...29...

577 15 1
                                    

*SANADIN CACA*

Mallakar SADI-SAKHNA

PROFICIENT WRITER ASSOCIATION

*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[29]

[Sumaimah a mahangar gani]

Tun lokacin da Goje ya fita har dare yafara kafin ya dawo,ina kwance akan gadona na ɗakin inna najiyo muryarsa yana ƙirana.
Shuru na ɗanyi saida inna tace
"Sumaimah ba ƙiranki yake bane?"
"Uhmm eh"
Kaina a sunkuye naje bakin kofar ɗakin,saidai ban ganshi ba da alama ya yi ƙofarsa.
Dan haka hijabina na saka akan doguwar rigar jikina na nufi ƙofar tasa.
Ɗakin a bude yake amma baya ciki,da alama yana bandaki,dan haka zama nayi akan katifa ina jiransa.
Ganin yaɗan daɗe yasa nayi tunanin inaga wanka yakeyi,hakanne kuwa dan shigowa yayi dagashi sai gajeran wando.
Bai min magana ba ya fara shafa mai,nima bance masa komai ba ina nan zaune. Sai bayan yagama kafin yazo inda nake ya zauna,kallona yake kaman mai nazari yakasa cewa komai.
Duk da cewar babu wani wadataccen haske iya na wayarsa ne daya kunna amma ina ganin fuskarsa.
"Meyasa baki bude wannan abunba da kikaga ina wanka?"
Saida yayi magana na kulada ledar da take tsakar ɗakin,sakkowa nayi na buɗe,tsirene a cikin yaki albasa.
"Lahh ban gani bane shiyasa"
"Uhm toki ɗibama inna kema kuma in zaki ji sai......."
"Wai anya kuwa inna zataji yanzu,dan yanzu muka gama cin abinci,nima kuma gaskiya ba lallai ba,amma barina tafi dashi koh?"
Nafada inason barin ɗakin,danna kula babu wani abu dayake buƙata,kawai ƙirana yayi,sannan yasamu sauƙi sosai bare yace da wani abun zan taimaka masa.
"Ahah tunda kun ƙoshi shikenan ajiyeshi kawai sai kuci da safe"
Na ajiyeshi,ba tafiya zanyi ba sai na tafi dashi kawai ai.
"Uhm naga nima tafiya zanyi to...."
Dariya yayi min tareda cewa.
"Ki tafi inaaa,aikin dawo ɗakin mijinki kekam,daga yau ban yadda ki dunga kwana a ɗakin inna ba,nan ne ɗakinki"
Dumm gabana ya buga,ban taba tunanin hakan nan kusa ba.
Hannuna ya zawo ya zaunar dani a gefensa,wanda hakan yasakani ajiye ledar da take hannunnawa. Kallona yake cikeda sigar damuwa da neman taimako wanda bansan na menene ba.
Hannayennawa yahaɗa dukka biyun a cikinnasa,tareda tattaro dukkan wani sauran nutsuwarsa,nima ganin hakan yasa na kafeshi da ido.
"Sumaimah nine na koreki da ɗakinnan a zuwanki na farko,a yau kuma na buɗe baki ina rokon daki zauna a cikinsa,ko kaɗan bawai tilastaki zanyi ki zauna dani ba,illah iyaka ina son hakan. Kiyi haƙuri da abubuwan dasuka faru a baya waɗanda nayi miki,bazan ce ki manta dasu ba,amma please kada ki ƙullaceni akansu. Dan Allah ki zauna dani ƙarƙashin inuwa ɗaya,idan kin amince dani kaman yadda kika faɗa,ki bani damar shiga a rayuwarki a yau ɗin,idan kinga kuma abin yayi miki sauri ki faɗamin zan barki kiyi nazari akai"
Bayan yagama maganar shuru yayi domin yaji mai zance,ganin nayi shuru yasa ya murza hannaye na.
Ajiyar zuciya na saki tareda cewa.
"Ba....bansan mai zance ba takamaimai akan wannan maganar,abinda ya faru da baya ya riga ya wuce wanda dama hakan ake fata a manta dashi. Batun nadawo kwana ɗakinnan kuma idan hakan ka buƙata to dole shi zanyi,saboda gidanka ne kuma ikonka ne,inda kaga dama ka sakani matuƙar bawai cutarwace ta shigaba dole anan zan zauna.
Sannan kana alaƙar aure kuma haƙƙinka ne daman,kaine da baka biɗa ba tunda. Zan iya hanaka idan da a bayane baka ciyardani ba baka tufatar dani ba. Amma a yanzu idan nace baka ɗaya daga cikinsu nayi ƙarya,dan kayimin wanda ban tsammata bama. Dan haka ka buƙaci samun nutsuwa dani na hanaka saboda wai kayimin ba daidai ba a baya bai tasoba"
