★★★★★

            Bayan sallar magriba ina zaune a saman abin salla ina azkar aka turo ƙofar ɗakina aka shigo, kaina na ɗaga ina kallonsa, yanda fuskarsa ke a tamke saida naji gabana ya faɗi, amma sai na dake abina nace, “Yah Qaseem ka dawo?”. Baice dani uffanba sai wata uwar harara daya makamin, ɗauke idona nai tamkar ban ganiba,  ya ida shigowa cikin ɗakin yana bin ko ina da kallo, bakin gado ya ƙarasa ya zauna, hakan sai ya sakani jin wani iri, dan kuwa ni kaɗaice a gidan, koda na dawo ban iske kowa ba, su mom basu dawo daga gidan rasuwaba. A daƙile yace, “Waye ya maidoki gida?”.
       Kaina tsaye nace, “Ummie ce, na jiraka naga baka fitoba gashi magrib ya gabato, sai kawai na biyota”.
        Shiru yay tamkar bazaice komaiba, sai numfashi yake saukewa da sauri-sauri, hakan yasani tsira masa ido, “Yayah lafiya kuwa?”.
         Wata harara ya sake danƙaramin kamar idonsa zai faɗo ƙasa, “Uwar miye haɗinki da shi Jawaad ɗin? Da har zaku  fita tare? Ban miki Warning akansa ba?”.
        Zamana na gyara sosai akan abin sallar saboda jin ƙafata ta fara yami, duk da na lura bawai maganar wasa yakeminba inata ƙoƙarin dakewa.
       Bansan yanda zan bashi amsa ya fahimtaba, amma ni banajin kuskure nayi tunda akan aikine ai. “Dake nake magana Bilkisu!!”. Saurin kallonsa nayi danjin yanda yay maganar a kausashe, nace, “Aiki muka fita fa”.
       “Aiki? Duk jami'an dake cikin Station ɗin babu wanda zai ɗauka suje aiki sai ke?”.
         “Yayah ni wlhy ban saniba”.
Saida yasake watsamin harara dayin ƙwafa sannan yace, “Su kuma waɗannan kayan na jikinkifa da nagani ɗazun? Ina kayan da kika fita dasu daga gida da safe?”.
     Kaina tsaye nace, “A wajen aiki da muka fita ne a mistake jikinmu ya ɓaci, to shinefa sai... Sai... Sa.........”
      “Sai ubanmi? Bilkisu!!”.
“Sai Rose ta bani wasu kayan na zanja”.
       “Harda ita kuka fita?” yay maganar cikin kakkafeni da idanu. “Eh” na bashi amsa cike da ƙwarin gwiwa.
        Karon farko da yaymin murmushi, ya sakko daga saman gadon ya zauna kusa da ni sosai ya tanƙwashe ƙafafunsa (Dan zuciyarsa tayi sanyi jin basu kaɗai bane, amma hakan ba yana nufin zaiƙi saka musu ido bane ba). Yanda muka samu kusancine ya sakani matsawa baya kaɗan, baice komaiba, saima hannuna daya kamo cikin nashi, nai ƙoƙarin amshewa amma sai ya hanani damar yin hakan, murya a sanyaye yace, “Bilkisu!”.
        Amsawa nai idona na kawo ƙwalla, dan banason kama hannuna da yayi......
       “Kinsan kuwa yanda nake sonki da kishin ganin wani ya raɓeki?”. Shiru nai bance komaiba, shima bai jira amsata ba ya cigaba da faɗin, “Daga yau karna sake ganinki da Jawaad, idan kuma ba hakaba to lallai zan saɓa miki kuwa! Domin koba aurenki zanba yayankine ni, dolene na saka miki ido gudun karki lalace”.
