BROKEN

810 50 1
                                    

SANADI NE

KHAIRAT UP

F.O.W

   Vote@wattpad khairi_muhd

          39_40

Asibitin standard aka nufa da ita cikin gaggawa aka amshe ta aka shiga dubata.

nan likita ya fito da wata takarda ya ce dasu

  _tana da aure ne?_

nan umma ta ce eh

_ana bukatar sa hannun sa dan ko she is critical ta zubda jini da yawa se an mata aiki maybe a samu chances na saving din ita da abun cikin ta saboda ta fadi sossai a kai it can be fatal._

umma da hajja da mummy aka soma kallan kallo mummy tace dama tana da ciki ne?

_dr ya katse su bamu da lokacin batawa kuyi sauri_

nan abbie ya shigo tare da mubarak da umar ya tambayi me ake ciki? nan suka fada masa yace to umar sa hannu tunda shi makyn din be karaso ba umar yasa hannu dr ya shiga ya koma aikin cetan rayuka biyu.

hajia amina da faisal a tare suka zo duk ta rude ta kasa samun nutsuwa.

me ya same ta ?

umma ta ce hajia ki kwantar da hankalin ki zata warke addu'an ku take nema kawai.

to me ya same ta wai? lafiya muka rabu da ita fa.

nan mummy ta fada mata ayko ta shiga tashin hankali da matukar kad'uwa kennan lokaci yayi?

  ina makyn?

ta dago a razane idananun ta sun rine sun koma ja dan tashin hankali ranar tasan cewa hawaye ma rahama ne. bata shiga tashin hankali ba saida abbie ya mata wannan tambayar " _ina makyn!_".

dirshan ta zauna kan kujera tana muzurai.

amina wai me haka ina tambayar ki kin mun shiru me yake faruwa ne? .

faisal ne ya ce am abbie ya makyn baya nan yayi tafiya ne an tura sa ayki ya shararo karya.

to hakan da zata fada shi ne take mun muzurai?

ayi hakuri abbie tana cikin damuwa.

   sanda dr ya fito yana share zufa suka tare shi da tambayar yaya? nan yace dasu su kwantar da hankalin su cikin ikon Allah anyi nasarar ceto ran uwar da dan kuma ana mata karin jini ne yanzu kuma tana bacci in ta farka zasu iya ganin ta.

hamdala suka yi hade da godewa Allah kowa ka gani ran sa fes ne banda mutum daya mummy ta ce na shiga uku na dama mutuwa tayi kowa ya huta yanzu me zata yi?

kafin yamma en gidan suka karaso ana kiran magrib ta farka dr ya kuma duba ta da kyau ya sa aka bata tea ya bada magani duk da tsamin jikin ta yake mata hakan be hana ta jin zirarowar hawaye daga kuncin ta ba hawayen dana sani, hawayen wautar ta, hawayen bakin ciki, hawayen da bashi da amfanni.

sanda dangin ta suka shigo se taji wani sabon hawaye ya balle mata duk zaton su na ciwo ne

basu san ba haka bane.
hawaye kawai ke fita daga idanuwan ta su ko banda sannu ba abunda suke mata suna lallaba ta.

mummy kam idanuwan nan sun firfito waje tana muzurai a matukar zabure take tamkar wadda za a ce kyat ta fyalla 😂 dan tasan karan ta da hajja bazai kyau ba, balle uban en gayyar mijin ta da kyar ta hadiyi wani yawu me daci ji kake makwat 😂.

likita ne ya shigo ya umarce su da su fita su bawa mara lafiya wuri tana bukatar hutu. allurai ya kuma mata bacci ya dauke ta.

❣❣❣❣❣❣

jamfa ce a jikin sa da hula se faman bad'a kamshi yake tsakiyan mutane yake suna meeting gaban sa yaji ya fadi ya kasa nutsuwa shi yake bada presentation din amma haka ya dakata ya bada excuse cewa be da lafiya he is sick hakan yasa mannir karasawa ya fita daga cabin din.

kan wata kujera ya je ya zauna ya maida kan sa jikin bangon kujerar idanun sa na fitar da hawayen da be san mesa ba gaban sa na ta faduwa gida ya tuna wayar sa ya zaro ya zuba number's din hajia sedai tana ringing sau daya ya katse kiran hade da runtse idanuwan sa yana tunanin anya ko ya ma kan sa adalci kuwa? ya ma hajia adalci kuwa? yasan yanzu duk inda take ta damu da ta gansa uwa fa ba abar wasa ba ce amma shin ta sauko, ta hakura? be da amsa.hannayen sa ya daga sama _*YA ALLAH KASA DUK SUNA LAFIYA , YA ALLAH KA BAYYANA GASKIYA NA KOMA CIKIN EN UWANA ,YA ALLAH KA TONA ASIRIN WANDA YAKE SAN RABA NI DA MATA TA, YA ALLAH KASA MATATA TA SO NI MUYI RAYUWA ME DADI KAMAR KOWA!* ya shafa hade da cewa ameen.

    duk yadda hajia ta so samun makyn kasawa tayi hakan ya kuma daga hankalin ta tana tambayar kanta anya bata da laifi kuwa?.

su ko su nas basu san me yake faruwa ba duk da sun ga alamun cewa akwai damuwa a tattare da hajia da faisal da ita kan ta rabi ga kuma rashin ganin makyn wanda khadyjat ta kira sa yafi a kirga bata samun sa to wai meke faruwa?.

muje zuwa

  SANADI NEWhere stories live. Discover now