"Hmmm naji daɗin bayananki,sannan ina jin daɗi a duk lokacin dakika faɗomin matsayin da nake dashi a wajenki,amma a yanzu ra'ayinki na buƙata ba wai matsayina ba,na yanke shawarar son fara rayuwa dake,sannan banason batun musgunawa ko cutarwa yashigo ciki. Shin kina ji a ranki nayi cancantar da zaki iya miƙamin amanar kanki?"
Wannan tambaya ta taba zuciyata sosai,ni wacece da bazan amince ba. Zare hannuna nayi daga cikin nasa tareda saqalasu ta bayan wuyansa,kuka na fara na farinciki,ganin lokaci guda kaman almara Allah ya karkato da hankalinsa gareni,ya kasance namiji mai nutsuwa da ban taba tunani zai zama,idan wani yace a lokacin baya zan kasance a tsakanin kafaɗun goje to zan iya rantsewa ƙarya yake. Amma yanzu sai nake ganinsa kamar yafi sauran mazan garin ma sauƙin kai.
Hannunsa naji yasaka yana bubbuga bayana,mun dan ja lokaci a haka kafin nazare hannayennawa,a yanzu kuma ina kan cinyarsa a zaune.
Naso kafin na bashi kaina kona shirya yin mu'amala ta aure dashi sai yaƙara nutsuwa da kuma sanin addini sosai,amma tunda ya buƙata ɗin zan amince masa,wataƙila hakan yaƙara tasiri wajen gyaruwar tasa.
Ina cikin tunanin naji bakinsa akan nawa,bansan lokacin daya iso kusa har haka ba.
Kwantarni yayi akan katifar a hankali,tareda ƙoƙarin maidani cikin sahun jerin matan aure masu albarka. Lokacin danaji mai afkuwa tana shirin afkuwa saurin buɗe bakina nayi tareda karanto Addu'ar da ma'aiki muhammad (SAW)ya umarcemu dayi,dan nasan gogan koda ya iyata ma bata ita yake ba a lokacin,abune dama da bai dameshi ba yanzu ake ƙoƙarin ganar dashi.
Nasha wahala ba kaɗan ba a wajensa,duk da cewar yayi iya ƙoƙarinsa wajen ganin bai min ta ƙarfi ba,amma halitta ta da tasa ba ɗaya bace.
Bayan komai ya lafah shuru naji yayi lokacin daya gangara ɗaya barin katifar,zato na idonsa biyu,saida naji minsharinsa kafin na jijjiga kai,wato a wannan yanayin najasar shi bacci yayi abinsa.
Tashi nayi da ƙyar ina cije baki na ɗaura zanina,jikina banda tsami babu abinda yakeyi,abinka da ban saba wannan dambarwar ba.
Randarsa na leƙa naga akwai ruwa a ciki,godiya nayi ga Allah kafin na ɗiba na nashiga banɗakinsa domin tsaftace jikina.
Lokacin dana fito har baccinsa yafara nisa,ruwan dayake hannuna na yarfa masa,nayi sa'a kuwa ya juyo yana kallona.
"Ka tashi ka tsaftace jikinka,bai kamata ka kwanta da najasa ba,ina ka iya wankan tsarki ko"
Tashi yayi ya zauna yana kallona,ba fuskata yake kallo ba,dan haka sai na bi inda yakalla,kan kirjina idonsa yake,kasancewar iya zaninne kawai jikina..
Hannuna na saka a wayance na tare saboda kunyar data kamani..
"Uhm badai wannan wankan bane da ake wanke bangare bangare na jiki,na iya shi mana,na kanyi innayi mafarkin wata......wanann kam maza dayawa ai sunayinsa..
Meyasa kike kare jikinki,bayan yanzu naga......."
"Am na bar maka ruwa a banɗaki,wataƙila zai isheka"
Da sauri nayi maganar ina nuna masa ƙofah,dariya yayi tareda dan jan hancina,dan ya kula so nake yabar zancen..
Kafin ya dawo kayana mayar tareda yaye zanin kan gadon naɗauko wani na saka,duk da yanda jikina yake min magiyar zai kwanta.
Ina kwanciya naji alamar shigowarsa ɗakin,yi nayi kaman bacci nake saboda in yayi magana ma bansan mai zance ba..
Ina jinsa ya hawo kan katifar tareda jawoni jikinsa,daga ƙarshema ya ɗora kaina akan kafaɗarsa.
"Saida safe matata,nagode sosai da kyautarki"
Yafaɗa a hankali tareda sumbatar goshina.
Zanyi ƙarya idan nace hakan bayyimin daɗi ba.

SANADIN CACAWhere stories live. Discover now