KAMA DA WANE....(Completed)

By Seemahwrites

13.2K 1.8K 210

even though they look alike that doesn't mean they should have same goals, their life is filled with regret... More

chapter 1
chapter 2
chapter 3
chapter 4
chapter 5
chapter 6
chapter 7
chapter 8
chapter 9
chapter 10
chapter 12
chapter 11
chapter 13
chapter 14
chapter 15
chapter 16
chapter 17
chapter 18
chapter 19
chapter 20
chapter 21
chapter 22
chapter 23
Apology
chapter 24
chapter 25
chapter 26
chapter 27
chapter 28
chapter 29
chapter 30
chapter 31
chapter 32
chapter 33
chapter 34
chapter 35
chapter 36
chapter 37
chapter 38
chapter 39
chapter 40
chapter 41
chapter 42
chapter 43
chapter 44
chapter 45
chapter 47
chapter 48
chapter 49
FINAL
Trailer

chapter 46

201 34 5
By Seemahwrites

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)
🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤
👩🏻KAMA DA WANE......
BATA WANE👩🏻‍🦱
💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

*Na*
*UMMU NAJMA*
marubuciyar *HAR ABADA*

*DEDICATED TO*
*AMMYN KHAIRAT(golden girl)*
*AND RUKAYYA IKRA(ummu sultan)*

Special gift to *Muhammad Karim*
*And Fenarh matar Soja*

46👯
Leqo da kanta tayi ta saita dutsen dai_dai qeyar mutumin, Sannan ta qwala mishi tayi saurin komawa cikin lungun ta buya tana dariya Sa'ood dai kallon ikon Allah kawai yakeyi,

Ihu mutumin ya saka Yana Sosa wurin da Leesa ta jefe shi dan Babu laifi ta qware wajan saiti, Lateefa na ganin abinda ya faru cikin murna ta qwala Kiran sunan "Haleesa!! Kina Ina ne 'yar uwa ki fito dan Allah"

Mutumin dai na tsaye yaga ta Ina Haleesan zata fito yaci ubanta Amman ganin ta tare da Sa'ood yasa yasha jinin jikin shi yayi qwafa kawai ya juya ya tafi, ya saka ma ranshi sai balaraben Nan ya tafi zai dawo ya ci qaniyar ta,

Rugowa da gudu Lateefa tayi ta rungume Haleesa tana dariya, sai Kuma ta sake ta taja da baya kadan tana qare Mata kallo,
"Leesa kece wannan? Innalillahi kin ganki kuwa? Kin dawo Kaman 'yar turawa, mijin Salee ne wannan ko?"

Murmushi Mai sauti tayi ta riqe hannun lateefa tana jijjigawa cikin Jin dadi tace "yayana ne wannan, yayan mijin Salee ne sunan shi ya Sa'ood, shi 'dan yayan mahaifi na ne yanzu nasamu dangi na Lateefa"

Tsalle ta daka ta qanqame Haleesa tana dariyan farin ciki "nayi Muku murna sosai Haleesa Allah ya saka mu a madamacin ku kema shi din Zaki aura?" Ta fada cikin zolaya tana kashe Mata Ido daya,

Rausayar da Kai Leesa tayi ta Ciro IV daga cikin handbag dinta ta miqa Mata "gashi naki katin gayyatar ta musamman, tun sauran sati nake so kije gidan mu ki tare asha hidima tare dake na saka ki a cikin qawaye"

Sake runguman Leesa latifa tayi tana Jin kaman tayi Mata kuka saboda farin ciki Sannan ta dago tacewa Sa'ood dake make a gefe Yana lallatsa wayar shi "sannu angon mu"

Ya saurari hirar su tun daga farko Kuma yaji sannun da Lateefa tayi mishi Amman batayi mishi da ya amsa ba, tun daga Kan shigar ta tasha mini skirt da gashin doki da kuma kwalliyar ta da yayi kaman na shedanun aljanu bai cancanci da ya amsa ba,

Fisge wayar hannun shi Haleesa tayi tana hararar shi, ya dago zaiyi masifa yaga Wanda ke cikin idon ta yafi nashi sai ya sassauta murya "novio please give my phone back I'm doing some official work and it's very important"

Dan saboda kada Lateefa taji sun sauya harce tayi tunanin wani Abu yasa tace "yau ba ranar aiki bane ya Sa'ood, aunty na tana gaidaka baka amsa ba"

Wayancewa yayi yace " ohh yaya kike"

Kan Lateefa a qasa tayi mishi proper gaisuwa sannan taja hannun Leesa suka Shiga gidan shugaba, Sa'ood ya bisu da Ido Wai a wannan gidan magajiyar karuwan qannen shi Sarwa suka tashi, Yana jin Yanda gidan ya dauki ihu da shewa na muryan maza da Mata kowa Yana oyoyo Salee Babu Wanda yayi tunanin Leesa ce saboda Yanda ta sake tana ma kowa da kowa murmushi,

