KAMA DA WANE....(Completed)

By Seemahwrites

13.2K 1.8K 210

even though they look alike that doesn't mean they should have same goals, their life is filled with regret... More

chapter 1
chapter 2
chapter 3
chapter 4
chapter 5
chapter 6
chapter 7
chapter 8
chapter 9
chapter 10
chapter 12
chapter 11
chapter 13
chapter 14
chapter 15
chapter 16
chapter 17
chapter 18
chapter 19
chapter 20
chapter 21
chapter 22
chapter 23
Apology
chapter 24
chapter 25
chapter 26
chapter 27
chapter 28
chapter 29
chapter 30
chapter 31
chapter 32
chapter 33
chapter 34
chapter 35
chapter 36
chapter 38
chapter 39
chapter 40
chapter 41
chapter 42
chapter 43
chapter 44
chapter 45
chapter 46
chapter 47
chapter 48
chapter 49
FINAL
Trailer

chapter 37

227 37 10
By Seemahwrites

(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)
  🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤
👩🏻KAMA DA WANE......
                          BATA WANE👩🏻‍🦱
   💙🖤💙🖤💙🖤💙🖤💙

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

         *Na*
        *UMMU NAJMA*
marubuciyar *HAR ABADA*

*DEDICATED TO*
*AMMYN KHAIRAT(golden girl)*
*AND RUKAYYA IKRA(ummu sultan)*

Special gift to *Muhammad Karim*
       *And Fenarh matar Soja*

37👯
"Me yasa ko na lokaci 'daya ba zatayi amfani da qwaqwalwar ta tayi tunani Mai kyau ba kamar Wanda kare ya lashe ma zuciya? Ki kalli fa Yanda mijin ta yaci ma 'dan uwanta mutunci a gaban idonta Amman Bata nuna damuwa ba ko kadan instead saima wani lallaba shi takeyi tana bashi haquri,

Wallahi takaicin ta ne ya Hana ni aikata komai ya saka na bar parlorn ma gaba daya saboda nasan idan naci gaba da zama I might do something crazy, na rantse da Allah bazan taba gani ana wulaqanta 'dan uwana na Bari ba ko wayene kuwa"

" Tashi ki zauna"
Mamanmu ta fada tana riqo hannun leesa daya, zama tayi tana facing dinta
"Yayanki yayi laifi Haleesa Dan haka ya zamo Dole a hukunta shi, kuma ni Banga laifin Sa'eed ba da ya dauki hukunci a kanshi, yanzu misali kisa kanki a matsayin Sa'eed mutumin da ya tashi cikin daula da Jin dadin rayuwa Amman rana 'daya 'dan uwan ki da Kika yarda dashi ya ha'ince ki saboda shi kiyi rayuwa gidan kurkuku na shekaru 1-1 har 8 Yaya zakiji?"

" Babu Dadi Mana mama Amman  shima ya Sa'eed din yayi Mana laifi Kuma Mun yafe mishi, ai ni da Salee muma cikin daulan aka aife mu amma sanadin shi Mun tashi a gidan karuwai tsawon shekaru 17 Kinga ya ruba nashi sau biyu harda qarin shekara daya, shi meyasa ba zai yafe ma namu 'dan uwan ba?"

Murmushi tayi irin nasu na manya ta lura Haleesa tana da kaifin baseera Babu Yanda za'ayi ta rudata ta gwada Mata cewa abinda Sa'eed yayi daidai ne, ita kanta tasan bai kyauta ba Amman ta wani fuska gwanda da yayi hakan maybe tozarta Idris da yayi shi zaisa ya gane kuskuren shi

"Ajizancin Dan Adam Kenan Haleesa mutum Mai yawan mantuwa ne Kuma mai aikata kuskure, dukkan mu Nan wani lokaci mukan aikata wasu abubuwa ba tare da sanin mu ba, Kuma dama haka ake son mace ta gari ta zamo Mai biyayya a wurin mijinta ya zamto duk lokacin da yake baqin ciki ko tashin hankali a wurin ta zai samu salama da nutsuwa Ina alfahari da Saleeha sosai nasan ko Bayan raina na ajiye 'yar da zata zamo abin koyi ma 'ya'yan ta, kema kada ki qullace shi dan Allah he is your brother after all"

" To yanzu idan ya Sa'eed baiyi niyan yafe ma ya Idris ba fa? Haka Zaki bar masa 'yar ki a wurin shi yaci gaba da zama da ita?"

