“Umma sai ta dinga ganin laifina, suma mutane idan baka haukace musu ba, ba zasu shafa maka lafiya ba, amman ita bata ganewa, kuma ita ma fa tana da masifar nan, kenan nima ai gado nai”

Tana ta mita har ta isa Islamiyar, sannan ta fara boye boye ganin ana dukan yan latti.

“Kai na fa girma yanzu, jami'a na ke, sai kuma na dinga tsoron bulala no way”

Ta fito kai tsaye ta nufi cikin makarantar inda ake dukan dalibai, malamai biyu ne tsaye a gurin dayan ta sanshi shi yake karantar da su a ajinsu, dayan kuma mutumen da ta ganine dazun da safe yana exercise. Bata bi bayan wadanda ake ma bulalar lattinba ta biyo ta gefe zata wuce ta cikin gate din makarantar, idonta na kansa shi ma ita yake kallo hannunsa rike da bulala, tana daf da wuce shi ya fisgota ta dawo baya.

“Ke kika fi kowa ne? Ba ga sauran nan ba ana dukan yan latti”

“Ina ruwanka”

Bulalar da ke hannunsa ya doka mata, sai da tai tsale, ta bude baki ta sake wata maganar ya sake shauda mata wata, da gudu ta koma inda ta fito tana hararashi.

“Bakin mugu azzalumi, ji mutumen nan daga kawo shi yau yau har ya fara dukan mutane, daman daga ganinsa bakin hanya na san bashi da mutumci. Hmmm kut baka san wace Zinneera ba Wallahi”

Kasa kasa take maganar, ta yadda ita kadai zata ji, shi dai baya jin abunda take fada ya dai hango bakinta na motsi, murmushi yake a zuciyarsa daman he just want to see her sad face, tsiwarta na burgeshi, ko ba komai yasan za su kulla takun saka a tsakaninsu.
   Haka ta biyo hanyar dawowa gida, itakam da a mata bulalar latti kara bata je ba, idan ka hadu da ita a hanya tana tafiya sai ka dauka natsatsar yarinya, domin kanta a kasa yake tafiyarta ma a kuntse kamar mai natsuwa. Umma na ganinta tasan za ayi dayan biyu ko dai tayi latti ko kuma ta canja shawarar zuwa makarantar ne, domin ta saba haka.

“Au dowowa kika yi?”

“Umma to na yi latti kuma an kawo wani shegen malami sabo daga fara zuwa sai dukana yake”

“Idan ba ki yi abun duka ba zai dakeki ne? Ke dai kam Allah ya shirya ki, duk yarinyar da ke da shekara goma sha bakwai ta san ciwon kanta, zaka tana abu kamar sauran mutane amman ban da ke, kinji haushi kikam”

Bata ce komai ba, ta jingina jikin kofar tana wasa da hannun jakar da ke ratayi a kafadarta. Ji take kamar da ta kai tsakar gidan Umma rufeta zata yi da duka.

“Umma yunwa na ke ji”

“In kin ga dama sai kije ki dauki abincin ki ci”

Da sanda ta wuce dakin dafa abinci ta dauki abincin ta fito ta shige dakinsu.

Be tashi daga makarantar ba, sai shida yau shine zuwansa na biyu a makarantar tun da ya dawo yai requesting yana son ya rika karantar a nan ganin ita ce kusa da shi, domin ya saba a can ma yana karantar a masallaci, tun a ranar suka amince amman ba fara zuwa ba sai jiya da yau. Daga makarantar family house ya wuce daman Abbah ya kirashi tun da ruwan saman suka dauke ya sanar masa cewar yana nemansa akwai inda za su je da magariba.
  Sai da yai sallah a masallacin da ke unguwar Lodge road sannan ya shiga gidansu, as usual falon Momy ya fara wucewa, yana shiga sanyin ac da kamshi mai dadi suka yi welcoming dinsa. Babu kowa falon sai tv dake ta aikinsa.
Saman sofa ya zauna ya kai hannu ya dauki hot tea da ke cikin mug ya kai bakinsa yana murmushi kama ganinsa kasan hankalinsa yana wani gurin ne.

“Miya saka murmushi haka”

Ya dago ya kalli Momy wacce ta fito daga bedroom sanye da farar atamfa, hannunta rike da da gilashinta.

“Evening Mom”

“Evening favorite, tell me what the secret?”

Ta fada bayan ta zauna. Sai ya fadada murmushinsa.

“You know i won't lie, actually wata yarinya na daka a makaranta hakan ya sani farinciki”

“What how?”

“The story is like this, ina son fushinta, tana da wauta ga ban dariya, ga jan magana, ga fada, ga rawa ga karatu ga waka ta iya yi akwai tsiwa, Mom everything about is perfect, dazun ta tare ni tana min tsiwa wai na wuce ta kamar zan takata saboda ina exercise, 0-1 kenan yanzu kuma ta yi latti a islamiya na zaneta kin ga 1-1 kenan, and i know dole zata yi wani abu dan ta rama”

“Wow what a super story you have ever told, so tell me did she know you have crush on her”

“What, no Mom she's under 20, and we are... I don't even know her name”

“Really, a ina take?”

“A nan unguwar ta ke”

Momy ta yi murmushi.

“I don't care if she's from a rice family or poor, all i care is my favorite has crush on her...”

“No Mom... You got me wrong”

“Everyone can got you wrong except your own Sweet Mother, i know who's my son. So kaje ciki Daddy ka yana son ganinka zaku je gaishe da Gwaggonka, idan kun dawo zamu yi magana da kai”

“Ba zan dawo ta nan ba”

“Fine”

Ta fada tana daga kafadunta fuskarta da murmushi. Sai ya mike tsaye yana fadin.

“Mom baki fahimta ba, i... I... O.. ”

A haka maganar ta makale ta ki fito har ya fice daga falon. Momy ta bishi da kallo tana murmushi.

“Dawowarka ta yi rana kenan, Favorite you can't deny it”

Gilashin da ke hannunta ta saka a idonta ta matsa ta dauki mug din da ya aje ta soma sha...

COMMENT SHARE.

ZABIN RAIWhere stories live. Discover now