KAMA DA WANE....(Completed)

Por Seemahwrites

13.2K 1.8K 210

even though they look alike that doesn't mean they should have same goals, their life is filled with regret... Más

chapter 1
chapter 2
chapter 3
chapter 4
chapter 5
chapter 6
chapter 7
chapter 8
chapter 9
chapter 10
chapter 12
chapter 11
chapter 13
chapter 14
chapter 15
chapter 16
chapter 17
chapter 18
chapter 19
chapter 20
chapter 21
chapter 22
chapter 23
Apology
chapter 24
chapter 25
chapter 26
chapter 27
chapter 28
chapter 29
chapter 30
chapter 31
chapter 32
chapter 33
chapter 34
chapter 35
chapter 36
chapter 37
chapter 38
chapter 39
chapter 40
chapter 41
chapter 43
chapter 44
chapter 45
chapter 46
chapter 47
chapter 48
chapter 49
FINAL
Trailer

chapter 42

188 33 3
Por Seemahwrites

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)
🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤
👩🏻KAMA DA WANE......
BATA WANE👩🏻‍🦱
💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

*Na*
*UMMU NAJMA*
marubuciyar *HAR ABADA*

*DEDICATED TO*
*AMMYN KHAIRAT(golden girl)*
*AND RUKAYYA IKRA(ummu sultan)*

*Wannan shafin taki ce ke kadai Momyn twins AKA Mrs zanna💖 kiyi yanda kika ga dama dashi🤩*

42👯
Shi abin tausayawa ne abin tallafawa Amman wasu mutane sukan dauke shi kaman bayi da muhimmanci su cuce shi, su hantare shi, basu san zasu iya rasa rahamar Allah saboda hakan ba? Meyasa mutane ba zasu zauna suyi tunani idan Suma suka mutu 'ya'yan su zasu iya Shiga irin wannan halin ba?

Ka ko kin taba tunani idan ka mutu akwai Wanda zai kula da naka ko naki yaran? Kuma wani irin riqo za'ayi musu? Tabbas duk abinda kayi shi za'ayi maka ko baka so ba, ba sai ka hada ya Kai dubu 'dari ba, ba sai ka Tara Kaya sunkai kala hamsin ba, ba sai abincin da zaka bayar ya Kai buhu goma ba, ko cikin Wanda suke zuwa makarantar gwamnati ka biya was kudin P.T.A Allah zai biya ka, idan ka Sami Mai Jin yunwa ka bashi abinda zai wadatar da cikin shi Allah zai biya ka, Wanda yake zaune bayi da aikin komai ko zare da alluran dinkin takalmi ka siya mishi ya fara bi gida_gida Yana samun halaliya Allah zai biya ka kuma ya Buda maka taskar arziqin ka,

Cikin suratul baqara Aya ta 215 Allah yace
بسم الله الرحمن الرحيم
و يسألونك ماذا ينفقون قل ما انفقتم من خير فالوالدي ولاء قربين واليتاما والمساكين

Suna tambayar ka me zasu ciyar kace duk abinda Zaku ciyar na alkhairi to kuciyar da iyaye, makusantar ku dangi, sa'annan *marayu* da miskinai,

Sa'annan cikin suratul baqara Aya ta 220 Allah yace
و يسألونك عن الائتمان قل اصلاح لهم خير

Suna tambayar ka Akan al'amarin marayu kace kyautata musu alkhairi ne, ku Sanya arziqin ku cikin kasuwancin da bayi da faduwa, ku nemi yardar Allah ta hanyar kyautata ma maraya, shuwagabanni kuji tsoron Allah alumman ku kiwo ne Allah ya Baku Kuma abin tambaya a kanku ranar alqiyama, 'ya'yayen ku suna Hawa manya manyan motoci, sun saka tufafi na alfarma marayu Kuma suna barci da yunwa, ruwa, Rana da iska duk a kansu yake qarewa, ku rage ko kashi Daya ne daga cikin nasu ku tallafa Mana dashi tabbas Allah zai biya ku"

Share guntun hawayen dake idon shi yayi cikin nutsuwa ya ninke takardan hannun shi sannan ya sauqa daga Kan stage din aka saka qabbara, sautin Allahu Akbar ke tashi ta ko wani kusurwa har sai da babban malamin da aka gayyata zaiyi fashin baqi ya hawo Kan stage kafin aka sarara,