     Yanda ya ƙare maganar sai yaban dariya, a raina nace, ‘Kaima ka samu dama ai lalatanin zakai’, amma a fili sai, nace, “Yayah nifa banice naje wajensaba, bayan na fito daga kiran da akai minne mukai karo dashi a hanya, shi kuma ya fito daga office ɗinsa, shine yace na biyosa, da farko ma bansan dani yake ba sai da ya sake aikowa sannan, amma dan ALLAH kayi haƙuri”.
     Murmushi yay min yana jinjina kai, yace, “Nasan dama ba laifinki bane, amma zan takama al'amarin birki tunkan yay nisa kinji, ina sonkine da yawa shiyyasa bazan juri ganinki da waniba ballema maƙiyina Bilkisu...”
     Ya ƙare maganar a hankali yana matsowa jikina sosai, gabana ne ya shiga faɗuwa, nai ƙoƙarin ja da baya amma sai hakan ya gagara saboda riƙon da yaymin bana wasa bane, sannan ƙarfina da nasa ba ɗaya bane, matsananciyar rawa jikina na fara sabida ƙoƙarin kawo fuskarsa kan tawa da yake, na shiga girgiza masa kai ina hawaye, roƙonsa nakeson yi, bakina sai motsawa yake amma na kasa furta komai, ya riƙe kaina da ƙyau yana ƙoƙarin ɗora bakinsa kan nawa na ƙwalla ƙara.
      Da sauri ya sakeni shima yaja baya saboda tsorata da ƙarata, jikina sai ɓari yake na tashi a guje na shige toilet ɗina na banko ƙofar harda murza key. ‘innalillahi wa inna ilaihirraji'un’ naketa ambata, wace irin masiface kuma wannan ni Bilkisu, kuka na shiga rusawa a bayin sosai, duk da inajin ƙwanƙwasa ƙofar da yaketa famanyi yana kiran sunana da bani haƙuri banko tankashiba, kusan mintuna talatin naji shiru alamar yabar wajen, ban buɗe ƙofarba har sannan sai bayan wani lokacin sannan na buɗe kaɗan na leƙa, babu kowa a ɗakin saima ƙofa dana gani buɗe alamar ya fita, komawa nai toilet ɗin na ɗauro alwala na fito, sai da na sakama ƙofar key kafin na tada sallar isha'i.
         Haka nai kwanciyata da yunwa ban fitaba duk da inajin motsin su mom da suka dawo kusan ƙarfe goma, ina idar da sallar asuba nai shirin barin gidan, dan gwarama na shiga gidansu Amina daga baya sai na wuce wajen aikin, bazanbi yah Qaseem ba. Sauri-sauri na kammala na fito, gabana ya faɗi ganinsa zaune a falo yana shan shayi alamar dai shima harya gama shirinsa, yanda ya tsatstsareni da idanu kuma ya sakani tsayawa cak nai ƙasa da kaina, “Kizo kisha shayi mu wuce, dan sauri nake yau”.
     Bance dashi komaiba na wuce zuwa kicin, kaɗan na haɗa tea a kofi na zauna a kicin ɗin ina sha, dan kuku ma bai kai ga fitowaba, saurin kallon ƙofar nai jin an shigo, nai masa kallo ɗaya na ɗauke kaina gefe, baice komaiba nima banceba, sai ajiye kofin da nai na nufi ƙofa, matsawa yay ya bani hanya, a ɗarare na raɓashi na fita yabi bayana.
      Badan raina yaso ba na shigar motar Yah Qaseem yau ɗinnan, shiru motar babu mai cewa komai ni da shi, ko redio bai kunnaba, tuƙi yake a hankali kamar bayaso, mun ɗanyi nisa da gida ina lafe a jikin kujera da karanto addu'ar neman tsarin ALLAH daga shaiɗanin dake ingiza zuciyar yah Qaseem ga abinda bai daceba gareni naji motar kamar ta tsaya, idanuna dake cike da barci na buɗe, naɗan waigo na kalleshi, ganin ni yake kallo sai na janye idanuna ina sake gyara zama, wlhy bazan ɓoye mukuba a tsorace nake, bani da ƙarfin dazan kare kaina ga murɗaɗɗan namiji irin yah Qaseem koda ace yay shirin cutar da nine, cikin dauriyar dole nace, “Yah Qaseem lafiya muka tsaya?”.
