a sena dawo"

Ɗan girgiza kai tayi yayin da Yusuf yayi waje da sauri.

Napep suka tara suka hau zuwa gidan Alhaji Nasir, yayin da gaban Yusuf keta faɗuwa.
Tun daga bakin layin shiga rukunin gidan jam'ian tsaro ne ke kaiwa suna komo wa, seda aka musu tambayoyi kafin su wuce da yake sun gane Abbas yana zuwa, aka barsu suka wuce.

Koda suka je gidan Abbas ne ya sallami me Napep ɗin, tun daga waje Yusuf ya fara ƙarewa gidan kallo tirƙash lallai mamallakin gidan yaci ai masa inkiya da Daula.
Suka ƙarasa ƙofara katafaren gate ɗin suka tsaya, Abbas ya ɗakko wayarsa ya kira Isa me gadi, yace masa suna waje.
Befi mintuna uku ba aka buɗe ƙaramar ƙofar dake jikin gate ɗin ya leƙo yana ganin su Abbas ya washe baki yace

"bismillah ku shigo Ashe kaine"
Suka shiga suka tsaya suka gaisa da Isa.
Isa yace "Sani wannan ne ɗan uwan naka daze aikin?"

Abbas yace "Eh shine"
Isa yace "Ya sunan shi?"

"Sunana Yusuf" Yusuf ya bashi amsa

Isa yace "masha Allah to Allah yaba ka iko, dan seka yi haƙuri aikin akwai samu amma babu sauƙi, bari inje in sanar wa da Alhaji zuwanku"

Abbas yace "shikenan babu laifi"

Bayan tafiyar Isa, Yusuf ya kalli harabar gidan, wasu irin motoci ne masu rai da lafiya a tsaye a gefe ɗaya, yayin da ainihin ƙofar shiga katafaren gidan se kayi wani gajeren tattaki daga gate ɗin kafin ka kai ga ƙofar.
Yusuf ya numfasa yace

"wai ni Abbas ya aka yi rukunin gidajen nan jam'ian tsaro ke gadi, Amma kuma nan gidan naga wannan ma shiriricin ke gadi"

Abbas yace "Sani dai ba Abbas ba"

Yusuf yace "Am sorry, Sani"

Abbas yace "duk yana cikin binciken da za kayi, ka kula kayi taka tsan2, banda sakin jiki da kowa dama nasan kai ba me son hayaniya bane"

Isa ya dawo yace "bismillah ku taho mu shiga, Alhaji yace a shiga daku"

Tunda suka kama hanyar shiga cikin gidan Yusuf yake ƙarewa ko ina kallo, an danƙarawa gidan dukiya kaman ba'a san ciwon ta ba.

Wasu irin faluka suka dinga ratsawa, kowanne da kalar sa da irin tsaruwar da yayi, shikan sa Abbas be san haka cikin gidan yake ba.

Sunyi doguwar tafiya kafin su iso wata ƙatuwar ƙofar glashi,Isa yasa hannu ya murɗa suka shiga da sallama.

Iya girman falon nan ya ishi wani talakan gina wadataccen gidan da ze zauna, Yusuf ya fara tambayar kansa shi kuwa wannan wane irin sana'a yake yi da har ya gina wannan gidan kamar baze mutu ba?

Babban mutum ne a zaune akan wata luntsumemiyar kujera yana karanta jarida gefen sa da wata mata, se 'yan mata biyu zaune akan kujerar dake facing ɗin su.

Aka amsa musu Sallamar, cikin girmamawa suka gaisa da me gidan tare da iyalan sa, yanayin gaisawar tasu ze nuna maka mutum ne me fara' a, dan kuwa fuskarsa ɗauke da murmushi ya amsa musu.

Isa yace "Yallaɓai sabon driver ne da kace a samo, shine suka zo yanzu"

Ya ajiye Jaridar hannun sa yace "Masha Allah wanne ne daga cikin su?"

Cikin girmamawa Yusuf yace "Nine"

Alhaji Nasir ya ɗan ƙura masa ido yace "masha Allah, ya sunan ka?"

"Suna na Yusuf"

Alhaji Nasir ya jinjina kai yace "Hajiya Halima kinji me sunan Yaya na ko?"

"Aikam dai me sunan shi" ta amsa

Alhaji Nasir yace "Allah sarki, Allah yasa me irin halin sa ne, ni duk Yusuf ɗin dana sani mutanen kirki ne, ina fatan kaima haka?"

Abbas yace "Alhaji ba ganin ido ba Shima mutumin kirki ne sosai"

Alhaji yace "ai dama na sani, ban taɓa ganin Yusuf mutumin kawai ba"

Ya kalli 'yan matan nan dake zaune yace "Amal jeki part ɗin gimbiya ta, ki gani idan idon ta biyu bata komai ki gaya mata Daddy na son ganin ta, idan kuma da abunda take yi ki ƙyaleta"

Wadda aka kira Amal ta miƙe tare da cewa "to Daddy" .