Shima sallama yayi ya gabatar musu da kanshi sannan ya fara da " daga Abu huraira Allah ya qara masa yarda yace manzon Allah s.a.w yace (me daukan nauyin maraya nasa ko na waninsa no da shi kamar haka ne a cikin aljannah, wato kamar yatsar tahiya da babba)

An riga an bashi guarantee na Shiga aljannah Kenan, na San duk cikin mu a nan Babu Wanda bayi son Shiga aljannah to ga dama ta same mu dama Mai matuqar sauqi dukda akwai dawainiya a cikin ta Amman duk Wanda zai iya ciyar da iyalansa ciyar da Mara guda Daya tol ba zai gagare shi ba, idan Kuma mutane kuka watsar da wannan damar kuka aikata zalunci ma maraya to fa Allah ba zai barku ba tabbas Zaku Shiga ciki uquba da tsananin azaba ranar qiyama,

Cikin suratul duha aya ta 9 Allah yace
فأما اليتيم فلا تقهر
Amma maraya karka rinjaye shi (karka cinye mishi dukiyar shi ko ka Hana shi katabus)

Cikin suratul ma'un aya ta 1 zuwa na biyu Allah yace
الرؤيا الذي يكذب بالدين
فذلك الذي يدعو اليتيم
Kabani labarin Wanda take qaryata addini
Wannan shine Wanda take tunkuda maraya

Sannan cikin suratul nisa'i Aya ta 10 Allah ya Kuma cewa
إن الذين يأكلون أموال اليتامى ظلما إنما ياكلون في بطونهم نارا و سيصلون سعيرا
Duk Wanda suke cin dukiyar marayu saboda zalunci iyaka wuta sukeci a cikin cikkunan su Kuma qarshen su wuta zasu Shiga wutar sa'ira,

Wa'iyazubillahi lallai wannan ya Kai qarshen asara ka rasa lahirar ka, kayi asaran duniyar ka Kuma har qarshen rayuwar ka mutane ba zasu dauke ka da daraja ba,

Haka malam abdulhameed ya dinga zaburar dasu, ya dauki kusan mintuna 30 Yana wa'azantar dasu Akan hakkin maraya kafin salon ya juya ya koma ga hakkin iyaye a Kan 'ya'yan su nanfa Haleesa ta Shiga cikin damuwa Jin Yanda ake kwatanta azabar da Allah yayi alqawarin za'ayi ma Wanda ke Saba ma iyayen sa musamman mahaifiya, ya kawo ayoyi da hadisai da dama Wanda ke nuna girma da darajan iyaye,

Lokaci daya Haleesa taji fitsari ya cika Mata mara saboda tsoro ta kalli mamanmu dake opposite dasu a Kan wheelchairn ta hankalin ta kwance tana sauraron wa'azin da akeyi, saƙe_saƙe ta fara a ranta tana jaddada cewa Wannan itace matar da ta dauki cikinsu wata Tara tayi naqudan su biyu sannan Bayan ta Gama dawainiya da su aka dauke su yaye su batayi ba, Bayan ta Shiga tsananin tashin hankali ta same su Bayan tsawon lokaci sannan itakuma ta qara daura Mata wata damuwar, Bata dauki mahaifiyar ta da daraja ba Bata taba wani yunquri Dan farnta Mata ba, Bata tantance alaqa da magananun da takeyi da ita Wanda ita kanta tasan Basu dace ba, mamanmu it kadai ta rage Mata a duniya cikin iyayenta Amman tana was da damarta na samun rahama daga kyautata mata,

"Babu babban rahama da Jin Dadi na duniya da ya wuce ka tashi kaga iyayen ka suna raye Kai da wulaqanta har abada, Babu babban asara Bayan rashin tauhidi sai Saba ma iyaye, Babu shakka Mai Saba ma iyayen sa indai ba Akan abinda ya kauce ma shari'a bane ɗan wuta ne, shi da rahaman Allah sunyi hannun riga domin fushin Allah yana daga cikin fushin iyaye"

Zufa taji Yana karyo Mata ta ko Ina ta riqe gefen dankwalin ta da Bai samu zama a kanta ba ta fara fifita dashi hakan ya jawo hankalin Sa'ood gareta domin sanyi ya fara shigowa wasu har sun fara saka kayan sanyi,

Dan sunkuyowa yayi Yana leƙa fuskarta yace "lafiya Haleesa?"

A zabure ta dago tana kallon shi sai rarraba idanu takeyi tace " na Shiga uku ya Sa'ood bazan Shiga aljannah ba"

"Kai! Wa ya fada Miki haka?"