" Bani da ikon raba abinda Allah ya hada, Kuma Ina roqon Allah ya kunyatar da duk Wanda yake son ganin wannan alaqan ta yanke, Saleeha tayi matuqar Dace da samun miji wanda nake da tabbacin zai Kare Mata dukkan haqqin ta, fadan dake tsakanin 'yan uwa bazai jawo matsala a tsakanin Mata da Miji ba dan Allah ki fitar da kanki a cikin maganar Nan"

" You are impossible" Leesa ta fada cikin kaushin murya ta tashi ranta a bace ta Shiga bathroom tare da banko qofar, girgiza Kai kawai tayi ta danna wheelchairn ta tayi gaba Saida Leesa taji qaran rufe qofa sannan ta fito ta kwanta,

**********
7:11am

Sauqowa yake yi daga stairs fuskar shi Babu walwala dan tun Jiya ranshi a bace yake kwata_kwata Bai samu ya runtsa ba, tun daga wurin yake jiyo muryar Haleesa cikin daga murya take magana that too da mahaifiyar ta, qara hade fuska yayi ya qarasa wurin Yana tambayar ta abinda ke faruwa, Dan sararawa tayi da ta ganshi tukunna tace

"Makaranta nake so a maidani"
"Daman za'a maidake makaranta Mana Amman ki bari mu sami nutsuwa tukunna insha Allah karatu sai kince kin gaji"

"Ni gaskiya yau nake son komawa na gaji da fitintinu da matsalolin cikin gidan Nan I cannot bear it anymore, kowa Yana gani ana abubuwan da Basu dacewa"

Gyara zaman hannun riganshi yake yi ranshi na tafarfasa rashin da'an Haleesa har ya wuce kansu yayun ta ya koma Kan mahaifiyar ta? A jiya ya dauka cewa ta canza hali ne Ashe kuwa yayi kuskure dan ajiye shi tayi na wucin gadi, ya kuwa zamo Mata tamkar Dole ta ajiye wannan dabi'un ko tana so ko bata so,

"Lower your voice Haleesa"

"Why would I? Tana gani ana tauye Mana hakki Amman tana shiru" ta fada tana nuna mamanmu "Kai daman banyi tsammanin zaka goyi Bayan mu ba duk da ka gwada hakan Amman dole zaka Gaza a hanya saboda Sa'eed 'dan uwan ka ne,

Duk abinda za'ayi Mana tana kallo Amman sai tayi shiru, why won't you fight for your family mama? Meyasa ba Zaki tsaya tsayin daka a Kan 'ya'yan ki ba ana juya 'yan uwana Yanda aka so Amman Babu Mai iya cewa komai saboda ke an maida mu qaramin danga Mai dadin qetara ko wani Kare da doki yazo ya watsa kashin sa kanmu don yasan ba zaki taba hanawa ba"

Zuwa wannan lokacin ran Sa'ood ya Kai maqura wurin baci Amman Yana qoqarin controlling tempern shi saboda Yana gaban mamanmu ne ba don hakan ba da tuni yayi qasa_qasa da Haleesa shi Sam bayi daukan nonesense ko a wurin waye kuwa,

"Ki rufe min baki kafin ranki ya baci"

A tsawace tace "bazan rufe ba ya Sa'ood ko me zakayi saidai kayi Amman tozarci shine abunda bazan taba juran gani anayi ma want nawa na qyale ba, a gaban 'ya'yan ya Idris Sa'eed yayi mishi duka matar shi tana kuka Suma suna kuka baka........"

Wani tsawa da Sa'ood ya daka Mata yasa ta qame tsamm Dan har cikin qwaqwalwar ta taji shi ta runtse idanun ta ganin Yanda ya daga hannu Yana Shirin kafta Mata Mari da sauri mamanmu ta dakatar dashi

"Por favor no le des una bofetada(Dan Allah kada ka mare ta)" bai mare ta ba Kuma Bai sauqe hannun sa ba ya tsaya Yana qare Mata kallo cikin bacin rai gaba daya yayi jaa lokaci Daya jikin shi na tsuma har wani karkarwa yake yi,

Ta sake cewa "por mi bien (for my sake) please"

a hasale ya sauqe hannun shi sannan yayi snapping yatsun shi biyu Yana gwada ta da na tsakiyan da qyar ya samu maganar shi yake fitowa shima ciki_ciki,

"Idan ke Baki dauke ta a matsayin mahaifiya ba ni tana da matsanancin daraja a wurina Kuma Ina mutunta ta fiye da rayuwata, wannan ya kasance na farko Kuma na qarshe da zanji muryar ki ya haura nata idan ba haka ba duk abinda nayi Miki ke Kika siya da kudin ki, babu Wanda zai wulaqanta ta ya zauna lafiya matuqar Ina raye wallahi tallahi, ya zamo Miki dole kiyi Mata biyayya ko kinqi ko kinso, ko da wasa iyaye ba abun wasa bane kima gode ma Allah kina da shi, Kuma na dawo na samu kinci gaba da wannan Maganar kiga Yanda zamu qare dake"

Yana kaiwa Nan ya wuce ya fita ko breakfast baiyi ba a hanya ya hadu da Sa'eed Yana shigowa part din daga gani haquri yazo bawa mamanmu Yana jinshi Yana mishi magana Amman yaqi kulashi don shima haushin sa yakeji, da hanzari ya qarasa jikin motar da zai tafi aiki da ita ya karbi key a hannun driver ya Shiga ko warming baiyi ba ya zuge ta a guje ya bar gidan,

Sosai yake falla uban gudu a titi ya rasa ma tunanin me zaiyi 'daya kowa ya hada mishi caji a ka sun saka shi cikin tension baima San ta Ina zai fara ba, rage gudun shi yayi ya sauqa yayi parking a gefen hanya sannan ya dauki wayar shi ya Kira Adam bugu biyu ya dauka,

Murya qasa_qasa yace "hello barrister kana gida ne?"