Babban abunda ya bawa Yusuf mamaki be wuce tun lokacin da' aka ce shine ze zama direban, matar da 'yan matan nan suke binsa da kallo ba, mussman wadda aka kira Amal yadda ta tsare shi da idanuwa.

Seda akayi Minti goma sha biyu da tafiyar Amal, sannan ta dawo tace "Daddy tace tana zuwa"

Alhaji Nasir yace "to babu laifi"

Wasa2 seda sukayi minti Arba'in ba suga Alamar wadda aka kira ɗin zata fito ba, iyalan suka ci gaba da hirar su aka bar su Yusuf shiru kamar mayu.

Gaba ɗaya Yusuf ya gaji da zaman, ga sanyin A. C da kallon ƙurillar da'ake masa duk yabi ya takure.

Alhaji Nasir ya kuma cewa "Ramla bawa baƙin nan Abinci kafin ta zo"

Ba tare da Ramla tace komai ba ta miƙe ta fice, ruwa da fruits ta kawo ta ajiye musu.

Abbas da Isa suka dinga ɗauka suna ci suna kallon tv, shikam Yusuf ya kasa cin komai, gaba ɗaya a takure yake, gashi ko ɗaga kai baya son yi saboda kallon da'ake masa.

Kaman ance ya ɗaga kai idonsa yayi tozali da wata irin kyakywar halitta, babu shakka itace a jikin hoton da Abbas ya tura masa, Amma a zahiri tafi haka kyau, gabansa ne ya dinga faɗuwa ƙirjinsa yana bugawa da ƙarfi, yarinya ce sharaf amma se kwarjini fara ce ƙal tana sanye da skin tied iya gwiwarta, se wata over size shirt data saka har wajen gwiwarta, kanta babu ɗan kwali gashin ta a hargitse babu ribbon, ta sake shi a kafaɗun ta.

Fuskarta a haɗe babu annuri, ta ƙaraso cikin falon ta zauna kusa da mahaifin ta. Tana zama Hajiya Halima ta miƙe ta canza wata kujerar

Alhaji Nasir yace "Lovely daughter ina fatan ba'a takura miki ba?"

Girgiza masa kai tayi alamar A'a

Alhaji Nasir yace "Sabon driver ne gashi nan, yazo ki gani in yayi miki"

Kamar baza tace komai ba ta ɗago ta kalle su ɗaya bayan ɗaya ta tsaida idon ta akan Yusuf ta ɗan ɗau lokaci tana kallon sa kaman tana ƙoƙarin gano wani abu.
Ɗauke kai tayi ta haɗe rai cikin isa tace

"Ramla kawo min madara da cup, sannan kije falona ki kawomin wata folder akan kujera"

Waigawa Yusuf yayi ya Kalli wadda aka kira Ramla, ta girmi yarinyar da har yanzu be san sunan ta banesa ba kusa ba, dan shi har yanzu beji wanda ya faɗi sunan ta ba, ramla ta miƙe ta tafi cika umarnin ta.

Yarinyar da dudu bata fi shekaru sha takwas zuwa sha tara ba, a idon ta da yadda take magana zaka gano tsabar izza, da isa, Ta kalli Abbas tace "kai kaman na sanka ko?"

Abbas yace "eh ni abokin Bala ne, ina zuwa gurin sa"

"good, kai Bala meye aikin ka?"

Cikin Rawar jiki yace "gadi ranki ya daɗe"

"to ka tashi da kai da shi ku fita ka koma kan aikin ka"
Ba musu bala ya miƙe, Abbas ma ya miƙe, kafin su bar falon ta kalli Hajiya Halima tace

"Madam i need privacy you can leave"

Ɗan taɓe baki Hajiya Halima tayi ta miƙe ta nufi wata ƙofar daban.

Ta kalli inda Amal take ta mata wani kallo, tun kafin ta furta komai Amal ita ma ta miƙe ta nufi barin falon.

Gaba ɗaya mamaki ya cika Yusuf, yadda take wannan izzar take wa manya magana babu respect kuma a gaban mahaifin ta amma bece komai ba, ya ma maida hankali akan jaridar sa kaman be san me take yi ba.

Ramlah ta dawo ɗakin ɗauke da cup da madara tazo ta ajiye, sannan ta miƙa mata folder, taje ta nemi guri akan kujerar da ta tashi zata zauna, Amma suka jiyo zazzaƙara muryar ta tace

"wait don't sit, get out from here, bana buƙatar wani a falon zan gana da shi"

Wata irin Ajiyar zuciya Ramlah tayi ta ɗan jinjina kai ba tare da ta waigo ba ta miƙe ta fita ta bar falon itama.