      Ajiyar zuciya ya sauke a hankali, har lokacin inajin idanunsa na yawo a kaina, sai dai baice komaiba, kusan mintuna biyu suka sake shuɗewa, a bazata na tsinkayi muryarsa, yace, “Kiyi haƙuri Bilkisu akan abinda ya faru jiya, banyi hakan da niyyaba tunda kinsha faɗamin baƙyaso”.
      Ajiyar zuciya na sauke inajin daɗin kalamansa, na share hawayen da suka zubomin, ba tare dana kallesa ba nace, “Na haƙura Yah Qaseem, amma dan ALLAH ka rufamin asiri, kaji tausayin maraicina ka barni da mutuncina, gidanku itace mafakata ta ƙarshe da nake alfahari da ita, idan shaiɗan ya lulluɓe maka ido ka tuzguɗemin ita bansan ina zan dosaba, haramunne a addininmu, sannan cutarwace a garemu, wannan ba shi bane soyayya kamar yanda yake a tunanin yahudu da nasara, ƙoface kawai ta saɓon UBANGIJI, kuma tushen fasiƙanci, daga kama hannuna da kakeson yi a koda yaushe matsala zata fara, tun inaji banason hakan wataran sai kaga shaiɗan ya ƙawatamin nafara jin daɗi, a tafi matakin sumbata, makulin buɗema shaiɗan ƙofa kenan da komai na baɗala zai iya wanzuwa tsakanin namiji da mace, duk takatsantsan ɗinmu wataran kafin mu farga sai akai ga aikata zina, ‘Wa'iyazubillah’. Yah Qaseem namiji da mace duk hukunci ɗaya garesu wajen ALLAH idan suka aikata zina, amma a zahirance ta rayuwar duniya mace itace ke fara ƙasƙanta a idanun al'umma makusantanta dama na nesa da ita, domin itace ke ɗaukar ciki, itace wasu almomi ke fara bayyana a gareta, farko rasa mutunci, ƙasƙanta mutincin gidansu dama ahalinta, tabon da zaita bibiyar rayuwarta har ƙarshen zuri'arta, ita ake fara aibantawa kafin abokin tarayyarta, itace ke rasa mijin aure, ita akafi nunama ƙyama, itace keda rauni. Abin tausayi da tashin hankali ƴa mace na fuskantar waɗanan matsalolin koda ace fyaɗe akai mata. Yah Qaseem indai sona kace da gaske dan ALLAH ka daina min waɗanan abubuwan, wlhy banaso, basa burgeni......”
          Qaseem yaja wani bahagon numfashi saboda tausayi da bily ta bashi, harga ALLAH sonta yake da gaskiya ba yaudaraba, ALLAH ne ya jarabcesa da sonta batare daya shiryama hakanba, yanda take kuka sai ya kumajin tausayinta sosai a ransa, murya a sanyaye yace, “Na fahimceki Bilkisu, insha ALLAH kuma zan kiyaye, idan kin amince zanma Dad magana akan aurenmu”.
      Sauran hawayena na share tare da kallonsa, ganin ni yake kallo sai na ɗaga masa kai alamar na amince. Ya saki wani murmushi najin daɗi yana sake tsatstsareni da idanunsa farare tas, a hankali ya furta, “Inasonki da yawa Bilkisu na, gara dai nayi na mallakeki kusa dani na huta da wa'azinnan”. Murmushi nayi ina ɓoye fuskata, shima yay ƙaramar dariya yana mai tada motar muka cigaba da tafiya. Hira yaytamin har muka ƙarisa station ɗinmu duk da ba amsa nake bashiba sai dai eh ko a'a da murmushi kuma.