"Aa na fita office yau da wuri saboda akwai wasu ayyukan da nake so na qarasa inason zan dauki hutu ne mu bar qasan tare da iyalina any problem?"

"Inaso mu hadu da Kai ne akwai magana Mai muhimmanci da nake son nayi da Kai so I'm coming to your office"

" Akwai wani matsala ne SD? Naji muryar ka wani iri ba Yanda na Saba ji ba ka fada min menene matsalar?"

Numfashi Mai zafi Sa'ood ya furzar Yana Jin takaici yace "barrister I choose the second option mu saka gwamnati cikin case dinmu a dawo Mana da hospital da orphanage yanzu me zamu fara a Kai?"

"Subhanallahi ai wannan ba maganar da za'ayi shi a waya bane ka qaraso sai mu yanke hukunci Allah yasa dai lafiya"

Katse Kiran Sa'ood yayi ya kunna motar shi ya nufi office din Adam Yana Shiga ya same shi a zaune sai lokacin shima yake breakfast Daman zaman jiran shi yake yi, basuyi wani dogon gaisuwa ba Adam yace

"Bari a kawo maka breakfast ka qara a Kan Wanda kayi a gida Dan nasan tunda mama tana tare da Kai ga amarya Babu zancen zama da yunwa"

Tsaki Sa'ood yaja in serious tone yace "joke aside ka dai San ba qaramin Abu bane ya kawoni nan idan zaka iya ka taimakeni please inason abun nan ya dawo Mana cikin sauri"

Sipping tea dinshi Adam yayi Yana kallon Sa'ood da wutsiyar Ido he seems restless, ya ajiye cup din sannan ya tattara dukkan hankalin shi gareshi,

"SD kaman Yanda na fada maka a baya wannan zabin Yana da hatsari sosai Yanda baka tsammani, ni nama kawo maka option dinne ba don komai ba sai dan na nuna maka cewa binciko Wanda yayi wannan crime din shine yafi, ku dada zurfafa bincike Zaku gano koma waye tunda Ina da tabbacin Yana kusa da ku, shi ya cancanci hukunci ba ku ba shi ya Kamata ya kasance cikin tsoro da fargaba ya Shiga cikin tashin hankali ba familyn ku ba"

" Na sani barrister Amman muna buqatar orphanage dinmu at the earliest na samu labarin Yanda yaran suke Shan wahala Basu samun kulawa Kai kana ganin na tsaya Bata lokaci na a Kan binciko mutumin da bamu San yaushe zamu gano shi bane? Ko Kuma muyi wani abu dan ceto rayuwar marayu"

Jingina jikin shi da kujeran da yake zaune a Kai yayi ya zabga tagumi Yana nazarin Sa'ood, daga look dinshi ya Gane Yana boye wani abu duk wasu sign na rashin gaskiya ya bayyana tattare dashi

"kana maganar marayu ka manta da familyn ka, sati biyu ne kawai da dawowar ku guri daya kada kayi kasadan sake jefa su cikin matsala think about it"

"nasan da haka Kuma na dauki alhakin komai da komai kaidai kasan Yanda saqon mu zai Isa gurin gomnati at the earliest"

" Ok Amman gaskiya zai dauki lokaci qarancin lokacin da zai dauka kafin mu samu feedback 3 weeks ne, zanyi komai da komai duk abinda ake ciki zaka jini"

Miqewa Sa'ood yayi ya dauki car keys dinshi "ni zan wuce office said naji daga gareka" suka sake shaking Sannan yayi mishi sallama ya fita,

_Manage please🤒 zazzabi nake fama dashi Amman insha Allah page din gaba zaiyi tsayi_ thanks

*Ummu Najma ce*😘

Continue Reading

You'll Also Like

218K 16.1K 20
Avantika Aadish Rajawat Aadi, with his fiery nature, adds intensity and excitement to their relationship, igniting a spark in Avni. Avni, like the ca...
1.4M 128K 62
RATHOD In a broken family, every person suffers from his insecurities and guilt. Successful in every field but a big failure when it comes to emotio...
Ice Cold By m

General Fiction

2.2M 83.4K 49
[boyxboy] Wren Ridley is always two steps ahead of everyone, or so he thinks. His life seems out of his control when he starts having feelings for so...
102K 9.5K 51
Boddo is a Fulani girl, who will be married at young age of 13yrs to the man who she never knew or saw in her life who is also educated.....how will...