Shugaba na Jin ana Kiran sunan Salee ta fito dan tabbatar ma kanta da gaske yaran da suka yaudare ta suka tsere ne yau suka dawo, kallo tabi Haleesa dashi tun daga sama har qasa sai Kuma ta juya ta koma dakin ta, jiki a sanyaye Haleesa ta buta ciki ta hange ta zaune ta kawar da kanta gefe sai taunar chewing gum takeyi qaras..qararas...,

A qasan kujeran da take zaune Leesa ta zauna, ta gaidata cikin ladabi Dan tana matuqar ganin girman shugaba saboda irin halaccin da tayi musu,

"Na dauka tunda Kun tafi ba Zaku taba dawowa ba, kunyi was da hankali na ke da 'yar uwarki Saleeha Amman Babu damuwa duniya ce daga yanzu Babu yaran da Zan sake taimakawa na rufe qofar taimako a kanku"

"Haleesa ce ba Saleeha ba shugaba, kiyi haquri Dan Allah nasan bamuyi Miki adalci ba bamuyi ma kanmu adalci ba Amman kaddara ta Riga fata ne Babu Yanda muka iya, yanzu Haka Mun samu dangin mu saboda sarqan mu da muka Miki alqawarin zamu baki Mun gano iyayen mu dashi"

Ta Ciro IV daga jakarta ta ajiye Mata a gaban ta,
"Kina cikin mutane masu matuqar muhimmanci a rayuwar mu Wanda ba zamu manta dasu ba, kina da Hali da Kuma damar da Zaki nemi kudi damu ki saka mu karuwanci ki samu riba Mai tsananin yawa Amman bakiyi hakan ba, kin tsaya tsayin daka wurin ganin kin Kare Mana mutuncin mu Mun samu ingantaccen rayuwa, haqiqa ke kamar uwa ce a garemu Shugaba Kuma har cikin zuciyar mu muke qaunar ki, wannan Kuma katin aure na ne na kawo Miki gayyata ne ba a matsayin baquwar mu ba saidai a matsayin uwa Wanda zata je Taya 'ya'yan ta farinciki, alqawarin da muka dauka Miki Kuma yanzu 'dan uwan mu zai cika Miki shi a waje sai kizo muje"

Abunku da Mara addini wani guda shugaba ta rangada Wanda qarar shi har tsakar gida ta tafa hannuwa "a hayye nanaye, yau BARIKI tayi riba ai banci ta zama ba Ashe harqan arziqi ne ta kawo ki, to muje" ta fada tana Kama hanyar waje,

Girgiza Kai Leesa tayi tana Murmushi, son kudin shugaba har yanzu Yana Nan tace "kidan rufa jikin ki shugaba babban mutum be sosai"

Babu musu ta dauko wani ficilin gyale ta yafa suka fita, shugaba da kanta ta shimfida ma Sa'ood tabarma ya zauna ita Kuma Leesa ta dauko mata kujera 'yar tsunguno,

Kallo Daya Sa'ood yayi Mata ya dauke Kai Yana Jin kaman yayi amai ga turaren ta Mai warin daga hankali kaman na Koran aljanu, ba don darajan Sarwa ba wallahi ko hanya bazai yarda ya hada su da wannan matar ba, basu tsaya wani dogon gaisuwa ba ya jawo wata qatuwar jaka da ya dauko a mota Bayan Leesa ta Shiga ciki, ya bude ya fara Ciro bundle din 'yan dubu_dubu Yana ajiyewa,

Saida ya ajiye guda ashirin sannan ya Ciro wasu ashirin din ya ajiye a Daya gefen
"Ga alqawarin ki Nan, Daya kudin sarqan Haleesa dayan Kuma na sarqan Saleeha"

Baki bude shugaba take bin kudin da kallo Wai yau ita aka bawa miliyan 4 a bulus ba tare da tayi komai ba, Bata Gama mamaki ba Sa'ood ya Ciro cheque ya rubuta Mata 20 million ya Bata,

"Wannan Kuma rabi ladan kula da Haleesa ne rabi ladan kula da Saleeha, Mun gode qwarai da Kika riqe amanar da Allah ya Baki Allah ya saka Miki da mafificin alkhairi, sannan Abu na qarshe Kuma inaso a kashe gidan Nan, inaso abar duk wani aikin ashsha da akeyi a cikin ta a rufe ta gaba Daya, idan hakan ta faru no Kuma nayi alqawarin Zan taimaka ma kowa a cikin ku da wurin zama da jari ko aikin you Mai kyau Wanda zai dauki nauyin ku harda iyalanku idan akwai maishi sai kuyi tunani akai idan Kun yanke shawara ku fada ma Haleesa ta sanar dani,"