"Baka ji ba? Ance Wanda ya Saba ma iyayen shi ɗan wuta ne, Kuma Ina tsoro Sosai wallahi bani so in Shiga wuta"

Ganin hankalin su Sa'eed ya fara dawowa kansu saboda ana wa'azi suna surutu yasa yace mata "ki bari idan munje gida sai muyi magana Amman ba zaki Shiga wuta ba idan Allah ya yarda"

Gyada kai tayi ta gyara zaman ta taɓa nusar da kanta ba don hankalin ta ya kwanta ba don maganar ya tsaya mata a rai, tabbas a islamiyyan su ana yawan fada musu illar saba ma iyaye amman Baga taɓa fitowa ɓaro_ɓaro aka ce mata zasu shiga wuta ba,

Har aka gama taro lafiya aka watse hankalin Haleesa bayi jikin ta, bayan sunyi sallar magriba aka kawo musu abinci irin wanda kowa da kowa zai ci a orphanage din aka shinfida musu tabarma a basketball field kowa ya zazzauna a qasa ana cin abinci ana nishadi, Za hada kan yaranta tayi suna cin abinci a plate daya ta gefen idonta take leqo Sa'eed Yana feeding din Salee, kawar da kanta gefe tayi ganin abin nasu yana so ya wuce mizani daga cin abinci sun koma wani abu daban saboda suna can gefe wurin da babu wadataccen haske sosai a wurin,

Suna gama cin abinci suka sauro alwala a wurin sukayi Salman Isha sannan suka fara zagaye orphanage din suna duba gyaran da aka yi, manyan cikin wanda suka san tsarin wurin ne suke nuna ma su Haleesa wurare saboda renovation akayi ba'a canza tsarin wurin ba, Ita dai nutsuwarta bayi jikinta ta ƙagu a koma gida Sa'ood ya fada mata yanda zatayi ba zata shiga wuta ba,

9:27pm
Suka shigo gidan, sallama sukayi kowa ya shiga part dinsa, Haleesa na shiga parlorn mamanmu ta zube a kan guiwowinta tana kuka, sautin sheshsheqar ta yasa mama da ta kusan shigewa dakinta ta biyo tana kallon ta, hankali a tashe ta danna kekenta ta qarasa wurinta tana tambayar ta abin da ya same ta,

Riqo hannun ta tayi ta qanqameshi cikin nata cikin kuma tace "mama dan Allah ki yafe min, I'm very sorry" hakan yayi daidai da shigowar Sa'ood parlorn ya tsaya yana kallon su cike da mamaki,

"I know that I'm not a good daughter, bani Jin maganar ki ina muku rashin ji sannan ina yawan saɓa Miki amman wallahi daga yau na Bari bazan sake ba wallahi dan Allah koyi haquri bani son in Shiga wuta"

Stunned mamanmu ta tsaya yana kallon Sa'ood, bata san wannan aiki nashi ne ko kuma wani abu daban bane amman koma menene tana farin ciki sosai Finally ta samu cikakkiyar iko akan Haleesa,

"Kinji mama? Allah nayi alqawari bazan sake ba ki yafe min Please"

Ɗan dariya tayi mai sauti ta saka hannun ta duka biyu ta fari ta sannan ta rungume ta tana zaune a kujerar, sunfi 1 minute a haka sannan ta fari ta tana qare mata kallo still fuskar ta da murmushi ta shafa kanta
"Allah yayi Miki albarka Haleesa yasa koyi ingantacciyar rayuwa, uwa bata taɓa fushi da ƴarta ke ƴar aljannah ce cikin hukuncin Ubangiji"............🧚

*Yauma dai manage😁*
_Gobe idan na samu dama zan fanshe insha Allah_

*Sorry for the errors Ummu Nana ba Malama nace😅*

_Keep voting_
_Keep following_
_Ummu najma loves you so much_😘😍

Seguir leyendo

También te gustarán

1.6K 148 28
Ayzar hisham Alee a man who doesn't believe in love again was ordered to marry an ordinary girl. Najma khaleel a lady with good values. She is loving...
449K 32.1K 43
ပဲပြုတ်သည်ငပြူးနဲ့ ဆိုက်ကားဆရာငလူးတို့ရဲ့ story လေးတစ်ပုဒ်
445K 16.2K 192
Won Yoo-ha, a trainee unfairly deprived of the opportunity to appear on a survival program scheduled to hit the jackpot, became a failure of an idol...
1.1K 142 13
Mahir Adam Dan-Musa, a true definition of egotistical, domineering and self-centered human being. He got the looks, the wealth and thinks no woman ca...