Madarar ta ɗauka ta zuba a cup tana sha, tana kaɗa ƙafa kaman tama manta da Yusuf a gurin.

Alhaji Nasir ya kalle ta yace "gimbiyar Daddy bari inje in ɗan watsa ruwa zan fita anjima, yadda kuka yi dashi kya gayamin in na dawo, in yayi miki.

Ɗan ɗaga girar ta ɗaya tayi ta lumshe ido ba tare da tace komai ba.

Bayan tafiyar mahaifinta haka suka ci gaba da zaman kurame ita da Yusuf

Can ba zato ba tsammani yaji tace

"what's the level of your Education?"

Yusuf ya ɗanyi jim sannan yace "secondary school" yai maganar ƙirjinsa na bugawa

Shiru ta kuma yi tana kallon tv seda aka kuma jan wani lokacin sannan ta kuma cewa
"Meye sana'arka?"
Gumi ne ya fara tsatstsafo masa dukda sanyin AC da yake ɗakin, Yusuf baya son kuma yin ƙarya, Amma yace

"Eh ina ɗan zuwa kasuwa ne ina yaron shago"

Cikin Tsara magana da take daki daki, da muryarta me sanyi tace

"Anyway naga kaman za kayi hankali, zan iya yadda ka zama direba na amma ina da sharuɗai"
Ta ɗanyi shiru kaman ba zata kuma magana ba, sannan ta ɗora

"bana son ƙarya, duk ranar da na gano kayi min ƙarya zaka fuskanci hukunci me tsauri, bana son sa ido da shishigi a cikin lamurana, bana yafewa maƙaryaci ko wanda yaci amana ta, babu ruwan ka da irin mutanen da nake hulɗa dasu, bana yadda da mutum kowaye ni kaina wani lokacin bana yadda da kaina balle wani, dan haka duk lokacin da kayi motsin da ban yadda da shi bama zan iya sawa a kulle ka, ban yadda da saɓa lokaci ko Alƙawari ba, sannan lokacin dana ɗauke ka aiki mallaki na ne bana ka ba, ibada kaɗai kake da 'yancin yi, bayan wannan baka da hurumin yin wani aiki idan ba nawa ba, se dai idan ni na baka dama, in ka amince da sharuɗai na" ta ajiye wata takadda

"kayi signing anan, salary 200k and your hard work determines your salary promotions"

Shiruu Yusuf yayi yana tunani, gaba ɗaya ya rasa abun yi
Yusuf yace
"ranki ya daɗe ko zaki iya bani dama inje inyi shawara"

"I don't gives second chance, and I don't want too much waste of time" ta bashi amsa tana maida hankalinta kan talabijin

Shiru Yusuf ya kuma yi ya ɗauki takardar yana jujjuya ta ba tare da ya karanta meye a jiki ba, gumi se karyo masa yake ya ciro biro a Aljihun sa, hannun sa na rawa ze sa hannu yaji tace

"that means you accept the terms and conditions i have mentioned?"

Jinjina kai yayi alamar yana ƙoƙarin ya saka hannu tace

"if you are here to spy don't sign this paper"

(idan kazo nan ne dan leƙen Asiri kar kasa hannu a takardar nan)

Ras! Gaban Yusuf ya faɗi, Anya babu wata a ƙasa, yarinyar nan bata san komai ba? Cikin ƙwarewar Aikin sa ya dake yace

"ranki ya daɗe menene Spy kuma?"

Banza tayi masa ba tace komai ba.

Seda Yusuf yayi Addu'a a zuciyar sa sannaan yasa hannu akan takardar.

Ta sa hannu ta ɗauki takardar ta jujjuya ta sannan tace

"signing this paper is like signing on your death contract!!! Jeka sena neme ka"

Tana gama faɗin haka ta miƙe ta bar falon

Ras! Ras!! Ras!!! Gaban Yusuf ya faɗi
A fili yace "My death Contract kuma?"!!!

Ayshercool
07063065680

Continuer la Lecture

Vous Aimerez Aussi

142K 3.3K 59
imagines as taylor swift as your mom and travis kelce as your dad
27.8K 1.6K 31
labari akan wata yarinya me rawar kai da rashin jin magana sam, labari akan taɓarɓarewar zumunci, tarbiyya da rayuwar 'ya mace idan ta rasa me jiɓant...
296K 23.7K 148
Hannu da yawa...... 🤝🏻🤝🏻🤝🏻
249K 7.9K 177
What if a Pokémon Trainer found herself in the world of One Piece? What if she found herself with the Strawhat Pirates? What if she finds herself get...