Shugaba dai ta qane ta kasa magana ta dubi maqudan kudin da aka ajiye Mata tabi ta dubi cheque din hannun ta, Bata taba tunanin zata samu kudi irin haka ba Ashe gwara da ta yarda ta karbe su a hannun saurayin ta alhajin da aka saka Masa su cikin mota shi yayi tunanin ma wata budurwar shi ce ta aifa Masa su shiyasa tunda ya miqa Mata su day yarjejeniyar zai bada kudin kula dasu da abincin su day komai da komai ya gudu Bata sake ganin shi ba har yau,

Kafin ta dawo hayyacinta ta nemi Sa'ood ta rasa har ya tashi daga wurin, wani ihu ta saka ta tattari kudin harda tabarman ta shige ciki dashi tana shewa kaman zata tashi gidan Babu abinda take maimaitawa sai "harqa ta mutu, daga yau harqa ya watse"

Haleesa dariya kawai tayi dajin haka tasan kudi ne kawai yayi aiki a Kan shugaba badon haka ba gwanda ta rasa rayuwar ta Akan ta rasa muqamin ta, sauran kudin taje ta raba masu Helen da sauran kilakan gidan sannan ta Basu IV sukayi musayar number tayi sallan azahar tukunna ta zauna jiran dawowar Sa'ood daga masallaci,

Duk Yanda sukayi da ita taci abinci firr taqi saboda Saida sukayi yarjejeniya da Sa'ood Akan ba zata Sha Koda ruwa ba a gidan karuwai idan ba haka ba a bakacin karatun ta, Yana dawowa ya Kira ta a way tayi musu sallama suka tafi sannan suka biya Yahuza suya spot ya siya Mata drinks da nama da Dan snack suka dauki hanyar komawa Kano,

Daff la'asar suka Isa unguwar su Ameerah, Sa'ood yasa akayi Masa sallama da babanta Dan bayi son barinta ta fara Shiga suyi Mata irin wulaqancin da ya samu sunayi Mata ranan,

Kwarjinin da Sa'ood yayi mishi da Kuma yanayin shi kana ganin shi kasan akwai dala, yasa har qasa baban Ameerah ya tsunguna Yana mishi gaisuwar ban girma Yana qi suyi musabaha, baisan shi ba domin ranar da yazo ya dauki Haleesa dare be Kuma Bai want tsaya qare Masa kallo ba Saida yace Haleesa ta fito daga mota sannan tsananin kunya ya Kama shi dan bai manta ta ba,

Gaida shi tayi cikin mutuntawa da sauri tayi ciki tana qwala ma mamanmu Ameerah Kira, Jin kaman muryan Haleesa yasa Ameerah da qannen ta sukayi saurin fitowa itama dazu da safe tazo wunin gida don auren ta yanzu wata biyu Kenan,

Da gudu Ameerah tazo ta rungume Haleesa daga ta sama tana Nishi, "yarinyar Nan ba kyau ba harda nayi kinyi, Ina Kika Shiga be Haleesa? Ina dai kina lafiya? Baki zo biki na ba nayi missing dinki sosai"

Miqa Mata IV tayi tace "Allah baiyi zanzo nakin bane Amman ga nawa Ina fatan Zaki zo"

" Ba zata je ba tunda qawarki kawai Kika sani kin manta da maman ki" taji muryan maman Ameerah ta Bayan ta Wanda fitowar ta Kenan daga bandaki,

Juyawa tayi ta rungume mama "sorry mama ta daga shigowa na ke na Nima, mama yanzu nasan gidan mu na samu iyaye na Kuma Suma sunce suna son ganin ku yanzu ma tare da Yaya na nake"

"Alhamdulillah, alhamdulillah Daman komai yayi farko zaiyi qarshe Haleesa.............🧚

*Page din yau anyi rungume_rungume da yawa shiyasa duk jikina ya Kama ciwo*😃
*Ayi min afuwa da qarancin pages din kwana biyun nan please*

*Ummu Najma ce 😘*

Continue Reading

You'll Also Like

74.5K 7.9K 45
Two sisters given birth But separated Find out more in the novel!!!
5K 442 40
love is a strange feeling but also a very strong connection that will either be your strength or your weakness it all depends on who you've to be wit...
8.6K 973 10
The heart is a confusing, altering thing no state of bliss lasts forever and no state of pain does either. A nice easy going girl, a temperamental a...
1.6K 148 28
Ayzar hisham Alee a man who doesn't believe in love again was ordered to marry an ordinary girl. Najma khaleel a lady with good values. She is loving...