BAYAN KWANA UKU.

       A kwanaki ukunnan Boss bai sake shiga harkataba, harna ɗauka gargaɗin Yah Qaseem ne yasa ya barni, tunda ina ganin dai yana sama dashi. Shima a ɓangaren Yah Qaseem na samu sauƙin yawan kai hannunsa jikina da yakeyi, sai dai wasu take-taken Yah Salman a gidan yanzu suke cazamin kai, ya masifar samin idanu, kowane motsina sai ya tanka magana a kai, Aunty Shahudah cema naga dai tayi sanyi, bansan mike damuntaba, amma saina lura kamar bata cikin nutsuwarta. 
      Ban sake cema baba maigadi komaiba game da zancen Amina saboda saka idon Yah Salman a kaina, amma inata wasu shirye-shirye a gefe nabin matakan da zan gano bakin zaren, dan abinda baba mai gadi yayi ranar yana nan tsaye cak a zuciyata bai gogeba. Da wannan tunaninma yau na fita wajen aiki.
     
          Tunda muka dawo sallar zuhur muna a office ɗinmu da boss ya dunƙulemu, kowa yana hidimar aikin daya dace, yayinda Ni da Ummie muna aikine muna ƴar hirarmu data shafemu, hakama sauran kowa nayi da abokin maganarsa, hakanne yasa ɗakin ɗaukar kananun surutai sama-sama. A bazata naji office ɗin ya ɗauki shiru tamkar ruwa ya cinye kowa, batare dana ɗagoba nai ƙaramar dariya ina faɗin, “Ummie mutuwace ta gitta a office ɗin namu ne?”.
      Shiru naji Ummie batace komaiba, hakanne ya sani ɗagowa a tunanina batajini ba.
            ‘kutumelecy’...............✍

Assalamu alaikum.

      Inason naɗanyi bayani da nake fatan a fahimceni, akan maganar aikinsu Jawaad, inason mai karatu ya fahimci wani abu anan, aikin da muka dangantasu dashi bawai yana nufin ainahin abinda ya shafi ma'aikatan zahirin bane, bamusan komai da ya shafesu ba, tayaya zamuce komai nasu sai ya shigo labarinmu, domin ba'akan hakan muke rubutu ba, da yawanmu ma idan za'a tambayemu bazamuce munsan waɗanan ma'aikatanba kai tsaye, domin su aikinsu bawai a bayyane yakeba kamar ƴan-sanda da dai sauransu da suke cikinmu ba, aikine na wanda kai kanka idan ba wani daliliba bazaka taɓa ka gansu suna yawo gama gari ba ko wani aikinsu a bayyane, so na danganta waɗanan jaruman littafine da hakan saboda mutunci da himma da ƙwazo na irin jami'anmu da mu kanmu bamu saniba, matasanmu kuma su zama masu himma dason bama ƙasarsu gudunmawa da zuciya ɗaya a kowace ƙasa suke ba lallai sai tamu ba, tom inaso ku kalli wannan kawai a matsayin labari bawai lallai abinda yake a zahiri ba, ko yake lallai mu bibiya, matsayinsu, misukeyi? Mizasuyi? Duk iyakarsa labari irin na marubuci {ƙirƙira}, bani da hurumin shiga abinda bani da lasisi a kai, domin bamma sani ba, waɗanan jami'an littafine bawai na zahiri dake aiki a ƙasarmu ba, idan kun kula sam babu wani sunan gari dake nunama a ina suke, ko a wane waje suke, musa a ranmu kawai ƙirƙirarren labari muke karantawa, ilimantarwa, nishaɗi, da faɗakarwa, ba akan kowaba, domin ba'akan kowan mukeyi ba, duk abinda zamu iya ganin yaci karo da waccan rayuwar ta zahiri to kawai fiƙira ce irin ta marubuci bawai dan inada ilimin sani ba ko bibiya balle bincika, ina fatan duk wanda ke bibiyar wannan littafi a ko'ina yake zai kasance maiyin ƙyaƙyƙyawan fahimta akan inda muka dosa, sannan abinda kake ganin na karkace ko shiga hurumin da banawaba ina fatan zakuyi gaggawar dawo dani hanya, ALLAH yasa mu dace, ALLAH kuma ya ƙarama dukkan jami'an tsaronmu lafiya da ƙwazo da nagarta a duk duniyar da suke.🙏🏻


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻

     
 

ƘWAI cikin ƘAYA!!Where stories live. Discover now